Showing 180001 words to 183000 words out of 184731 words

Chapter 61 - AMIR DA AMIRA complete

27 Aug 2026

31

Alhamdulillah tinda yafito anwanke shi daga zargin da akemishi

Murmishi yayi yace a wifey iyayen masifa koda y

ake anyo gado ba karanbani ba abin ajinin ki yake

Filow ta dauka ta wurgo mishi , da sauri ya cafe yana dariya yace kefa dadina dake idan gadon hajiya inna mai duniya yatashi saifa a hankali

Kuka ameera tasaka tana

dira kafa gefe ta kalla aikuwa ta wata sanda yar siririya mai tsayi dauka tayi tana fadin ni kake cewa mai masifa wllh saina zaneka kuma sainayi yaji naje wajan inna , tana bishi da gudu

Biye mata yayi suka ringa

zaga falon tana kuka tana magana fadi take saifa tayi yaji taje wajan inna ko saitayi shekara

Shikuwa ameer dariya yake mata , yace ai indai nine bazaki kamoni niba sai kin gajiyar da kanki tukun na tsaya

Haka

suka ringa zagaye falon saida ameera tagaji sosai faduwa tayi a kasa tana sakin sabon kuka , tsayawa ameer yayi ya koma inda take ya dagota

Kamar jira takeyi dama tashige jikinsa tana kaimai duka a kafada

Daukarta

yayi suka zauna yace haba wifey wai duk kukan nan na miye daga magana yana kunshe dariyar shi dan yau ya lura yan rigimar ne akusa

Sake shigewa tayi jikinsa tana shakar kamshin turansa mai sakata jin dadi tace ba

kaine ba kake demin nayo gadon masifa , bubbuga bayanta yayi yace to kiyi hakuri muje natayaki girki yunwa nakeji fa

Dagowa tayi tana dariya ta mike daga jikinsa tace yauwa muje nima ita nakeji

A tare suka jera zu

wa kitchen , jollof suka daura ameera na fata kwanika ameer yana wankewa bayan ta hada komai kafin yagama wanke kayan data bata ta goge saman da ajiye kayan tana daurayewa suka fito falo ameer yafara zama ameera ta h

aye cinyarsa tana dariya , hancinta yaja yace badai son jikiba to kwanta ko .kwanciya tayi nan sukaci gaba da hira

Yau anass yazo ganin fatima da baby iman a falo ya zauna mommy tashigo ganin anass tace a a lal

e da dan sanda abokin kowa

Kasa dakai anass yayi ya durkusa yace mommy ina yini nasameku lfy

Amsawa mommy tayi ds lfy yasu ammi naka ,Anass yace suna lfy tace na gaisheku

Mommy tace ina amsawa nan takoma d

akinta

Fatima ce ta karaso falon da baby iman a hannun ta ,Anass yamike ya amso iman suka zauna tare

Kallon shi fatima tayi tace sweetheart yanaga karame ko bakada lfy ne

Fuskar tausayi yayi yace ba gyara ras

hin lfy ba da wannan azabar da ake ganamin, dafe kirji fatima tayi tace nashiga uku azaba kuma sweetheart wayake gana maka azaba

Anass yace ke mana kinki komawa gida kullin ni daya nake kwana babu mai bani abinci a

baki bamai shiryani idan zanje office bamai tararraya ta idan nadawo daga aiki komai ninake ai dole na rame

Ajiyar zuciya fatima tasauke tace wllh nadauka wani abunne yasameka, Anass yace awoo bakima damuba kenan ko

F

atima tayi saurin fadin ba haka nake nufi ba ai gobe zamu ko ma nina daukama daukata kazoyi

Washe baki anass yayi yace kai haba nifa wllh na manta kawanan ku nawa agidan nan ashe gobe zaku koma amma naji dadi

Murmishi fatima tayi tace eh insha Allah

Daga bayansu sukayi ana fadin innalillahi wa inna ilaihin raju'un yauga yan iskan yara nizaku maida sakarya , a ni maryama yanzu ke fadimatu baki da kunya ashe kema wannan dununu

n ya koya mishi rashin kunya to wllh baku isaba

Kai dan sandar uba waye yace kazo shine ka lallabo ka lalubeta ko to kafita a idona bazata koma ba sai yarta tayi kwari tukun

Wato ku ga futsararru ku to zak

uga abinda zanyi

Anass dake dariya yace dama nasan za'a rina hajiya inna ai nazo da maganin ki , ledar hannun shi ya mikawa inna yace innar baffa ga kaji da lemo da goro na kawo mishi

Ai da sauri inna ta karba

tana washe hakora tabude kazar tagani gashashiya har biyu da goron ta ga lemo a gefe ,dagowa tayi tana kallon shi tace a a yaron kirki nagode sosai , kasan gobe ne fadimatu zata koma bari natafi dakina nan ta wuce

Da

riya sukayi fatima tace a sweetheart yau kayi maganin inna anrufe bakin

Murmishi yayi yace aikuwa dan tabamu gurine

Washe gari

Aka kai fatima gidanta da babyn ta iman anass kamar zai maidasu ciki hakaa yakeji sai

nan nan yakeyi dasu

Yaune su karima zasu koma garinsu anhada musu goma ta arziki su daddy zasu kaisu airport idan sunsamu lokaci zasuke zuwa ziyara kowa yazo za'a tafi rakiya zuwa airport

Ameera na saurin sa

ka rigarta ameer yashigo yace wifey kefa nake jira sun shirya mu ake jira nace su wuce zamu samesu a airport din

Ameera tace to muje nagama tana saka hijab din ta ya saka mata takalmi nan suka fito sai airport

Suna zuwa suka angosu wajansu suka nufa karima na ganin ameera da sauri ta rungume ta

Aikuwa ameera taringa kuka , Karima dinma na tayata

Mama tace to kukan ya isa haka jirgi yace ansoma kira

Sakin juna sukay

i amma ameera ta rike hannun karima gam

Abubaka da mufeeda da suka matso kusan su ameera

Mufeeda tace mommy aimu babu inda zamuje muna tare take ko abubakar ? ta juya da tambayar shi

Yace eh muna nan bazamu j

e dasu daddy ba

Da sauri ameera ta saki hannun karima ta rungume su mufeeda tana kuka hade da dariya

Dariya su fatima ke mata ,,Jamila tace a ni y'asu ameera wannan kuka kamar ance bazaki sake ganin anty karima das

u mama ba

Murmishi baban karima yayi yace jikata kiyi hakuri zamu sake dawowa bikin hajara zamuje mu daura daga inda kuka tsaya ne

Shara hawayen ta tayi tace to shikenan kakana nadena nima zanje wani lokacin bayan

bikin hajara insha Allah

Umar yace to yaya Muhammed yaranka sunce anan zasu zauna gasunan munbaku su har abada

Wani farin ciki mommy da daddy sukaji inna kuwa kuka tasaka tana fadin Allahu akbar jikona jinina

Da

riya umar yayi yace inna ke nabawa mufeeda yaya muhammed kuma abubakar , rungume shi inna tayi tana saka mishi albarka

haka suka tafi shiga jirgin sukayi suna daga musu hannu har jirgin ya tashi sama saida suka bac

ewa ganinsu tukun kowa yashiga mota

Inna takama hannun mufeeda tace zo nan ya'ta zaki maye gurbin ameera ta

Mufeeda na tsallan murna tace to inna ta nan kowa yashiga mota suka tafi gida

Haka sukaci gaba da rayuwa

r su mai kyau da tsafta , Aliyu yazo gidan su ameer yabada hakuri yanemi gafarar ameera da ameer nan take suka yafe mishi ,, yana ganin hajara baiyi nauyin bakiba yace yana son hajara abashi aurenta ,,Daddy yace yayi h

akuri ansaka mata ranar biki amma zai bashi wata

Cike da farin ciki aliyu yayi godiya yace wa daddy yanason yaga yarinyar don yafada mata ko yamata zata iya aurenshi

Daddy yace tana kauyensu amma za'ayi bikinsu lokac

i daya dana su hajara

Godiya sosai aliyu yayi tukun yatafi gida yana zuwa yafadawa mom dinsa taji dadin wannan karamcin nasu daddy mijinta nazuwa ta fada mishi shima yayi farin ciki yace gobe zaizo suje kauyen anemawa

aliyu auren yarinyar

Ameera ta kalli ameer tace kowa daddy zai aurawa aliyu ameer yace ina tunanin ko rashida ko kanwarta acikinsu daya zai aurawa

Ameera tace tab ka manta rashida anmata miji kanwarta ko bata is

a aure ba yanzu abinda zaayi na kira daddy nace mishi ya bashi khadija wannan shawarar tayi?

Kallon ta ameer yayi yace gaskiya kwakwalwar ki naja wifey na wannan abun yayi kawai kirashi muji maixaice

Cike da farin ci

ki ameera ta dauko wayarta daga caji ta shiga contact nember din daddy ta danna mishi kira ringing daya ana biyu ya dauka

Yace assalam alaikum daughter kece da daren nan

Gyara zama ameera tayi ta nutsu tace eh d

addy ina yini ya gida

Murmishi yayi yace lfy lau ya yaran naku, tace lfy lau am dama daddy wata magana nakeso muyi

Daddy yace fadi kanki tsaye daughter ina jinki

Ameera tace wacce yarinya zaka bawa aliyu a kau

yen mu

Murmishi daddy yayi yace eh bandai yanke hukunci ba da rashida zanbashi to ita ansaka nata bikin da dan mai gari , kanwarta bata isa aure ba , amma idan kina da wadda zaki bada saiki fada naji

Yar dariya amee

ra tayi tace eh daddy akwai

Daddy yace to ina jinki wacece

Ameera tace daddy maizai hana kuje anema mishi auren khadija tinda ita baa mata mijin aure ba amma yaka gani?

Daddy yace kai amma kin kawo shawara mai k

yau nasan iyayen khadija zasu amince insha Allah baban aliyu yakirani zaizo gobe muje kauyen sai muje cen gidansu khadija

Dan murna ameera cinyar ameer tadawo ta zauna tace Alhamdulillah daddy hakan yayi Allah yakaimu g

oben saiki muje yakukayi ,, nan takashe wayar

Kallon ta ameera yayi yace wifey keta dabance halinkima na dabanne yana rungume ta jamusu blanket tayi ta rufesu

Washe gari Alhaji hashim baban aliyu yazo wajan daddy

nan suka kama hanyar kauye , suna zuwa bayan sun huta abbu da abba suka musu jagora zuwa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login