Showing 42001 words to 45000 words out of 295116 words
kofar ta waje ya harde hannuwansa a kirji kamar Mai tunanin.
Ganin malam din da salahuddeen sun shi
go ya daga kansa Yana amsa sallamar su. Mujiba ce ta leko tana fadin" ta tashi din gata Nan fitowa".
Bai shiga falon ba Saida malam ya Fara shiga sannan suka biyo bayansa.
Sannu salahuddeen din yayi Mata ya dauki jinita take a Nan yayi Mata gwajin maleri
a ai kuwa ita ke damunta har ta Kai || +.
Allura ya dauko Yana fadin " malam allura za'a yi Mata emal, idan Allah yasa an dace shi kenan idan Kuma Bai sauka ba sai ayi Mata Attusunate, amma muna fatan Allah yasa a dace ma".
"Allaumma amin ya Rabb". suka
fada su duka. Magunguna ya rubuta Mata na ulcer da tayi masa complain na ciwon girji da gefen kafadar ta, sannan yayi Mata Allah ya sawaqe suka fita.
Har magariba su zahra suna gidan Baba malam, tun bayan fitar su malam ba dadewa Iya Abu ta koma daki ta k
wanta Zahra ta rufeta da wani qaton blanket barci Mai nauyi ya dauketa.
Nan falon suka zauna suna Dan tattaunawa da junansu, da tafiya zasuyi Majiba tace su zauna zuwa wani lokacin tunda ansan suna Nan Dan lokacin da zasu shigo mujibar taga kaninta Mubara
k tace ya fadawa Mama suna gidan Baba malam.
Duk hirar da Mujiba ke yiwa Zahra Sam hankalinta baya tare da ita ta tafi duniyar tunanin abinda ya faru dazu da Wanda aka Kira da Mahmud wai ita Zahra ce kwance a kirjin wani namijin daba muharraminta ba, Kum
a ba wani mataki data dauka Koda kuwa na kad'a Masa warning ne yanda gobe baze Kara marmarin rungumar wata ba, Amma Wai sai gata ta b'ige da shakkar idanunsa abinda kaf tarihin rayuwar ta hakan Bai taba faruwa da ita ba, ga wata faduwar gaba ta ba gaira ba
dalili data sameta yanzu, ganin nan biyu da tayi Masa duk Abu daya takeji a kansa.
Wani wawan tsakin Zahrar tayi Wanda ya tabbatarwa Mujiba Bata tare da ita duk zubar da takeyi kamar 'ya'yan kanya.
"Keda waye kike tsaki haka kuma?".
Majiba ta fada.
"Kedai
kawai bari kawai ba komai. Ta fadar tare da you kwafa ta tashi tsaye tana fadin
"Tashi mu wuce gida tunda Naga wannan barcin na Iya Abu bana Kare bane, inaga har da allaurar barci yayi Mata gaskiya".
A kofar gida suka yiwa malam sallama Yana ta Sanya mu
su Albarka.
Tun daga ranar Zahra Bata sake fita ba tana gida saidai lokaci-lokaci Mujiba na shigowa, a ranar data cika sati daya Abbansu ya dawo murna ba'a maganarta gurin Zahra, duk da tana ganin shi a can syprus din idan yaje Amma hakan bai Hana sun Kai
wani lokaci ba suna tattaunawa irin ta d'a da mahaifi.
Saida Zahra tayi sati biyu sannan ta nufi Jos gurin Aunty Hasana.
Taji matukar dadin zuwanta Jos din. Dan har gidan Aunty Jana sukaje da Yara tunda lokacin da akayi bikin Bata Nan. Duk inda ya kamata t
aje taje har gidansu Mama taje haka ta kaiwa jannifer ziyara lokacin sunyi hutu tana karatu a Nan University ta Jos.
Maganar samari da gaske ta sakata side idan ka ganta tana magana Mai tsawo da namiji to ka tabbatar dan uwanta ne ko wani Mai qirma a idan
unta.
Satinta daya a Jos suka taho tare da aunty Hasanar da Yara Wanda a satin sukayi hutu, bayan dawowar ta daga Jos ne su Hameeda sukazo hutun semester.
A lokacin ne Salma ta fito mata a mutum sak, ta nuna da gaske Bata yin zahra abinda yaso ya kawo b'ar
aka Mai girma kenan tsakanin Mama da Ammah Dan da gaske an Kai hakurin Ammar karshe, maganganu Salmar ta ringa saki kamar lokutan baya, sai dai a wannan karon Zahrar ta nuna Mata jiya fa ba yau bace, idan da tayi tolerating na nonsense din ta a yanzu Kam
dai dai take da ita tunda Bata Jan girmanta a gurinta, abinda ya Kara harzika Salmar lokacin da Zahra ta kalleta tayi tsaki tace "Wai wannan ce mace,kina duba mirror Kuma kina ganin kanki kuwa?gara ni da har kike min gorin ana saka aurena ana fasawa, Ina
laifi tunda har ana ganina ana sona, kaddarar Babu mijina a cikin su ce take rabani dasu, kefa ko Kare Bai taba zuwa yace Yana sonki ba, baga kanwarki Nan ba Ina cewa har anzo tambayar aurenta? kije kiji da abinda ya dameki Zaki zauna kina fada da kanwar
bayanki".
Tana Gama fada Mata maganar ta nufi hanyar ficewa daga dakin. Cikin fushi salmar tayo kan Zahrar ta fardota baya saura kadan ta Fadi dai dai lokacin Kuma sahura ta shigo zatayi musu sharar yamma ta tarar da wannan badakalar, da sauri ta shiga ts
akanin tana Basu hakuri ta Kama salmar ta fita da ita daga dakin tana faman zagin Zahrar abinda ya janyo hankalin Amma dake main kitchen din gidan tana yiwa Abba gas meat saboda Yana sonsa sosai yawanci idan Yana gida kusan duk dare sai anyi Masa shi.
Da s
auri ta fito tana tambayar "me yake faruwa ne?"
Sahura ce ta fada Mata abinda ta shiga ta gani tsakanin Zahra da salmar, juyawa kawai Ammah tayi ta koma taci gaba da aikinta Bata Kara lekowa ba tanaji Mama ta fito tana fadan daman ai ba tun yau ba ta fuska
nci Zahra ta Raina Salma, Kuma komai runtsi dai Salma ai gidan ubanta ne Nan ba Mai hanata sakewa.
Zahra ce ta fito zata wuce zuwa part din Ammah,har ta gota Mamar batace komai ba, Mamar tace.
"To fiqe kafi qaya tsini da Kika Samu guri kina yanda kikeso a
gidan wallahi duk rintsi bazaki Kai matsayin 'ya'yan gida ba, tunda har abada ba'a canzawa tuwo suna"
Har zahra tayi kamar ta maida Mata martani sai taji bazata iya ba babba babba ne, kawai ta shige part dinsu.
Har Mama ta juya taji maganar Ammah daga baya
nta, dan harga Allah batasan Ammah ta fito main kitchen din ba, Sam duk da tana jiyo kamshi ta dauka a can part dinta take aikin.
Bata juyo ba Amman ta tsaya.
Ammar tace
"Haba Mama ban zaci haka daga gareki ba wallahi, cewa nake da Zahra da su Hameeda dau
ka daya ne a gurinki, ai saiki tambayi meya hada fadan?kiyi musu fadan gaba daya ba wai ki nuna Salma itace taki ba, kina fadin maganganu irin haka ai na dauka ni duk binda lauje ya yayo a gidan Nan ya kamata ki dauke shi ciyawa ne na gode amman ki sani Ba
nda komai nufin Allah ne Zahra tafi karfin ace Mata 'yar karere tunda Mai gidan ne da kansa ya karbo rikon lokacin da aka nemi tafiya da ita kema Kuma sheda ce kinsan su waye kakanninta ba bakinki bane, dukiya idan ana gadonta kinsa Zahra 'yar mun gada ce,
ko shi Wanda kike takama da dukiyar tasa yasan tazarar da nisa a tsakaninsu da kakanninta idan kina tunanin karya ne idan yazo ki tambaye shi ze Baki cikakken bayani".
Bata jira taji abinda mamar ke kokarin fada Mata ba tayi gaba abunta ta nufi part dinta
.
Tun daga ranar Ammah ta daukewa Mama wuta gaisuwa kawai ke hada su, a kwana na biyu da Mama ta karbi girki ta kasa hakuri ita abin yafi damunta ta fadawa Abban Ammah Bata Mata magana, yayi mamaki matuka da gasken gaske Dan wannan shine karo na farko da i
rin haka ta faru da matan nasa duk tsawon shekarunsu. Bai taba rabasu akan sun Sami matsala ba Koda wasa, dan haka ya Kira Ammah a waya yace tazo part dinsa Yana son ganinta.
Batayi mamakin ganin Mama a zaune ba tasan za'a Rina tunda kaf tasan halin Mama n
a zahiri.
Gaishe da Abban tayi suka Kuma gaisa da Mama, tambayar ta Abban yayi ko akwai abinda ya hadasu da Ammah ne?.
Ba wani kwana kwana ita Daman tun can baya Bata da munafurci ko kadan. Dan haka ba wani ta fadawa Abban duk abinda ya faru tunda Saida ta
tutsiye Zahrar akan ta fada Mata abinda ya hadasu da Salma da kuma abinda mamar ta fada, shi kanshi Abban yayi mamakin abinda Salma tayi sosai, itama Mamar ya nuna Mata kuskurenta na fadar wannan maganar ya Kara da cewa.
Ban tabi yiwa zahra kallon ba nin
e na haifeta ba, bil hasal ma shine dalilin da yasa ban aura Mata Daya daga cikin 'ya'yana ba, ita kadaice ba uwa ba uba tun batasan inda kanta yake ba, mu ta sani a matsayin iyaye sauran yaran Kuma 'yan uwanta. Idan na aura Mata wani a cikinsu ba zata Zam
a feel free tare da ni ba, idan damuwa ta shiga ba Wanda zata fadawa kinga ai anyi adoh badan kyau ba".
" Haka ne suka fada.
"To karna Kara Jin makamanciyar irin wannan maganar, ba Wanda ze kawo min rarraba kan iyalin gidana. Zahra 'ya tace kawai na saka s
unan mahaifinta ne Dan haka shari'ar musulunci tazo dashi, badan in nunawa duniya bani na haifeta ba, a kiyaye kodon gaba".
"In Sha Allah".
Suka fada.
Bayan tafiyar iyayen yasa suka turo yaran yayi musu fada sosai sanan ya Kare da nasiha.
Tun daga lokacin
abubuwa na zahiri sukayi sauki sosai.
Kusancin Zahra da Hameeda ba abinda ya taba shi saima Kara shakuwa sukeyi a kullum suna Jin dadin butun, Zahra suna waya sosai da Ummee da Mama Hanifa harma da uncle Haisam a wasu lokutan.
Lokacin da hutunsu ya kusa
karewa duk sai Zahra ta nemi walwalarta ta rasa ko da yaushe kamar marar lafiya ana saura kwana biyu ta tafi Ammah ta matsa Mata taje Kiran da Baba malam yake Mata, dan sau kusan uku yana turo Yara tana cewa gata Nan Amman sai tayi burus da zancen.
Har dai
ta Kai Ammah karshe tayi magana. Hameeda tace ta rakata suje tare, yau gurin malam din ba kowa ba Kuma rumfar karatu tunda ranar basa karatu. Gurin ganawa da mutane suka sameshi su Habib suna ta gyaran Shirin kantar littafai.
Da sallama suka shiga suka ga
ishe da malam din sannan suka gaishe dasu Habib, sai sukayi shiru.
Malam ne yace "Zahra'u Ashe lokacin komawar taki har yayi ko?"
Kara risinawa tayi tana fadin "eh lokacin yayi yayi Baba gobe zan tafi in Sha Allahu amma a Istanbul zan tsaya sai wani satin
zan wuce syprus din".
"Masha Allah. Allah ya taimaka, ki Kara hakuri akan lamuranki duk wani bawan Allah na kwarai sai Allah ya jarabce shi Dan ya gwada imaninsa ki dauki abinda yake faruwa dake Daman haka Allah ya rubuta Miki taki kaddarar kada ki yanke
kauna daga Rahamar Ubangiji. Ga addu'oi nan da littatafan addu'a ki tafi dasu ki ringa yinsu Kuma kada a shagala da ambaton Allah a duk inda aka Sami kai, Allah yayi Albarka ya bada nasara ya kiyaye hanya".
"Allahumma Amin suka fada a tare".
Habib malam y
a yiwa magana ya Miko ledar da aka saka sakon nata, Hameeda ta karba suka Kara yiwa malam godiya suka fito suka shiga cikin gidansa Zahra ta Kara duba jikin iya Abun ta Kuma yi Mata sallama.
Basu koma gida ba, gidan su mujiba suka shiga Bata Nan ma sai Mam
an ta suka barwa sallahun tafiyar zahrar suka nufo gida, sunzo dai dai masallacin gidansu ne sukaga Ya Abdul Hakeem da Dodon Zahrar a zauna a kan carpet karami a gefen masallacin suna hira Kai da gani da kyakykyawar alaqa a tsakanin su.
Gaishesu sukayi suk
a wuce, Hameeda ce ta kalli Zahra tana fadin "Kinga wancen Guy din yanda Salma ta mutu kansa ba magana! lokacin data Fara ganinsa munzo hutu wallahi kamar zata zauce akansa sai da Mama ta taka Mata burki taci Mata mutunci akan ta rasa Wanda zata so sai Al
majira Wanda ba'a San asalinsa ba, duk yanda taso ta nunawa mamar wannan da banbancin da irin Wanda ta sani amma Sam taki fahimta Dan har so tayi tayi Mata duka tana fadin Dan lalacewa ta rasa Wanda zataso sai fakiri Mai allaziwahidin Dan salon Abba yaji y
a Goya Mata baya tunda Wai ance sune suka kawo shi garin bandai San kan labarin ba gaskiya". Ita dai Zahra Bata tofa tataba daga uhm sai umh umu uhm, har suka karasa gida.
A Daren sun raba dare suna Hira da Ammah a Nan ta dunga yi Mata magiyar ta daure taj
e gurinta ko zuwa karshen shekara ne ta ganota ba ta tura Mata Ya Abdul Hakeem ba.
Karfe shida Mai kyau sun dauki hanyar Kano ita da Ya Abdul Hakeem da Hameeda da magaji.
Nan suka zauna da zahra suna ta Hira kafin lokacin tashin su yayi, in da wani Abu da
ya damu Zahra a gurin Bai wuce kallon da wani matashi ya kureta da Shi ba, duk inda zata dago Kai sai sun hada Ido dashi, Sam ya hanata sakat da idanunsa idan ba idanunta kemata gizo ba har wani lumshe ido yake da wani kankance su. A haka har lokaci ya ci
ka aka Fara shiga jirgin hand bag ce kawai a hannun Zahra tunda kayan an tafi dasu tun zuwansu lokacin da ta juya ta Fara tafiya ba zato taji hawaye a idanunta abinda ta dunga kokarin kar tayi kenan tun daga gida lokacin da Auta Musaddiq ya fasa Kuka da su
ka taso Amma sai gashi ta kasa jurewa itama Saida suka zubu, juyawa tayi kadan lokacin da zata hau steps din sai taga Ya Abdul Hakeem ya Kama hannun Hameeda sun juya sun Fara tafiya tana share hawaye da dayan hannun itama ta juyo hannu Zahra ta dago Mata a
lamar bye sannan ta Haye zuwa ciki.
Kusa da wata Mata ta zauna da alamar kamar zatayi sa'ar Ammah, ta gaisheta.
Saida jirgin ze tashi ne taji na gefenta Yana fadin "duk tunanin gidan ne ya hanaki jin sanarwar a daura belt da ake ne?" Ya fada in a soft vo
ice. Dago Kai tayi ta dubi Mai maganar dake gefenta, wannan Wanda ya dameta da kallo ne kafin su shigo, ita Sam batama San sanda ya zauna kusa da ita ba.
"Nagode" ta fadawa tana saka belt din lokacin da jirgin yayi balance a sama ne ta cire belt din ta bu
de computer dake jikin kujerar dake gabanta tana kallon location din da Suke bi tun tana Gane garuruwan data sani ko take jin sunansu har aka shigo Wanda sai dai ta karanta kawai. Jefi jefi suna Dan magana da matar dake kusa da ita. Nan kusa da ita dai Bat
a Kara kallonsa ba tunda taga shi kallon mutane kamar dabi'arsa ne.
Sanyi kamar tafiyar awa daya taji yana Mata magana da farko yi tayi kamar bataji ba, Saida matar dake kusa da ita tace "bakyaji ba ana Miki magana, ko kina da aurene?".
Kai ta girgaiza ala
mar A'a.
"To meyasa kina Jin Yana Miki magana Kika kyale shi? ba Dadi irin haka baka wulakanta mutum ba kasan gaba abinda Allah zeyi ba kinji".
A hankali take Mata maganar yanda ita kadai zata iya ji.
"Tom nagode in Sha Allah zan kiyaye". ta fada mata.
Ba
i hakura ba har Saida ya Sami kan Zahra duk da ba wani sakewa tayi dashi ba Amma dai hakan yayi masa.
Lokacin da suka sauka haka ya dunga bin Zahra kafa ya kafa har ta dauko kayan ta da aka gana screening suka fito, a Nan ya fada Mata sunansa Mushahu shi D
an Kano ne Yana aikin government Yana Kuma kasuwwnci yanzu ma harkar kasuwancin ta kawo shi kasar. Zahra ma ta fada Masa sunanta da inda take karatu da Dan zaman da zatayi anan kasar kafin ta wuce.
Bai bar airport din ba har Saida Mama Hanifa tazo daukar
zahra, da yake Mushahun wise ne sosai ya sake da Mama Hwnifar don Basu rabu ba har Saida ya karbi address din gidanta, saida suka bacewa ganinsa sannan Shima ya nemi taxin cikin airport ya nufi hotel din da yake sauka idan yazo kasar da buri kala kala a zu
ciyarsa kan Zahra.
Satinta daya ata nufi syprus kafin lokacin Mushahu ya Kai Mata ziyara yafi sau hudu ba karamin samun shiga yayi a gurin Mama Hanifa ba.
Zauwanta makaranta da kwana daya Sajida da Khadijah da Fatima suka dawo Anisa ce Bata dawo ba suna U
mara da Yayarta sai Kuma sukayi Dan Samu matsalar visa.
Karatu Suke ba Kama hannun yaro Koda yaushe suna busy da karatu, tunda Zahra ta rabu da Musbahu a turkey Sam ta aje batunsa a gefe duk da kusan Kullum saiya kirata sun gaisa Yana ta kafa gwamnatin sa
a gurinta. Bazato ba tsammani ranar wata Saturday taje weekend gidan Uncle Haisam ya kirata da number din kasar Yana fada ya shigo kasar tayi jiransa Nan da awa daya ze shigo makarantar, ba karamin mamaki tayi ba da jin hakan, dan harga Allah batayi zaton
da gaske yake ba da yace Mata Yana Nan zuwa syprus din.
Nan da Nan ta fadawa Aunty Jinan matar uncle zata koma school yau suna da wani group Assignment data manta zasuyi ta taho, Bata Hana ta ba tunda Daman uncle din baya kasar sunje wani aiki south Korea,
snacks Aunty jinan ta hada Mata masu yawa ta tafi dasu. Allah ya taimaketa ta fito da card dinta na shiga bus ko train, mintina talatin masu kyau suka kawota kyrenia city.
Lokacin data shiga hostei dakinsu ta wuce ta Kara gyara jikinta.
Wani karamin bask
et da dauko ta zuba snacks da drinks masu sanyi, turare ta Kara fesawa har Brandy wadda Suke daki daya take tambayar ta ko zataje wani park ne ta huta yau weekend?
Eh kawai tace Mata tayi gaba ta fita daga