Showing 18001 words to 21000 words out of 295116 words

Chapter 7 - AUREN HUCE HAUSHI COMPLETE

nayi duk yanda zanyi Amma abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaski

ya Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake ne Kawai mafita".

"Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?".

"Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole sai da Kai za'ayi Dan haka suyi

hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar tafi yi maka armashi ko?"

Ya fada cikin zolaya.

"Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da zuwan ka turo wannan friend din n

aka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai Kuma ka Kira Baba malam ka fada Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake ciki baze wuce kwana buying zuwa uku ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son n

a barta a Nan gidana akan na tafi Bata tare ba".

"Ko dai.......?"

Sameer ya fada Yana dariya.

"Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai ku".

Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta.

Misalin karfe Sha biyun R

ana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam.

Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki nufi falon malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar Masa da kayan daga Sameer.

Malam y

ayi godiya ya saka Albarka ba adadi.

Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan suka gaisa da Mahmud din.

Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki.

Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da a

n jima za'a Mika musu can gidan Alhajin.

Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta gani malam yace ta turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu.

Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fad

awa Alhaji yanzu su malam Mudi da Alaramma malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u.

Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min haka ko wancen da aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa nayi suj

e da kayan idan tazo saiya ba matarsa".

Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba wannan yaron Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya"

"Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan

sai wance Allah ya saka da Alkhairi ya bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe Masa ido ba".

Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba Nan take makotansu suna dasawa da Zahra sosai sun K

uma yi sabo sosai da Sajida tun lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar lokacin suna makaranta.

Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai Zahra na ganin haka ta tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta ka

rasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu da zuwa, sai daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda ya kula ta, di

rectly dakin Mama ta nufa.

Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa da sauri Zilai Mai aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin "Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara Mai farar aniya suk

ari bakai farin banza Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi, Amarya gidan Mahmud Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki ya sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin da

ga dakin Ammah Inna maimuna ta fito.

💋







💋





AUREN HUCE HAUSHIN



💋







💋





WRITTEN

BY

MAMAN FATIMAH

PAGE NINE

🔷

(9)

____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, g

uda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya"

Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fansh

i jikata tunda kin koma roko".

Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanza

ro a bene" .

Ta Kara kwarara wata gudar.

Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki"

Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke f

ama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne.

Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun.

Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade

fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau.

Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin.

Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah.

Sa

i da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra.

Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kay

an kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba.

Mama

ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika d

angana da gurin kanwar uwarki".

Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa.

"Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa"

Tana Gama fada ta shige uw

ar daki.

A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra.

Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu.

Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Am

mah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana.

Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani

ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa.

Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake faruwa

************_

_

TUSHEN LABARIN

AZARE KATAGUM L.G.A

BAUCHI STA

TE

UNGUWAR FAMFON SHANU.

Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne h

ar baka bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah s.w

.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi amfani dasu ka

wai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi".

Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki

fa kiji".

Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya.

"Kai Kuma dariyar me kake?"

Ammah ta tambaye shi.

Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar "Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu y

ake min dariya Kuma nace ya tayani daukar jikar ya Kiya".

"Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu".

Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari.

"Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam

Bala harya kawo mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya so

n jiki ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki, shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta biyani Kamar wani Dan dako".

Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin

dariyar Kuma wallahi kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba".

"A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su

Hameeda kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa karatun ba kanta ba".

Ya fada Yana cire safarsa.

Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kaf

in taci abinci saboda Bata son ta makara a islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke sallar Azahar.

Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga dakin Mama ta biya Hameeda ne

taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito tana zumburar Baki.

"Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda".

Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama hanya ki wuce, ko za

ta ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa"

Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba Mai jin abinda take fada duk da Amma

h na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da bangaren na Mama.

Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah na tafi"

"To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi".

"To" ta amsa ta nufi waje da sauri.

Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari Tasha a gi

dan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke 'yar riko ce.

Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko.

Da Ammah ta tsareta ta fada M

ata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu ba".

Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "

itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji" kai ta gyada alamar to.

Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki na ciki ne ta baka na ba

ka.

Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar, daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara.

Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta gaishe da Ammah ta zauna s

ukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta Kai Masa abinci.

Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda za'ayi, Ammar ce ta zaun

a tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta.

Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku ranar Saturday zakiyi jarabawar share f

agen shiga karamar secondary school ta kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci gaba a makarantar da yake".

Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama.

******Alhaji Jafar Mai yadi haifaff

an garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da

Nanna, kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary.

Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa b

a daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna jarinsu.

A hankali

Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka.

Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara

bunkasa da taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa k

okarin shago kafin ya dawo.

Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Al

lah ya samu course din da ya nema Agricultural science.

Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta

fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu.

Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba.

Wata

ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa.

Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta n

ufa tunda tasan shagon nasa.

Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?"

Dariya tayi kyawawan hakoranta j

erarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni".

Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gida.

Da dare Yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login