Showing 141001 words to 144000 words out of 295116 words
yana hasaso inda yasan face din amma ya kasa ta
ntancewa ke nan DANGE shine mijin da aka aurawa zahra a matsayin Almajirin Alaramma? take a nan yaji wata irin karaya ta mamaye masa zuciya yasan ya rasa zahra har abada, shi dinwa da ze iya ja da wannan dan tahaliki, ko manyan manajojinsa bai isa yayi tak
ara dasu ba kafin ma a kai ga P.A dinsa.
Cikin nuna tsantsar karaya ya cewa Faruq.
"Ban gane shi ba sai bayan ya wuce, ina labarin dana baka dazu akan fasa aurena da akayi?" Kai Faruq ya gyada masa yana fadin "Na gane bana yarinar nan 'yar Azare ba?.
"Eh t
o ai wannan ta cikin motar itace yarinyar da nake fada maka kuma tabbas shine aka aura mata a matsayin Almajiri kolo, bari na nuna maka hotunan daurin auren, dan wani yaro nasa ya turo min hotunan na dade ina tunanin inda nasan fuskar Amma ban taba ko hasa
shen shine ba, tunda nasan meze kawo shi Azare harda zaman Almajiranci".
"What!!! Almajiranci kuma?
"Yes of course, bari na nuna maka pictures din ka gani". Ya fada da kyarin gwiwa duk da karfin hali kawai yakeyi hankalinsa idan yayi dubu a tashe take.
Ya
ciro wayarsa daga cikin aljihun wando ya shiga gallary ya nemo hotunan, cikin sauri da zaquwa Faruq ya karbi wayar, da Sameer ya fara cin karo a hoton yana kusa da Ya Mahmud sai kuma wadanda be sansu ba, a hankali ya ringa duba hotunan tabbas Ya Mahmud ne
tunda ga P.A dinsa nan wato duk tunanin da akeyi yana turai ashe yana Bauchi state saboda tsabar iya bada kafa.
Dago da kai yayi yana kallon Uncle din nasa da mamaki fal fuskarsa.
"Na gani tabbasa wlh shine, to amma ta yaya hakan ta faru? nayi mamakin aure
n daka fada min yayi, bafa wanda yasan inda yake ya yanke hulda da kowa fa, yanzu na gama fada maka irin badaqalar da aka sha a family din wanda yasa ya tsallake yayi tafiyarsa, uncle sorry bari na bishi hankalina baze kwanta gani nake kamar dabara yayi mi
n ya gudu".
Kai kawai Musbahu ya iya jinjina masa, yayi hanyar ficewa da sauri, yana fita Allah ya kawo adaidaita ba kowa ya tare ya shiga saida suka fara tafiya ya fada masa Hausawa Bawo road.
Tunda Mahmud ya fice daga harabar sahad store ya saki motar
yana wani irin tuki, ko iskar data aje zahra be duba ba itama takurewa tayi jikin kofa da gaske shakkarsa takeji dan ya hade gabas da yamma kudu da Arewa, ya doki sitiyari yafi sau shurin masaki.
Ita dai zahra sai addu'a take Allah ya sauke su lafiya, gaba
n wani gida taga ya tsaya Mai shegen kyau haske ya cika ko Ina da karfi ya danna Horn din kamar ance masa Mai gadin sabon kurma ne, da sauri ya fito ya nufo motar banban mutum ne ba yaro ba, ganin baisan motar ba yasa ya karaso da sauri ganin Wanda yake
wannan mahaukacin horn din.
Bazato yayi arba da Mahmud, da sauri ya zube Yana kwasar gaisuwa, hannu kawai ya iya d'aga Masa da sauri ya koma har Yana hadawa da gudu yaje ya bude gate din, da gudun dai ya shige har kofar ya nufi ba parking space ba, kofar d
a zata sadaka da main parlourn ya tsaya ko motar be tsaya kashewa ba ya zagayo ya bude side din zahrar take zaune yasa hannu ya fisgota waje, be saurari komai ba ya nufi steps din shiga ciki da ita, ganinsa kamar mahaukacin Zaki ya saka zahra cikin tashin
hankali, da hannu Daya ya zura katin ya bude kofar, be tsaya a parlourn ba direct upstairs ya nufa da ita tana turjewa tare da fasa masa kuka Dan wani irin riko ya yiwa hannun Kamar ze tsinke Mata tsintsiyar hannu, be saurareta ba Saida ya dangana da inda
yayi niyya bedroom din da suke sama guda uku, ya nufi na kusa dashi da karfi ya tura kofar da suka shiga yasa kafa ya Maida kofar,Kan wani lafiyayyan Turkish bed yayi musu masauki, yana zuwa Bai bi takan kukan da takeyi ba ya saka hannu ya fisge Rolling di
n da tayi yana huci.Dan magana ma ya kasayi saboda wani Abu da yake taso Masa, baya tayi da sauri ganin Yana neman cakumo rigarta, Kan gadon ya hauro Shima ko takalmin kafarsa be cire ba, Rigar jikinsa ya cire yayi jifa da ita, ya kamota tata Rigar ms yasa
hannunsa ya karketa tun daga sama har kasa, take jikinta ya bayyana, ya kasance daga ita sai farar bra tas da farin pant a jikinta,jikin Nan sai wani glowing yake kamar kifi tarwad'a, cikin tashin hankali da matsananciyar kunya ga kuka take fadar "Dan Al
lah kayi hakuri me nayi maka wallahi bani na kirasa ba, shine ya ganoni ya taho ko magana banyi Masa ba,ai kana kallon mu, wallahi bansa zasuzo ba ba Kaine ka kaini gurin ba?".
Ta fada tana kankame jikinta.
Duk abinda ke jikinsa ya cire ya jefar, Shima Dan
ganinta a haka ba karamin bijiro Masa da tsohon tsimi yayi ba Rabon da yaji haka tun karonsu a Azare lokacin data farfada Masa maganganu Hannu yasa ya fisgota jikinsa ya fisge brezier da karfi ya jefar, Yana fadin.
"Daman kun shirya had'uwa dashi shine
yasa Kika gudu d'aga gidan Hajiyar ko? saboda ki samu damar sheke ayarki tare dashi tunda be aureki ba ai sai kije yayi abinda yaga dama dake ko? Niga sakarai Wanda besan inda yake masa ciwo ba, yau basai gobe ba zamu raba wannan rainin ni dake, ganin na d
aga Miki kafa Ina tausayinki yasa raini ya Fara shiga tsakaninmu ko? abun har ya Kai a gabana ake neman rungumarki wlh da yayi wannan gangancin Daya gane maza suna suka tara, idan kina cikin matsuwa saiki fada min ba kije kina kyarkyara ba a waje na isa na
yi satisfied din duk fitinarki yarinya, sarauki ne ni Zan iya da duk bukatarki, ya Kamo hannunta ba zato taji ya Dora shi a......."
Cikin wata irin zabura tayi wani juyi kafin ta Kai ga sauka ya cakumota gaba dayanta ya dawo da ita jikinsa, jikinta sai tsu
ma takeyi kamar ana kada Mata gangi.
Dai dai kunnan ta ya saka Bakinsa.
"Ina Zaki ai yau no way out, badai abinda kike muradi ba kenan?Baki da matsalarsa na fiki finita Dan haka kizo mu kwada daga Nan zuwa wayewar gari". Yana gama fada ya hade bakinsu guri
daya Dan kukan ta nema yake ya karya Masa zuciya.
Da zafi- zafi yake tafiyar da ita Dan da gaske duk wani Alkawari ya jingine shi a gefe yau jinsa yake kamar mayunwacin zakin da ya kwana uku baici nama ba ko yaron Daya wuni baisha Mama ba Saida tafiya t
ayi nisa yaji labarin ya canza salo dan shi harga Allah ya wani manta tani wani period.
Kankameta yayi Yana wani irin numfashi har Saida tsoron da tajeji ya ninku ta dauka ko somewa zeyi cikin wata dasheshshiyar murya yace Mata "marata ciwo take min duba
dakin tsakiya ki dauko min wani magani a cikin kwalba a bed side din jikin gwdin " ya Kamo hannunta ya Dora akai taji wani dumi a marar tasa, matse hannun nata yayi Yana sakin wani Nishi cikin galabaita, take ta Kara rudewa da sauri ta tashi ta daura gyal
en ta tunda Riga ta tashi daga aiki da sauri ta fita tana waiwayensa ya rintse idonsa hannunsa Yana Kan mararsa.
A bude dakin yake Bata tsaya kallon dakin ba, bedside din ta nufa direct cikin ikon Allah wadda ta Fara dubawa a Nan taga kwalbar da kananun ta
bles a ciki, har zata fito taga irin karamin fridge a dakin, budewa tayi da sauri cikin sa'a ta samu ruwa a ciki ta dauki Daya ta fice da sauri tana shiga ta nufe shi da sauri tana Fadi tashi kasha ga maganin, taji Shiru Kara matsawa tayi tana Masa magana
Nan ma shiru taji da sauri ta hau gadon tana girgiza shi cikin tashin hankali.
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH.
P. 49
______ Duk budirin da take Yana jinta tana ta faman jijjiga shi Sai da yaga da gaske hankalin
ta ya tashi sannan ya dago kansa Yana kallonta da hargitsatstsun idanunsa, wata ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta kauda idanunta da gasken gaske wani irin nauyinsa takeji, matsowa jikijnta yayi a hankali ya sakata a jikinsa Yana fitar da numfashi a jikin
wuyanta, wata irin kasala ta kara saukar mata gashi ba halin kwacewa ya kanainayeta ta ko ina.
Cikin kunnenta yayi maganar da wani yanayi Mai wuyar fassarawa. "bani maganin na Sha".
Da sauri ta Mika masa 'yar kwalbar, jikinta ta janye da sauri ta dauko ro
bar ruwan data Dan gangara wurin karshen gadon.
Kwara biyu ya Ciro maganin ya karbi ruwan ya watsa maganin a bakinsa yabi da ruwan, Saida ya shanye shi tas sannan ta karbi robar.
Zanewa yayi ya kwanta rigingine, hannunsa Yana dafe da goshinsa Dan ji yayi k
ansa Yana wani irin Sara masa, ganin haka yasa zahra janyo blanket din ta rufe jikinta dan itama har lokacin jikinta Dan karkarwa yake mata daga ciki.
Sun jima a haka kowa da abinda yake sakawa a tasa Zuciyar, Amma ita zahra Hamdala take ga Allah Daya tarf
awa garinta nono, tab da yanzu ba wannan batun akeyi ba, tsikar jikinta ce ta tashi sharrrrrr.. jikinta ta kankame guri Daya tana ayyana wani Abu a cikin ranta, Jin motsin tashinsa tayi, dan waiwaya inda yake kwance tayi taga ya tashi ya nufi toilet Yana h
ada hanya.
Har ranta taji tausayinsa sai dai tafi tausayin kanta a kan halin da yake ciki.
Ya jima tsakiyar ruwan sanyi Yana dukan jikinsa,sai ajiyar Zuciya yake saki ba kakkautawa tamkar yaron Daya wuni kuka baiga uwarsa ba, Saida ya samu nutsuwa sosai sa
nnan yayi wanka ya fito har lokacin tana kudundune a cikin blanket din.
*
Har gate din gidan Mai adaidaita sahun ya kawo Faruq yana fadin "Yallabai kayi muhalli Mai kyau Allah ya kawo abokiyar Zama ta gari Masha Allah".
Shi dai Faruq hankalinsa in y
ayi dubu to Yana Kan ya shiga yayi arba da Ya Mahmud dinsa badan yaso ba ya taho ya barosa, yaso kafarsa kafarsa su taho dan gani yake kamar guduwa zeyi ya rasa inda ya shiga, kudin da baisan adadinsu ba ya Ciro ya mikawa Mai Dan sahun yayi gaba. Yana Jin
Mai Dan sahun na fadin " Yallabai kudin fa sunyi yawa ka duba kuwa?"
Bai waiwayo ba ya dago masa hannu Yana fadin "kaje ka Kara petrol da sauran". Yayi gaba abinsa, yana jiyo yanda yake kwararo Masa addu'a kamar ba gobe, da yake irin mutanen Nan ne m
asu kaifin harshe kamar jikan maroki.
Sau biyu Faruq yayi knocking din gate din,malam Musa ya leko ta kofofin dake jikin gate din, ganin shine yasa da sauri ya bude Faruq din ya shigo, sun yiwa juna farin sani tunda sun Sha zuwa da Mahmud suna kwana idan
wani Abu ya kawo su kanon, sauda yawa anan gurin malam musan yake zama idan baya son fita ko Ina.
Cikin mutunta juna suka gaisa malam Musan yake fadar "Ashe tare kuke da yallaban Amma kunyi shigowar dare gaskiya, kaga motar can ma a kunne ya barta Naga ka
mar Matar tasa Bata Jin Dadi, dan da sauri suka wuce ciki ko motar Bai samu damar rufewa ba, nayi mamaki da naga yau yallabai da kansa ma yake tukin motar".
'yar dariya Faruq yayi, Bai tofa ko kalma Daya ba akan maganar tasa da yayi akan Ya Mahmud din, gur
in da motar take Ya nufa Yana fadin.
"Ina zuwa Baba Musa Bari na gyara parking din".
Zuciyarsa fari tasss, Daya samu Mahmud a gidan ba kafa ya bashi ya gujewa haduwarsu ba kamar yanda ya yanke hulda da kowa, bai San Yana da irin wanna Zuciyar ba Saida aka
samu matsalar, Amma Abu mafi daure Kai yanda Baba Musa yasan matarsa ce har yake fada Masa, ko a Ina ya samu labarin dasu Family dinsa Basu sani ba?.
Saida ya Kai motar parking lot sannan ya dawo gurin Baba Musa ya zauna suka Fara Hira, tunda mutuminsa ne
sosai, sai da sukayi nisa a hirar sannan Faruq ya tambayi Baba Musan ko da sabuwar lambar Ya Mahmud a gurinsa shi ya baro wayarsa Mai sabuwar lambar a gida, tunda ya fada Masa ba tafiyar su Daya ba, shi biki yazo garin, shine ya shigo tunda ya fada masa Ya
na garin.
Ba musu ya Miko masa wayar yana fad'in.
"Duba ka gani Nima jiya jiya nan ya kirani da ita yake fada min za'a kawo kayan gyaran wancen sabon ginin da aka Gama".
Ya fada Yana nuna Masa inda su Mahmud din suka shiga.
Number ya saka a wayarsa ya maid
a Masa wayar Yana fadin "dauko min keys din wancan part din na shiga na kwanta na gaji sosai".
Dakinsa ya shiga ya fito Yana fadin gasu ka duba niba banbancewa nakeyi ba. Amsa yayi yayi masa sallama ya nufi part din Zuciyar sa fal da tambayoyin Daya Kamata
ace ya yiwa Baba Musan Amma gudun bada wata kofa da za'a Sami wata kofar sanin wani abun yasa yaja bakinsa yayi shiru.
Har Mahmud ya shirya cikin pyjamas dinsa sky blue tana kudundune a cikin blanket din, duk Kai kawon da yake tana jinsa amma ko motsin k
irki batayi ba, sai ya Gama komai ya nufi kofar ficewa daga dakin ya juyo kadan Yana Kare Mata kallo da gaske ita ce rauninsa yaga alama, a hankali ya koma cikin dakin yaje har inda tayi wurgi da hand bag dinta ya tsuguna ya dauka ya koma gefen gadon ya za
una ya bude jakar, wayarta ce da sauran tarkace irin na Mata sai ATM cards dinta da 'yar robar maganinta a ciki na wajen Hajiyar makwarari, ATM'S din ya dauke da wayar da sauran kudin data Ciro jiya a Hanyar Janbulo, harya mayar da jakar ya ajiye sai kuma
yayi saurin Kara daukota kamar Wanda aka tsikara ya Kara budeta cikin wani zip na gefe ya bude takardu ya gani ya cirosu duka passport dinta ya gani da wasu magungunan da aka Bata na Asibiti sai takardun tests da akayi Mata na Azare Dana Nan kanon.
Passpor
t din ya dauke ya hade da abubuwan daya dauka ya Mike ya fice daga dakin yana saka Mata alamar tambayoyi masu yawa.
Saida taji ya fice daga dakin da kusan minti goma sannan ta samu zarafin tashi zaune tana Dan turo Baki tana 'yan matanganunta a ciki Wanda
ita kadai tasan me take fada.
Sai lokacin ta shiga bin jikinta da kallo ita fa duk ya dagula Mata Lissafi. Banda taimakon Allah da yanzu ba wannan batun akeyi ba, tsikar jikinta ce ta kara tashi yarrrr kankame jikinta tayi tana sauki wani malalacin numfash
i, tare da furta "Narrow escape".
Ta Kai dubanta inda yayi Mata wurgi da kayan jikinta, ita har zuwa lokacin ta rasa meya tunzura shi haka daga ganin Musbahu ita ba ita takai kanta ba, ba ita tace ajeba ballentana yayi tunanin setup ne.
Itama wankan ta shi
ga yi tana zuwa ta duba jikinta cikin ikon Allah period din ya dauke Daman tun safe taga alamun hakan duk pad din data saka a yinin haka nan take cirewa, ta yanzu ma hakan ce ta kasance, tayi hamdala ga Allah tafi a qirga wato ba karamar kariya wannan pad
din ta Bata ba.
Wankan tsarki tayi tare da wankan sabulu ta fito daure da towel, yanzu ta Zama 'yar gari gurin suturar sakawa, gurin kawai ta nufa ta Ciro Riga da wando sleeping dress masu rawa ta saka ta dauko hijabi ta shimfida sallaya ta tayar da sallar
magariba da insha'i.
Mahmud Yana fitowa dakin Daya tura zahra dauko Masa magani ya shiga, direct wurin wasu lokoki ya nufa a ta tsakiya ya bude ya zuba duk kayan daya dauko a Jakarta, wayar kadai ya rike a hannunsa.
Kira ne ya shigo wayarsa yana dubawa
ya gane number Faruq ce.
"Ya Salam". Ya furta a hankali wallahi ya manta da batun Faruq kwata kwata Saida yaga kiransa ya tuna Daya hadu dashi ma, to Ina ya samu wannan number din shidai yasan be Kira wasu mutane da yawa ba da layin Dan sabo ne jiya ya Far
a amfani dashi, sai Kuma ya tuna ya Kira malam Musa dashi jiya yasan a gurinsa ya karba, tasowa yayi ya nufo parlourn farko Yana dealing number din Faruq din.
Yana dagawa yace Masa "ka shigo sabon part din nan ka sameni a parlour". Ya yanke Kiran..
Cikin k
ujera two seaters ya zauna a kasalance badan Shima Yana Jin kishirwar haduwa da Faruq din ba da Babu abinda ze fito dashi ba.
Fitowa yayi da zummar dauke motar Daya Bari a gurin, ga mamakinsa Bata gurin a parking space ya hango ta, Dan murmushi yayi yasan
aikin Faruq ne.
A Nan ya tsaya ya Zuba hannunsa a cikin aljihun rigar Yana shaqar iskar dare da take kadawa a hankali Mai dadi, malam Musa ne ya hango shi a tsaye a gurin da sauri ya nufo gurin Yana fadin "barka da dare yallabai anzo lafiya?".
Hannu ya Mi
ka masa duk da nokewar da malam Musan yakeyi sai da sukayi musibaha. Mahmud din na fadin "lafiya kalau Alhamdulillahi, nagode kwarai, ya iyalin naka da jikin".
"Wallahi Alhamdulillahi