Showing 180001 words to 183000 words out of 407268 words

Chapter 61 - Raina Kama COMPLETE





Da sallama ya shigo, amma saiya isketa baje a gado tana shak'ar barcinta, yad'an murmusa kafin ya k'arasa ya zauna a bakin gadon saitin fuskarta, yatsunsa biyu yasaka a gefen wuyanta dan yasan da wahala wannan barcin ya kasance na lafiya, aikam jikinta rin

gim yake da zazza6i, tausayinta ya kamashi, lallai uwa dabance acikin al'umma, Ashe haka sukeshan wala, tundaga d'aukar cikinma zuwa rainonsa, akoma rainon yaro, daganan tarbiyarsa, lallai masu raina mata ko kallonsu masu k'arancin tunani sune masu k'aranc

in tunanin ai, ya d'an lumshe idanunsa yana cije lips, ganin ta dunk'ule a waje d'aya saiya ja bargo ya lullu6a mata, harya mik'e ya koma ya zauna, risinowa yay kanta a hankali ya mannama goshinta kiss, sannan yamik'e ya fice.

Koda ya dawo saiya wu

ce d'akinsa, yabar su Aiyaan suna kallonsu.

Kayan jikinsa ya cire ya kwanta shima, dan yana buk'atar hutawa kona 2hours ne, kwanciyarsa kuwa babu dad'ewa barci ya saceshi.

Kiran sallar la'asarne ya tashesu kusan lokaci d'aya, Galadima yatashi

da k'yar, a mamakinsa sai yaga Aiyaan da Aryaan kwance a gefensa suma suna barci, murmushi kawai yayi yasako, saida ya watsa ruwa sannan yay shirin tafiya massalaci cikin k'ananun kaya.

Harzai fita saiya dawo yashiga wajen Munaya. tana tsaye gaban w

ardrobe tana neman kaya, da alama wanka tayi, dan daga ita sai towel.

Banji sallamarsa ba, saboda shi idan zaiyi magana bayason bud'e baki, ganin batajishiba saiyayi gyaran murya, a tsorace na waigoshi, ganin shine nai saurin saka kayan dana d'akko

ina kare k'irjinna da tura baki, bakinsa ya d'an ta6e, sai kuma ya shiga takowa inda nake, duk takun da yayi sai gabanna ya fad'i, na waiga kozan samu nabar wajen ko abinda zan suturta jikinta sosai, amma sainaga babu a kusa, kuma ina jikin wardrobe d'inne

sosai ai. ban gama yanke shawara ba ya k'araso daf da ni, kuma matsawa nayi na matse jikinna sosai a drowa d'in, shikuma yawani had'e gabas da yamma, wannan ne yakuma sakamin tsoronsa a raina, na zata kowata tsiyarce ta kawoshi.

Hannu yasaka ya d'ag

o da ha6arta muka kalli juna, ya tsareni da idanu yanda nakasa janye nawa cikin nashin, munkai kusan 2minutes a haka, kafin yakumamatsoni sosai, ya kai fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, dan haka saina lumshe idanu, murmushi yayi ya hura mata i

ska akan idanun, ta rumtse idon sosai, ya d'an ja baya yana ta6e baki, kafin yasaka hannu ya cire nata dataketa faman kare k'irji da kayanta, still ya kuma matsawar saitin kunnenta yana fad'in “wane darene jemage bai ganiba yalla6iya”. ‘ya k'are maganar da

shafa kirjina ya fice abinsa.

Kad'an yarage namasa ihu wlhy, aiko yana fita na durk'ushe a wajen ina sauke numfashi, sometimes nakan rasa yazan fassara Galadima da ayyukansa.

Da k'yar Na iya tashi nayi sallar nakoma kan gado Na kwanta.



Galadima kam daya fita dariya ce taita cinsa, ya kula Munaya akwai tsoro, kuma haryanzu a tsorace take dashi, cikinnan ne kawai kanci galaba akanta yake samunta cikin sauk'i, ya girgiza kansa kawai yana murmushi.

Bayan ya dawo massalaci d'akin nata

ya dawo, dan yanason suje su gaida jama'ar gidan, maybe gobe suje masarautar papi ma.

A kwance ya iskeni, nak'i kallonsa, jingina yay da mirror yana fad'in “yaya jikin naki?”.

Ban kalleshinba nace, “da sauk'i”.

“ALLAH ya k'ara

sauki, idan zaki iya tashi ki shirya muje cikin gida, kafin waccan tsohuwar tafarama mutane surutu”.

“to” nafad'a ina mik'ewa, Na sakko a gadon, harna nufi wardrobe zan d'auki alk'yabba saina tsaya, batareda Na kalleshi ba nace, “toka fita Na shir

ya”.

Hard'e hannayensa yayi a k'irji yana fad'in “ashe bazaki shirya d'inba, dan bazanje ko inaba”.

“karkaje d'in, ai akwai bayi” nayi maganar a zuciyata.

Kayan Na d'auka na shiga toilet, shikuma ya ta6e baki.

Babu dad'ewa na

fito tsaf, nayi k'yau, nazo ta gefensa na d'auki turare nasaka kad'an sannan na kallesa nace, “na shirya”.

Baice komaiba ya nunamin hanya, gaba nayi yana bina a baya muka fice.

Kasancewar tazarar dake d'an tsakaninmu da sassan nasu muka shiga

mota, dan banajin dad'in jikinna, bama zan iya tafiyarba.

6angaren Abba hayatudden muka fara zuwa, daga nan sai sashen matan mai martaba, soyayyar da uwargidansa ke nunamin yasani k'ara k'aunarta, sai addu'a take zabgamin akan ALLAH ya saukeni lafiya

. Galadima kad'ai ke amsawa, amma ni saidai a zuciya kawai. daga nan muka d'an shishshiga wasu sassa, 6angaren mama fulani shine k'arshen zuwanmu.

Kunsan dai mutuniyar taku akan mulki, tana kishingid'e kuyanginta nata bauta, mai matsa kafa daban mai

firfita daban, ga masu bata labarai, tufa takeci cikeda k'asaita da izza.

Amintacciyar baiwarta data mana iso tana gaba muna biye, mama Fulani ta d'agama kuyanginta hannu alamar subata waje.

Rige-rigen ficewa suka, yayinda mukuma muka k'arasa

gareta, idonta a kammu ko k'yaftawa batayi, nidai tsarin ALLAH na nema daga sharrinta, ina dalili wannan kallon k'urilla haka?.

Galadima yace, “barka da yammaci”. nima saurin fad'a nayi.

A yatsine ta amsa mana, ta d'ora da fad'in “Saraki k

ayi wuyar gani?”.

Galadima ya murmusa yana kallona, “Ranki ya dad'e kinsan mai amarya ai yafi dubu wahalar gani dama”.

“Humm” kawai tace batareda ta amsaba.

Sai zuwa can tace “nafa manta, ina tayaku murnar samun k'aruwa”.

“mun gode

ranki ya dad'e, amma taki murnar itace tazo a latti, gashi kuma idonkine yafara hango abin cikin kwan tun a india”.

Mama Fulani ta tsatstsare Galadima da idanu, shikuma yay salute nata yana murmushi.

Jitai kamar zata makesa dan haushi.



Ya lura da haushin da taji, dan haka ya kama hannuna muka mik'e tsaye yana fad'in, “bara mukoma inda muka fito ranki ya dad'e, a huta lafiya”.

Bai jira amsartaba mukayi fitowarmu.

Da kallo kawai ta bimu, takasa koda motsawa, tarasa miyyasa

yau Galadima da matarsa suka mata wani mugun kwarjini? batada mai bata amsar tambayar tata...

Yini guda yau Galadima a gida yayishi, baije ko inaba, sai da daddare Nuren yazo sukayi magana, daga nan yace ya nema mana tickets d'in zuwa masarautar

su.



Washe gari muka tashi da shirin tafiya masarautar su papi, mukad'ai muka tafi, babu kuyangi babu dogarai, dagani sai shi dasu Aiyaan, sai Nuren..................



🏼

*_ALLAH ka gafartama mahaifanmu_*

😭🙏🏻

*_typing

📲

_*



💡

*_HASKE WRITERS. ASSO....._*

*_



RAINA KAMA.....!!



_*

_(Kaga gayya)_

*_Bilyn Abdull ce

🤙🏻

_*

~Book 2~

👉🏻

1



5



...................Abin yabani mamaki ganin yanda akazo tarbarmu, y

o saikace wani Sarki, hakan yakuma tabbatarmin da Galadima d'an gatane a wannan masarautar.

A masarautar ma gungun mutane muka iske wai masu tarbarmu, ni dukma sai kunya ta kamani wlhy, musamman da Mom ta rungumeni tana fad'in “ga maman twins d'in

mu ga Maman twins d'inmu”.

Galadima dai murmushi yayi, Nuren kam dariya ya kemin.

Lallai naga tsantsar soyayya a wannan masarauta, sai nan nan ake dani kamar wata sarauniya, duk wani Motsina Inno tace minakeso? hakama mom.

Aiyaan da Aryaan

kam ai suna tare da Galadima, duk inda yasaka k'afa suna biye.

Nikam dai a kwana biyun da mukayi babu abinda zance da wad'annan bayin ALLAH sai godiya, naga karamci naga hallaci sosai, hakama k'annena.

Sosai Galadima yasamu tattaunawa da papi

a tsakaninnan, sunyi maganganu masu muhimmancin gaske. Musamman akan ciwon Abie da cikin jikin Munaya, harma da Abbanta. sosai kuma Galadima yakuma samun haske akan lamuran.

Kwannamu biyu muka dawo cikeda kewarsu, tare da tarin alkairi ga wad'annan mut

ane masu tsayawa a rai.

Mun dawo da kwana 1 yaran gidanmu na ma'auri suka kawomin ziyara.

Aunty khaleesa, aunty Hauwa'u, aunty Ramlah, aunty Raheenat, matansu ya hameed, Fiddausi, Siyama, Zarah, Safara'u, Fauziyya, Haleematu,Munubiya, Ayusher,

Feena. Wayyo dad'i wlhy saika d'auka biki akeyi, rasa inda zansaka kaina nayi saboda dad'i, shi kansa Galadima ya fahimci ina tare da tsantsar farinciki, nima dagewa nayi namusu hidima iya hidima, dan hardani aka shiga kitchen.

Sukam duksun rikice da

mamaki, dama haka gidan sarautar yake, dan saidama Galadima yaje da kansa ya shigo dasu. Su Aiyaan anata murna anga 'yan gida.

Ranar dai anan suka yini zir, dazasu tafi Galadima yay muzu alkairi mai yawa tareda godiya ta musamman. Sunji dad'i sosai k

uma sunyi farinciki, sunata masa godiya nima ina tayasu.

Da zasu tafi jinai tamkar na rik'esu, aiko harda 'yan kwallana, sauk'inama kawai su Aryaan tare dani.

Kowaccensu tatafi da labarin data gumtsawa uwarta a bayan fage, dansu Zarah dai sun

Shiga taitayinsu, sun gane ruwa ba sa'an kwando bane, nanfa hassada da bak'inciki tamkar ta babbake zukatansu, mamansu Yaa hameed hardama Abba ALLAH ya Isa tana sharar kwalla, wai yasan da gidan sarautar amma ya yarda Zarah ta auri d'an sanata, ga aunty kh

aleesa nanma kullum cikin matsala da miji, dan kishiyarta akwai kissa.

*_ALLAH yarabamu da ciwon hassada fans_*

😏

Sati d'aya da zuwansu muka koma India, saboda Company suna Neman Galadima da gaggawa. harda innaro iya bala'i muka taf

i

🤣

.

A jirgi taita kudundune fuska a gyale wai batason ganin tashin jirgi, duk tsare gidan Galadima saida yayi dariya, Aryaan da Aryaan kam sukaita tsokanarta. Yau babu masifarnan dan bata kulasuba, saima Galadima ne ya hanasu. nikam banza na musu

dan tawama ta isheni nikam. Jikina sai ciwo yakeyi, ga cikina na mun ciwo shima kad'an-kad'an.

Khumar da Sauban da Samha sukazo d'aukarmu, muka rungume juna da samha muna farinciki.

Daga nan muka wuce gida, yaukam munashan k'auyancin innaro

, ni harma tabani haushi, komai tagani saita tambaya, Kodai su Aiyaan basa abinda takeyi.

Mun iske jakadiyane kawai sai bayi, Su Momma da innarmu suna asibiti, Mudai sama muka haye ni da shi, 'yan biyu kuwa suna wajen Samha ta kasa ta tsare, innaro

kuma aka barta da jakadiya.

Ko ina tsaf yasha gyara tamkar mai d'akin na nan, Muna shiga kwanciya nayi bisa kujera, naja bargon saman gadon na lullu6e, kallona yayi da mamaki “k lafiyarki kuwa?”.

“zazza6i”. kawai nace masa na k'udundune har k

aina.

Zama kawai yayi ya zubamin idanu cike da tausayi, ganin zaman bazai masaba yatashi ya shiga toilet, saida ya gama dukkan uzirinsa sannan nima ya had'amin ruwan wanka, tadani yayi, na tashi da k'yar tamkar zan masa kuka.

Yace, “tashi

kije kiyi wanka kozakiji dad'i”.

Baki na tura masa gaba.

“idan bazaki iyaba tashi muje na miki”. ‘yay maganar cike da basarwa’.

Harara na zuba masa sannan na mik'e na nufi bayin. shikuma ya ta6e baki yana wani mikilin Murmushi.



Abincima sai nan ya saka aka kawomin, dan nakasa sauka.

Innaro sai catake wai nacika langyare, dan naga yana shagwa6anine shiyyasa nake ta6ara, ai badaga kaina aka fara cikiba.

Galadima dai murmushi kawai yayi danshi lamarin innaro

abin dariya ya d'aukesa, tana buk'atar uzuri.

Bayan nasamu naci abinci daya bani nasha magani, harzan kwanta a sofa yace na koma saman gadon, kamar zanyi magana saina fasa, na tashi kawai na koma.



Yana kammala duk abinda ya dace yafi

ce asibiti domin duba Abie da Abba.

Yaji dad'in yanda yaga canji sosai a jikin nasu su duka, dan raunuka da yawa sun warke a jikin Abba, da bakinshi ma ya amsa masa gaisuwa yana masa godiya, inna da baba k'arami sunata saka masa albarka. maganar da

abie ya fara kuwa rungumesa yayi yana kuka Abie nayi, hakama su Momma, a hankali Abie yace “ina d'iyata Muh'd”.

Murmushi Galadima yayi, yace, “zuwa anjima zaka ganta Abie, yanzu na barta tana barci zazza6i ya rufeta”.

Momma da Aunty Mimi suk

ace “ALLAH dai ya sauketa lafiya to”.

Babu kunya Galadima ya amsa da amin.

Aunty Mimi dake kusan dashi ta doki gefen hannunsa, “kai mara kunya, shine zaka amsa”.

Hannu ya saka ya rufe bakinsa yana fad'in “ni jikan Abdul'fatah da Abubakar

”.

Dak'uwa Momma tamasa tana kai masa duka, ya matsa da sauri yana dariya.

Abie ma murmushi yakeyi, lallai yau yakuma ganin canji tare da d'ansa sanyin idaniyarsa, sukam yaushe rabon da suga irin wannan nutsuwar tare dashi haka, lallai dolene s

u godema ALLAH da shigowar Munaya cikin rayuwarsa, basu da wani abinda zasu iya biyanta har abadan, saidai suyita mata fatan alkairi da k'yautata rayuwarta.

Saida na tashi sannan muka tafi asibitin muma, wajen su momma muka fara zuwa, Momma da aunty

Mimi sukazo suka rungumeni tamkar zasu had'iyeni dan dad'i, nikam duk kunyarsu ta gallabeni, sai 6oye fuska nakeyi, koda zan gaida Abie ban yarda na kalleshiba.

Sauban da Samha sai dariya sukemin.

Duk bak'in halin innaro saida tayi kuka ganin

halinda Abie yake ciki, taita kwarara masa addu'a kuwa.

Su momma sunji dad'i, kuma sunata girmamata.

Samha sai dama-dama takeyi dasu Aiyaan, motsi kad'an tace, “ALLAH yasa Aunty gimbiya muma ta Haifa mana irinku”. Su Momma sunata amsa mata da

amin. Nidai kaina na k'asa saboda kunya, ina lura da Galadima kuwa duk sanda tafad'a saiya murmusa kuma bakinsa ya motsa alamar yana amsawa da amin.

Sosai naji dad'in ganin jikin Abbanmu shima, dan har magana mukayi, jikinsa yayi k'yau sosai, kar

ayunne ma kawai suka rage nakula, amma k'ananun ciwukan duksun warke, to wajene dayake samun kulawa ta musamman. Munaya harda rungume inna, itako ta tureta tana hararta, su Aiyaan kam duk sun d'are bisa cinyarta suna d'okin ganinta da kewarta. Itama tayi k

ewarsu over, tsakanin uwa da d'a kenan (iyaye mata ga naku fa

🥰🥰🥰



👍🏻

).



Haka muka dawo gida ina farinciki, koba komai nasamu nutsuwa mai yawa a yau d'innan, aiko ban yarda mun kwantaba saida nayi nafilfili domin mik'a godiya ta ga ubangij

in sammai sannan na kwanta.

Galadima kuwa muna shigowa d'akin sirrinsa ya shiga yanata aiki.

___________________________

Hankalin Minister ya kai k'ololuwar tashi shida families nasa akan 6atan 'yarsa, farhat, duk wata hanya day

a kamata subi sunbita amma babu koda labarin Wanda ya ganta, tun lamarin nabasu mamaki harya koma basu tsoro, ga wani text massage da akama minister d'in d'in kwana 10 daya wuce.

_Idan kana buk'atar 'yarka kana iya mik'a wuya._

Wannan ma

ssage ya tsaya masa a rai, har police sun kar6a amma sun gaza gane komai gameda massage d'in ko wannada ya turo shi.

Mahaifiyar Farhat harda kwanciya asibiti, dan ita kad'aice mace a gidan, dan haka suke masifar son yarinyar da mata gata, dudu shekar

unta 16 ne kawai, tana wata private boarding school ne a abuja. a binciken da Galadima yakeyine ya gano hakan, kuma yayta bibiyar yarinyar har saida yasamu nasarar saka Nuren ya kwamuso masa ita.

___________________________

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login