Showing 54001 words to 57000 words out of 407268 words

Chapter 19 - Raina Kama COMPLETE

bayanin kawo kud'in nawa, amma cikin halin ko in kula tace su basu kawai, idan sun barni agidan kuwa najawo musu abin kunyar dayafi nabaya, harma tashafi sauran kannena suk'i auruwa tamkar ni.

Wann

an furuci ya Sosa zuciyar abbanmu, amma saiya danne saboda girman mahaifiya.

An sallamo gwaggo Safiyya da kwana biyu jikina ya birkice nima, dole aka kwasheni aka kai asibiti.....



*********

A 6angaren sarki kuwa bayan tafiyar Galad

ima da kansa yazo masarautar gagara badau, an masa tarba ta girmamawa domin shid'in babban abokine ga kakansu Galadima wato (marigayi sarki Abubakar na lll).

Mama Fulani kanta in kunga yanda take girmama sarki (Abdul'fatah idris) saikusha mamaki Ku d

'auka ba itace mai ji da kanta d'innanba da tsantsar nuna sarauta(gaba da gabanta yo

🥴

).

Sarki bai 6ata lokaciba ya sanar musu abinda yazo dashi, ganin tsantsar farinciki nayi ga mafi yawan jama'ar gidan, dan hukuncin sarki Abdul'fatah yamusu da

i-dai, koba komai an k'ask'antar da Galadima d'in, Wanda yadace ace an sama masa d'iyar wani mashahurin sarki ya aura, kodan sarautar da ake da yak'inin shine yakama ta ya gada.

Murmushi papi yayi, saboda ganin farinciki zancensa a fuskokin wasu

nsu, yasan tabbas dawata manufa suke wannan farinciki, amma hakan bai damesa ba, domin shi da k'yak'yk'yawar niyya yayi. maganar sarauta kuwa sune suke ganin bazai iyaba saida wata d'iyar babban sarki, amma shi yanada yak'inin ko d'iyar shugaban talakawan

duniya koda baiwace agidan Galadima ya aura sarauta ta ALLAH Ce.

Daga baya ya tsara musu yanda yakeso Neman auren ya kasance, bawai zasuje musu da rigar mulki baneba, yanason suje amatsayin talakawa domin ganin tarbar dazasu samu daga iyayen yariny

ar, daganan zai gwada yak'inin tarbiyar gidan da mutuncin iyayenta.

A masarautar sarki ya kwana, washe gari sukayi shigar talakawa shida sarki jalaludden k'anin mahaifin Galadima, sai wazirin papi dana sarki, saikuma k'annen mahaifin Galadima b

iyu sannan aka sami tsohuwar mota suka tafi aciki bisa jagorancin wani dogari da sarki yasa yamasa binciken gidansu munaya.

Abinda basuyi zatoba shi suka samu, domin tarba ta mutunci da girmamawa suka samu dagasu Abba, duk da suna kallonsu talakaw

a fitik harma da yak'inin sun fisu komai.

Hakan ya burge sarki Absul'fatah (papi) shi kansa sarki jalaludden lamarin ya masa dad'i. Sun bada kud'in gaisuwar farko data biyu naira subu 30 kacal.

Sai bayan tafiyarsu sannan su Abba sukaita mamakin

kansu anya mutanen bada wani siddabaru sukazo musuba? Yazama ayi basu sansuba amma suzo su kar6i auren 'yarsu? sukuma su basu babu musu kamar sun gaji da ita. (Niko nace kwarjinin sarauta suka muku abba

😜😂

).

Can kuma dasu sarki suka tafi sunata ya

bawa suma, sarki Absul'fatah dad'i dukya gama cikasa, lallai Galadima yasamu tsatson daya dad'e yana masa fata da addu'ar samu.

Momma koda papi yakira yamata bayanin bataji komaiba, saima addu'a data masa da kuma nuna farin cikinta akan lamarin

, koba komai zataga auren Galadiman ta, amma saida tayi hawaye data tuna za ayi auren Galadima babu mahaifinsa, kamar yanda akayi na Haneefa (Aunty Mimi).

Data sanarma Abie saiya fad'ad'a murmuahinsa, yayinda hawaye ke zirara ta gefen idanunsa, ALL

AH sarki iko da falala, tun yaronsa na shekara 5 a duniya yake a wannan halin, gashi har zaiyi aure, yagodema ALLAH da wannan jarabawa shikam.



A satin papi yaje India ma da kansa, yaduba jikin Abie dakuma maganar auren Galadima dayayi mu

su, nanma saida Abie yay hawaye, amma sarki Absul'fatah yayta masa nasihar yawan hak'uri da kar6ar k'addara, ya nuna masa sunada yak'inin zaici ribar can.

Abie yana son surukinsa kuma aminin mahaifinsa sosai, dan duk lokacin dazaizo dubashi da irin

salon nasihar dazai masa wadda zai k'ara tasirantar da imani a zuciyarsa.

Galadima kuwa sai wani basarwa yakeyi irin shifa abin bai d'ad'ashi da k'asaba, kuma bayason abin, aurenma dole za ai masa, haka yaytaima Abie korafi yana shagwa6a.

Murm

ushi Abie yay tayi yana lallaahinsa da idanun.

Cikin tsokana sauban dake d'ayan gefen Abie shima yace “yaa Sam to kawai ni abani kana, kaga na huta da zuwa tad'i k'ofar gidan kowa”.

Wata uwar harara Galadima ya maka masa, wadda tasaka Momma da

auty Mimi da samha da jakadiya dariya, shi kansa Abie murmushine ya fad'ad'a afuskarsa.............



🏼

Wannan shine yafaru 6angaren Galadima munaya bata saniba.

Guys kuje zuwa kawai, k'ila zuwa dare kujini da bonus



🏻

‍♀⛹

🏻

‍♀

ALLAH yabama mun

aya lafiya.

Barka da juma'a.

😄



🏻

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*

😭👏🏻

*_Typing

📲

_*

*_HASKE WRITERS ASSO...

💡

_*

_(Home of expert and perfect writer's)_

*_



RAINA KAMA......!!



_*

_{Kaga gay

ya}_

*_Bilyn Abdull ce

🤙🏻

_*

👉🏻

1



7



.........Cikeda girmamawa yace, “Ranka ya dad'e barka da dare?”.

“barkan ka dai Muhammad. dama kashigo k'asar kenan?”.

Gabansa yad'an fad'i, danshifa yama manta mai

martaba baisan yazo k'asarba, dakiyar dole ya aro yace, “wlhy kuwa nashigo d'azun yin wani aiki, amma gobema idan ALLAH ya kaimu zan koma”.

“tofa, gobe gobe? kuma gashi inason ganinka a goben”.

d'an jimm yayi, irin tamkar baisan komaiba, ci

keda shakku yace, “ranka ya dad'e lafiya dai ko?”.

“lafiya k'alau, wata muhimmiyar magana nakeson muyine”.

“to shikenan, zanshigo insha ALLAH ”.

“to madalla saina ganka”.

Dafe kai Galadima yayi yana mamakin kansa, anya kuwa

baima kansa d'aurin gorobo? koda yake idanfa yayi hak'uri shekara 1 ne ko 2 kacal, inma komai yafito kafin cikar shekarar zai sawwak'a matane, yad'an murmusa sannan yakoma ya kwanta abinsa cikeda tunani barkatai.

★★★★★

Rashin reply d'in G

aladima ya dameni, haka dai naita danne zuciyata dankar innarmu da Munubiya su fahimta, nacigaba da harkokina tamkar banida wata damuwa a zuciya, saima sallar dare damuka fara dagewa da tashi nida Munubiya, gakuma azumin damuka tashi dashi yau litinin.



Duk da innarmu ta fahimci inada damuwa batacemin uffanba, saidai tausayina na damun zuciyarta, tana dannewane kawai.

Munubiya kam tsaf tagama fahimta ta, amma itama saita nuna bata fahimci komaiba, taje tasamu innarmu da maganar son a d'aga bikint

a again.

“munubiya ba wannan yakamata muyiba, addu'a yakamata muyima 'Yar uwarki, idan da rabo saikiga ALLAH ya kawo mata miji a cikin watanni 2nan dasuka rage kinji. nima nasan tana acikin damuwa, amma tana dannewa a zuciyarta saboda farin cikinmu.

addu'ar dazamu mata itace tsantsar k'aunarta a garemu”.

“shikenan innarmu, insha ALLAH zamu kuma dagewa da fad'ama ALLAH, itama ALLAH ya kawo mata ta hanyar da batayi zatoba, ya sakanka mata fiyeda sadaukarwar datayi, innarmu nasan sadaukarwar

da 'Yar uwata tayine yasakata a wannan halin, ta sadaukar da farincikinta saboda ni, mizanyi na biyata nikam”.

Murmushi innarmu tayi, tace, “addu'a”.

★★★★★

Washe gari yatashi ya shirin tafiya masarautar su Momma, Harun yakira yace

ya nema masa ticket.

Cikeda mamaki Harun yace, “yaushe kashigo k'asar Galadima?”.

K'aramin tsaki yaja, dan shifa yama manta Harun baisan da zuwansa ba, Link d'in hannun rigar milk d'in shaddarsa yake k'okarin sakawa, cikeda dakiya yace, “jiya n

azo da daddare, kuma inagama yau zan koma”.

“tofa, amma baka cikin masarauta?”.

“no a hotel Na sauka”.

“ok barato a nema ticket d'in, sai muzo mu d'aukeka”.

“karka damu harun, banason kowa yasan nazoma, muhad'u dakai kawai a air

port ”.

Koda suka yanke wayar sai yaja tsaki, gaba d'aya yakoma mak'aryaci, abinda yatsana arayuwarsa fiye da komai kenan (k'arya) amma sai gashi shi yana zundumata, “Astagafurullh” yashiga maimaitawa a zuciyarsa.

Tsaf yafito cikin shadda

milk color (nakula yana k'aunar milk) d'inkin rigar 3quarter, harda su hula, yayi k'yau sosai, yafito ainahin sa na cikakken bahaushe kuma basarake, ya fesa turaraensa Na kullum, komai nasa dayazo dashi ya had'a a waje d'aya. sannan yakashe kayan wutar be

droom d'in.

Afalo ya iske Muftahu zaune yana jiransa, yad'anyi mamaki amma sai bai nunaba, yabashi hannu suka gaisa.

Muftahu yace, “zaka dawo ta nan kenan?”..

Kai Galadima yad'aga alamar a'a, sannan yanufi kayan wutar falon yafara ka

shewa. saida yagama komai sannan ya kalli Muftahu alamar suje.

Murmushi kawai Muftahu yayi, danya lura yau miskilawanne aka.

Sun isa airport, lokacin shima harun harya je, mamakine ya kama harun Dan ganin Galadima tare da Muftahu, shima y

anzu yana mamakin yanda Muftahu ke kuma kusanta kanshi da Galadima, baice komaiba yabashi hannu suka gaisa kamar yanda yabama Galadima.

Harun yanason suyi magana da Galadima amma ga Muftahu a wajen, sai kawai yashare akan sayi a waya kawai.



Basu wani dad'e a airport d'inba jirgin su Galadima yatashi.

★★★★

Yau hankalin kowa a tashe yake agidanmu saboda gwaggo Safiyya da aka kawo batada lafiya, dayake ba'anan kusa damu take aureba, tanacan wani gari daban, tun lokacin bikinsu ya

a Hameed tamasu Abba complain akan batajin dad'i, amma kunsan maza darashin d'aukar Abu serious, sai basu maida hankalinsuba.

Ita kuma kunya tahanata kuma musu maganar, har aka gama biki ta tafi, ashe baiwar ALLAH ciwo nata cin jikinta babu Wanda ya

sani, tun tanayi a tsitsaye har takai ga kwanciya, yaranta sun kaita asibiti amma basuga wani canjiba, hakanne yasa suka maidota gida, Dan aganinsu dai su Abba sunfi mahaifinsu k'arfi.

Aiko suna isowa babu 6ata lokaci aka wuce da ita asibiti.



Dan danan aka fara bata taimakon gaggawa.

Muda innarmu ne kawai da innaro a asibitin, amma matan gidanmu babu wace tabimu, kusan mudasu baba k'arami muketa shiga da fita a asibitin dan ganin komai ya dai-daita.

Kusan yamma saigasu Sa

fara'u lokacin ma gwaggo Safiyya tana barci, yaranta duksunyi jigum-jigum da innaro saboda tashin hankalin dasuke ciki.

Har dare ba'abar kowa yashiga wajen taba, sai su Dady kawai, ganin dare yayi akace mu muje gida kawai.

Haka muka tafi akab

ar innaro da aunty habiba d'iyar gwaggo safiyyar ta uku, itama tayi aure amma tafito, yanzu zawarci takeyi. saikuma yaa Anas da aka barmusu saboda ko wani Abu zai taso.



★★★

Tunda yafito daga jirgi ya hango tawagar masarautar kakannin

nasa, yasan tarbarsa sukazoyi, inhar zaishigo haka sukeyo gayyar tarbarsa, saikace wani bak'o daban, gefe yayi da fuskarsa dankarsu gansa, sashen motocin da akan d'auka drop ya nufa, duk manyan motocine da aka tanada dama domin irinsu, d'aya yabud'e da Ka

nsa yashige da sauri, alamar yayma driver d'in suje.

Tacikin glass yake kallonsu yana murmushi, yanda suketa d'aga kai nason hangosa, suna fita daga airport d'in ya kwantar da kansa ajikin seat ya lumshe idanunsa yana tunanin wane hukunci mai ma

rtaba zai yanke akan maganar, shin ya amincene? Kokuwa?.

Driver yace, “oga ina muka nufa?”.

Bai bud'e idonsaba kuma bai d'agoba, yace “gidan sarki”.

Ta madubi driver n ya kallesa, “yalla6ai ko kaine ma dai akazo tarba daga masarauta?”

.

Murmushi kawai yayi batareda yace komaiba.

Jin bai amsaba sai driver yakama bakinsa ya tauke shima.

Ganin shine yasa dogarai suka bari aka shigar dashi har cikin masarauta, tunda yafito bayi da hadimai keta zubewa suna kwasar ga

isuwa, hannu kawai yake d'aga musu, fuskarsa ad'an sake take, bai d'aureba baikumayi murmushi ko dariya ba kai tsaye.

Tuni an kar6i kayansa an nufi sashin inno dasu, shikuma yanufi fada, Dan yasan yanzu Sarki suna fadanci.

Cike fadar take

da 'yan majalissar Sarki anata fadanci, bayan an masa iso yashiga da sallama, nanfa dogarai suka fara zuba masa kirari.

Hannu kawai ya d'aga musu ya rissina yana mik'a gaisuwa ga Sarki.

Sarki da fuskarsa tacika da fara'ar ganin jikan nasa ya ams

a cikin lumshe idanu.

Nan dogarai suka d'au da fad'in “sarki ya amsa maka sarkin gagara badau na gobe, an gaida magajin sarki, galadiman gagara badau, ALLAH yabaka zamani irinna sarki gagara badau.

Galadima Yakuma rissinawa ya mik'a gaisuwa ga

'yan majissar sarki, suma cikeda fara'a suka amsa, kowa yasan irin tsantsar k'aunar da sarki kema jikan nasa a masarautar.

Atake anan sarki ya sallami kowa, fadanci yatashi saikuma gobe idan ALLAH ya kaimu, yau yanada ganawa ta musamman da jikan

sa.

Haka kowa yatashi yana musu addu'ar kasancewa cikin aminci.

Tareda Galadima sarki yashiga cikin gidansa, hannunsa Na rik'e da Na Galadima, ba sabon Abu bane hakan a masarautar, duk Wanda yakwana yatashi acikinta yasan matsayin Galadima az

ukatan masu masarautar.

Akatafaren falon sarki suka yada zango, babu dad'ewa da shigowarsu saiga jakadiya da kuyangi uku, kowanne d'aukeda babban tire, bayan sun dire komai suka zube suna kwasar gaisuwa wa sarki, sannan suka gaida Galadima.

J

akadiya ma ta rissina ta gaida Galadima damasa barka da zuwa masarautarsu.

Bayan fitarsu Galadima yakuma risainawa a girmame ya gaida sarki kakansa.

Cike da murmushi sarki ya amsa yana kamo hannunsa, “Muhammad Sameer! kana lafiya”.

“A

lhmdllh ranka ya dad'e”.

“Masha ALLAH, ya kabaromin Zeenah ta da jikin babanka da 'yan uwanka kuma su Haneefa?”.

“Momma lafiyarta lau, hakama jikin Abie Alhmdllh, suma su aunty mimin haka”.

“to Alhmdllhi, ALLAH yacigaba da jagorantar

lamuranku ya albarkaci rayuwarku ta gobe da jibin jibima”.

Murmushi Galadima yayi yana amsawa da amin.

Sarki da Galadima tare sukaci abinci, (tun yana k'arami dama idan yazo gidan hakance ke faruwa tsakaninsu) Sunci sun k'oshi sukayi

hamdala ga ALLAH.



babu wani 6ata lokaci sarki yashiga masa bayanin kiran nasa akan maganar da Fateema (mom) tazo masa da itane jiya, shima ya zauna yayi nazari yagane hakan shine dai-dai, Galadima ya auri Munaya.

tur6une fuska Galadima

yayi tamkar baisan komaiba, yace “ranka yadad'e ka gafarceni, ammafa ni bata minba ai”.

Sarki yay murmushinsu Na manyan k'asaitattun masu ji da mulki, “basai tayi makaba Muhammad, domin sanda Na aurama babanka Zeenah itama bai mataba, amma saboda b

iyayya dakuma tausayin d'iyar 'Yar uwarta ta amince tamin biyayya, to kaima hakan nakeso gareka, ka amsamin da to kawai saimu zauna lafiya, kasan magana biyu ba halina baceba ko”.

Jinjina kai Galadima yayi yana kuma tankwashe k'afarsa, cikeda girma

mawa yace “ALLAH ya huci zuciyarka ranka ya dad'e, Na amince da za6inka, ALLAH yabani ikon rik'ewa”.

Cike da tsantsar farinciki Mai martaba ya rik'o hannun Galadima, “Muhammad ALLAH shiyi maka albarka, ya tsareka dadukkan sharri, ALLAH yabama maha

ifinka lafiya kaji”.

“amin ranka ya dad'e, ngd sosai ”.

Daga nan hira suka cigaba

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login