Showing 237001 words to 240000 words out of 407268 words
Da yake su Saleem sun sanar dasu Muftahu su
Aunty Salamah d'in sai Nuren ya kuma yima Galadima bayani.
Aunty Salamah tace, “ka gafarcemu ranka ya dad'e, nasan zakayi mamkin mun shigo abinda ba'a gayyacemu ba, insha ALLAH zakaji dalilin shigowar tamu nan gaba. game da shiga gidan nan mungama ko
mai, maza 5 ne da mata biyu, wad'anda shigarsu ta tabbatar min suna cikin hadiman masarauta su matan kenan”.
Kai kawai Galadima ya iya jinjina masa. daga nan yaymata nuni da zasu iya farawa.
Da taimakon su Ameer suka shiga gidan.
★★
*
★★★
*
★★★
*
★★
Fitar Galadima da kusan awanni hud'u, around 2am Munaya ta farka a firgice, Inno dake zaune akan Sofa, mom da Aunty Mimi kuma a gefen gadon suka kalleta, tashi Mom tayi da sauri ta nufeta tana rik'eta, itama Aunty Mimi ta taso.
Kuka munaya ta sanya tana fad'in “Mom sun mutu ko? Nasan dama kashesu zasuyi, Aunty Mimi dan ALLAH miye laifinsu su? kwanansu 7 fa kacal yau a duniya, mi suka sani game da abinda ake tuhumarsu? An durk'usar musu da kakansu, an hana mahaifinsu nutsuwar zu
ciya data rayuwa, shin wannan tabon bai Isa a barsu su taso da shiba a rayuwarsu? Har sai an had'a da salwantar dasu kenan?”. ta fashe da kuka maiban tausayi.
Tasowa inno tayi ta zauna a bakin gadon itama, kamo hannun Munaya tayi ta kwantar da ita a j
ikinta tana shafa kanta, yayinda itama kwallar kebin nata kumatun.
Aunty Mimi da mom ma duk hawayen sukeyi, kalaman Munaya sun ta6a zukatansu.
Lallashinta da magana mai dad'i suka shiga fad'a mata, sai sauke ajiyar zuciya takeyi, ga jikinta yayi
ringim da zazza6i saboda nononta sun mata hak'e-hak'e, rabonsu da shansa tunda rana, tausayinsu ya kuma kamata, tasan yunwa da k'ishi ma kawai sun Isa su k'arar da numfashinsu, hawaye masu d'umi suka kuma gangaro mata a kumatu suna sauka jikin inno dake sh
afa kanta.
Shayi Aunty Mimi ta had'o mata, amma fir tace ta k'oshi, da k'yar inno ta samu ta lalla6ata tasha Quarter d'in kofin.
Mom tace, “wannan nono kid'an matsesu kozasu rage miki nauyi, dan shine yakawo wannan zazza6in”.
Bata musaba
aka kawo k'aramin bowl ta matse aciki, Aunty Mimi ta zubar a bayi”..
Tanason tambayar ina Galadima tanajin kunya, sukuma babu Wanda ya sanar mata komai, kodan gudun k'ara tada hankalinta.
Magani suka bata tasha takoma ta kwanta, yayind
a sukuma suka mik'e duk suka d'aura Alwala suna mik'ama Ubangiji kukansu, danshi masanin sirrin 6oyene, yana kallon komai, kuma shine zai kawo iyakar komai d'in.
★★★★★★★
Duk wannan abun dake faruwa su Momma babu Wanda ya sanar musu, saidai s
ukaji a jikinsu tamkar akwai matsala, sunta kiran numbers amma daga wadda zasu samu a kashe sai wadda network zai hanata shiga.
Sai suka d'aura ko shagalin sunan ne yakawo hakan.
*******************
Tunda Munubiya suka koma gidan kuka tak
eyi, ko kad'an tak'i sauraren yaran da keta tsula kuka suma, balle tabasu nono.
Ba itaba hatta su Ayusher dasu feena kukan sukeyi, hakama Samha harda shid'ewa, dan itama su tabi bata koma masarauta ba, Yaa marwan da mama Rabi'a ne kawai ke k'ok'arin d
anne nasu suna lallashinsu.
Yayinda dare yay nisa duk sai suka d'aura alwala suka zo suna mik'ama Ubangijin talikai kukansu da k'ok'on barar bama wad'annan k'anan alhaki kariya da fatan ku6ta.
A 6angaren gidan su Munaya kam duk
hassadarsu yau dai sun tausayama gudan jininsu da yaranta, sundawo gidane kowa yana sharar kwalla da addu'ar ku6tar yaran.
Ita innarsu Munaya ma ai ba'a magana, ALLAH kad'aine yasan halin datake ciki, ta shige d'aki ta rufe kanta tana jera nafilfili,
dan wannance kawai gudunmawar dazata iya bayarwa a garesu akan wannan lamari mai sark'ak'iya da yawa.
Abban su munaya ma yau harda hawayensa, dukda bashi da tabbas akan hasashensa yasan komai zasu iya, saboda SD yanada kusanci da wann
an masarautar sosai, duk abinda ke hannunsa da bayanan daya ajiye ya shiga tattarasu waje d'aya...............
✍
🏻
😿
Duk nisan jifa dai k'asa zai fad'o, kwana 99 na 6arawo, 1 kuma tak namai kaya.
👎🏻
Fans insha ALLAH dai abuwa sun far
a warwarar zare, sai mubi su Galadima muga yanda zasu dawo mana da triplets d'inmu gida
😭
, yau Munaya tabani tausayi daga ita har Galadima, dan shima dai dannewa kawai yake saboda jarumta, ALLAH ya rabamu da sharrin mak'iyi komai k'an k'antarsa, Harun da s
auran munafukai MAZA BISA KANKU
🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻🏇🏻
.
Barkanmu da dawowa my sweet fans
🤕😡
.
Yau bana cikin yanayin dariya
😡
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*
😭👏🏻
*_typing
📲
_*
💡
*_HASKE WRITERS ASSO....._*
*_
♦
RAINA KAMA.....!!
♦
_*
_(Kaga gayya)_
*_Bilyn Abdull ce
🤙🏻
_*
~Book 2~
👉🏻
2
⃣
7
⃣
................Tunda suka d'akko yaran suketa kuka, musamman Abdurraheem dahar shid'ewa yakeyi, ALLAH dai yabasu sa'a ne sa
ida suka fito suka fara kukan, neman haukatasu ma sukaso yi tun amotar, jisukai tamkar su rufesu da duka, saidai babu damar hakan, dan basuga abin duka jikin wad'annan kwad'unan yaranba.
Da farko sunga kamar ana binsu, sai daga bisani ne sukaga ba h
aka baneba, har dai suka iso gidan y'an uku basu barsu sun shak'i iska ba.
Suna shiga suka danna musu wasu allurai, cikin mintuna k'alilan jikinsu dukya saki sukayi luf.
ganin lokaci yaja har kusan 10pm babu alamar wani motsi hankal
insu ya kwanta, dan sunsan dai tabbas sun tsira, wayar wadda ta sakasu aikin suka kira, amma tak'i yin picking.
Cikin matan d'aya tace, “kusan dai bazata d'aga ba, saboda nasan masarauta a haukace take yanzu, saidai mubari zuwa safiya”.
Tsaki d'aya yaja, “kai nifa gaskiya a tsorace nake, gara ta d'auka asan mafita, bana buk'atar gawar yarannan takwana a hannunmu, kunsanfa babansu mayene wlhy, tsaf zai bibiyemu”.
“kai dalla ai yanzu bashida wannan damar, caza'ayi a fad'ama police,
sukuma aikinsu zai farane zuwa safiya, kafin sannan munma gama binne gawar yaran mun kama gabanmu”.....
“eh kumafa hakane”.
Suna tsaka da wannan hirarne su Galadima suke shigowa, gidan k'aton gaskene dan haka suka kasa fahimtar INA zasu dos
a, Galadima Yakuma danne abin kunnensa da d'anyatsa d'aya cikin murya k'asa-k'asa yake fad'in “Sauban kufara muje”.
“yauwa Yaya zaku shiga hannunku Na haggu, duk sunajin maganar dan haka sukabi hannun haggu, yayinda su Ameer ke binsu a baya suma.
Galadima dake gaba ya bud'e k'ofar a hankali duk suka shiga, daga can Saleem yace, “duk Ku rarrabu sir, dan abin ya nuna yaran suna ainahin tsakkiyar gidanne”.
Batare da sunyi magana ba duk suka rarrabu.
'Daya acikin 6arayin yace, “kai nif
a kamar motsi nakeji gaskiya”.
“to sannu mai kunnen maciji”. cewar d'aya aciki.
Cikin matan d'aya tayi dariya tana fad'in “nakula kaidai bibo matsoracine halan?”.
Hannu ya d'aga zai kwad'eta, a harzuk'e yana fad'in “k wlhy kacaccala
ki zanyi, bar ganin kinfito daga masarauta, kubadan ma an had'amu aiki dakuba kun Isa saninmu ne? jimin y'ar iskar mara kunya”.
Hak'uri y'an uwansa suka bashi, ya mik'e yana jan tsaki ya fito danya duba.
Galadima dake la6e cikin labule ya
y saurin fitowa, abinka da dogon mutum dan danan yasamu damar shak'osa ya shaka masa abin hannunsa, tun yana k'ok'arin kare kansa har jikinsa ya saki ya kwantar dashi a k'asa.
Jinjina Muftahu dake kusa dashi yamasa, sannan suka cigaba da shiga.
'Dayar baiwar tana kitchen tare da wani suna iskancinsu Nuren yasamu damar sad'ad'awa, (kunsan dai shahararren kidnapper ne
🤭😂
) yauma tsiyar ya aikata wajen jefa ma namijin handkerchief a fuska, macen tai yunk'urin zuba ihu yasa k'afa ya tad'ota ta f
ad'in, sannan ya danne bakinta da ya shak'a mata itama.
K'arar fad'uwarta taso fargar da sauran, dan haka duk suka mik'e suna fara lek'e-lek'e, aikam Muftahu yasamu ya tad'e d'aya ya fad'i, Ameer dake bayansa shima ya shak'a masa, harda mangareshi y
ana fad'in “kwallon shege taka ta k'are, inakai ina satar sarakunanmu insha ALLAH”.
dariya taso kufcema Muftahu amma ya danne bakinsa da hannu yana girgiza kai saboda tsiyar Ameer.
Fad'uwar wani da suka juyo ya sakasu kuma saurin waigawa waj
en, Galadima ne ya sakeshi ya fad'i, “shegen k'arfin jinine dashi dak'yar abin yay masa tasiri”. Galadima ya fad'a yana halbinsa da k'afa.
Gaban d'ayar baiwar dake la6e jikin labule ya fad'in, dan tabbas wannan muryar Galadima ce, kowa yasan bai
iya R ba, zuface tashiga keto mata jikinta na 6ari, ta to she bakinta saboda kuka daya kufce mata, saigata tana tsilala fitsari saboda ganin Galadima yanufo ta wajen, shikenan itakuma tata tak'e, wannan zakin gagara badau d'in binneta kawai zaiyi da ranta.
Waige-waige Galadima ya fara saboda jin numfashin mutum dayakeyi kad'an-kad'an ta wajen, har yayi gaba ya dawo baya yana yaye labulen wajen. shi da farkoma ya zata aljanace saboda yanda ta zazzaro masa ido. fincikota yayi ya Watso tsakar d'akin, ma
maki ya kamashi ganinta da kayan manyan kuyangin gidansu.
“tashi tsaye”. ya fad'a cikin matuk'ar d'aure fuska, kad'an yarage kashi ya kufcemata.
“ina suke!!!”.
Yafad'a cikin matuk'ar tsawa daya firgita hatta su Sauban dake saurarensu a way
a.
Wannan tsawar tasa ce ta saka d'ayan fitowa a tsorace da gun a hannu, Aunty Salamah dake bayansa bai saniba ta hankad'ashi yay gaba zai fad'in, Nuren ya ida tad'eshi da k'afa.
Gun d'in data fad'i ta silalo gaban Galadima ya taketa da k'afa y
ana huci da taunar lips. Handkerchief d'in hannunsa yasaka ya d'auki bindigar, ya saita namijin da ita.
Mazari jikinsa ya fara yana d'aga hannu sama, “dan ALLAH ranka ya dad'e karka kasheni, wlhy bansan komaiba, oganmu ne yasan komai da wannan baiwa
r”.
Kunamar bindigar Galadima ya d'ana, nanfa su Muftahu duk suka rud'e, Nuren yace, “Brother please karkayi harbi, nasan zasu fad'a mana, dan ALLAH kayi hak'uri”.
Gaba d'aya jijiyoyin kan Galadima sun mimmik'e, sai fidda huci yakeyi a waha
lce.
Muftahu ma yashiga rok'onsa, Su Saleem dake sauraren komai dagacan duk suka rud'e, Sauban yace “yaa Sam ALLAH ya huci zuciyarka, amma idan ka aikata haka a wajenwa Zamu samu hasken sauran abubuwan?, dan ALLAH kayi hak'uri badan mun isa mu saka
ka ba, saidan halin da mahaifinmu ya tsinci Kansa tsawon shekaru, gakuma dama tazo mana ta Sanin sirrin 6oye, muyi amfani da ita ta sauk'ak'ak'iyar hanya....”
Sakin gun d'in Galadima yayi ak'asa yana dafe k'irji, wani mugun bugawa zuciyarsa keyi, d
a baya-baya yanemi zubewa a k'asa, cikin hanzari Nuren da Muftahu suka taresa, da taimakonsu ya zauna akan kujera. Yana nuna baiwar da d'ayan hannusa.
Aunty Salamah data fahimci mi yake nufi tace, “ina yaranne?”.
Jikin baiwar Na 6ari ta nun
a k'ofar wani d'aki, shiga Aunty salamah tayi itada Ameer suka d'akkosu.
Saidai duk a firgice suke, dan yaran babu alamun rai tare dasu, zufa ta shiga ketoma Aunty Salamah, haka ta fito rungume da Abdurraheem da Amaturrahman, shikuma Ameer ya d'akko
Abdurrahman yana fad'in “Aunty kamarfa yarannan sun mutu”.
Wannan kalma caraf a kunnen Galadima.
Wata muguwar zabura yayi yamik'e tsaye, sai ya kuma dafe k'irjinsa da sauri hajijiya tafara katantanwa dashi, basu fargaba sai jinsa sukay
i kawai a k'asa.
Gaba d'aya suka kuma rikicewa, sukayi kansa.
Muftahu yace, “bamuda isashen lokaci, asuba ma ta gabato, dolene mubar gidannan dan ko yaushe zamu iya gamo da abinda bamu shirya masaba”.
Duk sunyi na'am da wannan maganar t
ashi, nan fa suka fara kwasar wad'anda suka sumar suna kaiwa mota, sannan suka tasa k'eyar d'ayar baiwar da wancan, suma.
Yayinda Nuren yad'an bincika gidan, ganin babu wani abunda zasu k'aru dashi yazo suka kama Galadima daya Suma suka fita dashi.
Hankalin Sauban ya tashi matuk'ar tuk'ewa, ya fito yana nufarsu da ta6a jikin d'an uwansa, “Yaa Nuren miya farune? miya faru da Yaa Sam?”.
“Sauban bamu hanya, ba lokacin wannan baneba yanzu”.
Sole Sauban ya matsa baya hawaye Na kwarara
a idonsa, suka shinfid'ar da Galadima a bayan mota, sai lokacin Sauban yaga yaran a hannun Aunty salamah da Ameer, da hanzari suma ya nufesu, Aunty salamah ta bashi Abdurraheem, jujjuya yaron yayi yaji kamar baya numfashi, “innalillahi....” yashiga maimai
tawa zufa Na keto masa, dolene Yaa Sam ya suma, hawaye yafarayi yana rungume yaron a jikinsa, Tausayin dukkan ahalinsa da suka kwallafa rai ga yaran ya kamashi, musamman ma iyayensu, ya ALLAH nasan bazaka jarabcemu da abinda bazamu iyaba, ALLAH kabamu juri
ya”.
Muftahu yace, “su shiga mota, duk shiga sukayi, Nuren dasu Ameer suka wuce da wad'ancan sauran wani waje daban, Muftahu kuma ya kira police d'in da suka shirya komai dasu, a hanya suka had'u, sai sukai joining d'insu tamkar tare sukayi aikin, suk
a kira manyansu suna sanar musu gashifa sun kama wani matashi da baiwar masarauta da yaran....
Wannan labari yama su d.p.o dad'i ya kira IG shima ya sanar masa, yaji dad'i shima, koba komai mai martaba zai yaba k'ok'arin dasukayi, akace yanzu suna in
ane?.
Amsawa sukai da gasu a masarauta, dan harda Galadima sukayi aikin, yana kuma cikin wani yanayi shida yaran yanzu haka.
Basuda za6in daya wuce suce musu to suma gasunan zuwa masarautar.
Tun'a mota su Muftahu sun gargad'i baiwar nan
da d'ayan mutumin akan suce su biyune suka sacesu, inhar sukace basu kad'ai bane wlhy saiya kashesu, sannan su tanaji fad'ar wani abun ba ainahin gaskiya ba, (dan Galadima baya buk'atar police su shiga cikin aikinsa yanzu, yafison saiya kama kowa sannan,
dan inhar police suka shiga aikin mutane da yawa zasuyi escape ne) shiyyasa Muftahu yayma wad'ancan gargad'in tunma kan su k'arasa cikin masarauta.
Da yawa wasu basu rintsaba a masarauta gagara badau yau.
Munaya dai dole aka sake d'irka mata
allurar barci mai k'arfi, dan kusan kuma haukace musu tayi gabannin asuba, dalilin wani barci daya figeta tayi mafarki mai matuk'ar tada hankali.
Su inno Na zaune har yanzu suna kai kukansu ga ALLAH Muftahu da Sauban suka shigo d'auke da Galadima
da suka kamo tamkar gawa, sai Saleem da police biyu dake falo d'auke da yaran sukuma.
Zaram duk suka mik'e suna tambayar lafiya? Miya sami Galadiman?.
Basu sami wata amsaba, saida suka kwantar dashi a gadon sannan Sauban ya share hawayen fusk
arsa yana fad'in “suma yayi inno”.
Aunty Mimi da mom sukayi kan Galadima suna kuka, inno tace, “kun samo yaranne?”.
“eh gasu can a falo tareda police, saidaifa duk sun mutu, shiyyasa ma Yaa Sam ya suma”. yak'are maganar yana kuka.
H
awaye suka zuboma inno, waya ta d'auka ta kira papi, Wanda shima dai a zaune suka kwana dagashi har Sarki jalaludden.
A time d'in dama