Showing 297001 words to 300000 words out of 304903 words

Chapter 100 - FULANI COMPLETE

ta fasa kwai ta kwada shi kuma ya hada komai ya karyarwa.

Da rana ma haka ya girka musu jalof yana nuna mata yadda zata yi, duk

da ya san idan tai ba lallai ne yai dadi ba domin bata saba girki a gida ba sai dai yana da kyau ta fara koya tun a yanzu, da dare ma haka ya nuna mata yadda zata dafa indomie. Washe gari misalin 11 jirginsu ya daga zuwa Katsina, suna sauka Ra'ees ya iso y

a dauke su, zuwa gidan Shattima dake cikin garin Katsina. A gidan suka huta sai yamma suka shiga Bandalo, zo ka ga kauna Inna kamar zata hade Fadime, sai mamakin yadda Fadime ta soma canjawa take cikin kankan lokaci, Fadime ma tana ta murna ganin an gyara

gidansu kamar a birni. Bappa kam dukawa Shattima ne kawai be yi ba tsabar murna da farincikin ganinsu, duj yadda Fadime ta so ta kwana a gidan Shattima be barta wai saboda matsalar tsaro duk da kasancewar zuwan na su ma ba kowa ya san da shi ba. Da za su t

afi ne yake shawartar Bappa cewar zai sama masa wani gidan a cikin garin Katsina ya koma domin a ganinsa zai fi samun tsaro a can fiye da nan.

Ba dan ya fada mata gobe zai kawo ta ta sake ganinsu ba da ba zata yarda ta be shi ba su kwana a Katsina ba,

hakan kuma be hana ta yi masa kuka ba. Washe garin da za ta koma ta tashi da zazzabi mai tsanani, ko kanta bata iya dagawa sai da Shattima ya bata magani ta sha, bayan siyayyar da sukai musu ta Yola Shattima ya aika yaronsa aka siyo musu kayan abinci masu

yawa ya aika direba tare da kayan aka kai musu sannan ya kara ya sanar musu ba zata samu zuwa ba saboda bata jindadi. Kwananta uku a Katsina tana jinya sai da ta fara samun sauki sannan Shattima ya saka ta mota da police aka kaita ta wuni ta kwana a can ta

sake wuni ta kwana sannan tai musu bankwana tana ta kuka ta dawo Katsina, washe garin ranar suka bar Katsina zuwa Yola, kar ku so ganin yadda ta labe masa a jiki cikin girjin daman tana jin jikinta babu kwari tun rashin lafiyar da tai.

ZAINAB POV.



Yayi murmushi ya dauki karan dake gabansa ya saka a wuta.

“Miye alakar addini da soyayya?”

Kallonsa tai a zatonta idan ta fada masa haka zai janye kudinsa ne akanta, hakan yasa tun a lokacin da yai mata wacan maganar ta daina sakewa da shi.

“Yana da alaka mai karfi, a iya abun da na sani addinina be yarda mace ta auri mijin da bashi da addinin musulunci ba, amman an yarda miji ya auri mace ko bata irin addininsa”

“Kina fada min wannan ne da gaske ko kuma kina neman nisanta kanki da ni ne

?”

“Ma zai saka mace ta nisanta kanta da kyakkyawan namiji irinka? Kana da kyau Wasim, kyau na halitta da na zuciya, duk da kasancewarka ba musulmi ba kana da tausayi kuma baka cutar da kowa, baka wasu halaye na banza, babu macen da za ka taya wa kaunar

ka ta ki karba, sai idan da wani dalilin kamar wanda na fada ko makamancinsa”

Yayi murmushi a yanzu ya gamsu Zainab tana sonsa kenan ba kamar yadda zuciyarsa take raya masa ba.

“Me zai hana mu aje addini a gafe?”

“Babu wannan damar a gareni domin

rayuwata tana tafiya a tare da addnina ne, addinin musulunci addini ne mai sauki da kuma mai dadi, idan har na bar addinina to wuta ce zata zama makwancina ranar gobe kiyama”

“Ban gane ba”

“Ranar da za a tashe mu, ayi mana tambayoyi kan abun da muka

aikata, kuma ayi mana hisabi daidai gwargwadon abun da muka aikata, daga nan wanda ya aikata zubuni za a yafe masa idan Allah ya ga dama, idan kuma tsakaninsa da bawa ne dan'uwansa kamar ni da kai, sai a cire wani abu daga aikinsa a biya wacan idan kuma ba

shi da komai sai a ciro zunubin wacan a tafta masa, idan dan wuta ne zai dauwama a wutar idan kuma dan aljanna ne zai shiga aljanna bayan an gama kona shi, wanda yai aiki na gari kuma sai a saka shi aljanna daidai gwargwadon aikinsa gwargwadon matsayinsa

a aljanna”

Wani kallon mamaki yai mata.

“Wai kina nufin bayan wannan rayuwar da muka yi zamu sake yin wata? Bayan mun mutu kenan”

“Sosai kuwa, za a sake wata rayuwar da za a bi hakkin wanda aka zalunta, kuma azabtar da wadanda sukai zaluncin, tab

bas bayan wannan rayuwar akwai wata rayuwa, wata rayuwa mai ban tsoro mai tsananin firgitarwa, musamman ga mutanen da ba su bi Allah ba”

“Amman miyasa abubuwa bauta suke da yawa ne?”

“Abun bauta daya ne Allah Subhanahu wata'ala, shi ne dauwamammen ku

ma rayayye, shi kadai ya cancanci bauta kuma shi kadai za a bautawa a rabauta, shaidan ne yake raya ma mutane cewar akwai wasu abunuwa da suka cancanci bauta bayan ubangijina, ban taba burge ka idan ina sallah ko alwala ba?”

Ta tambaya tana kallonsa.

“Tun kamin ke akwai wanda nake ganin suna sallah da yawa, abun yana burge ni, amman ina ganin kamar akwai wahala ayin hakan”

“Babu wata wahala idan ka saba, kuma zaka samu natsuwa sosai a cikin ibadar”

Kadan ta labarta masa daga ibadar sannan ta jad

da masa.

“Idan har kana son na kuma ka shirya zama da ni, dole na ka aje addininka ka bi nawa, bin addinina kuma yana nufin watsi da al'adunka ka zama mutum kamar ni, ka aje tsafinka da komai”

Yayi murmushi.

“Kina da tsada kenan?”

Sai ta kai h

annunta ta taba fuskarsa.

“Sosai”

Yayi murmushi ya sake deban wasu karan ya saka a wuta, sai ta kwanta jikinta tana kallon wutar.

“Addinina be bani damar taba jikin namijin da ba muharramina ba”

“Minene haka?”

Ta fada masa da gamsasshen ba

yani.

“To miyasa kike yi?”

“Zan daina duk ranar da na samu wanda ya zama mijina halal malak”

Yayi murmushi.

“Barin addinina ba abu ne mai wahala ba, haka na al'adata domin ina jindadi idan nai shigar mutanen kirki masu saka tufafi irin naki, i

na jin na cika cikanken mutum, ina jin natsuwa idan an saka tufafin da suka rufe min jiki gaba daya, sai dai barin tsafi ina jin kamar zan cutu”

Ta dago da sauri ta kalleshi.

“Ba zaka cutu ba, ina tunanin saboda ni zaka yi, inda zamu je babu wanda z

ai mana sheri ko ya jefe mu da wani abu, zamu yi rayuwa ne cikin farinciki da kaunar juna, kuma saboda ni zaka yi ba kace kana son farincikina ba? Ba kace zaka zama min komai ba? Ashe ba so kake na jidadi ba?”

Ya karasa hawaye na sauko mata tana kallons

a, shi ma kallonta yake yana jin kamar ba zai iya ba, barin tsafin da ya zame masa jiki? Ba dan kalubalen da zai fuskanta ba sai dan sabon da yai da shi. Kawar da fuska tai tana cigaba da hawayen.

“Ashe ban cancanta ba, ashe ba da gaske kake ba, amman

na sani wata rana zan samu wanda yake so na da gaske, wanda zan iya yin komai saboda farinciki”

Ta mike tsaye sai shi ma ya mike tsaye ya riko hannunta.

“Ban taba yin karya ba, zuciyata bata raya min na fadi abun da ba shi ne ba, idan nace idan son

ki to ina sonki ne da gaske Zainab har cikin raina...”

Yayi shiru yana kallonta kamin ya cigaba.

“Idan har hakan zai faranta miki rai, kuma zai sa na rabauta, zan aikata na miki alkawari sai kin samu farinciki saboda ni...”

Murmushi da kuka ne ya

zo mata a lokaci daya sai ta lumshe ido tana maida numfashi a hankali.

FALMATA POV.

“Kenan ke yanzu cigaba zaki yi da karatun?”

“Eh ai sai da muka yi magana da shi yace ya yarda zan cigaba da karatuna bayan aure”

“Gaskiya haka yafi, ni

ma yace idan na haihu zai saka ni a makaranta, a gida yake dan koya min su gaisuwa da kuma yadda zan iya karatun hausa, gashi har ina iya hada hausa na karanta”

“Hakan yayi gaskiya, ai kin samu miji mai sonki da gaskiya Falmata, daman hausawa sun ce ma

i hakuri mawadaci”

Falmata ta yi murmushi tana kallon kawarta Khadija.

“Komai ya wuce, ni kaina ban tsammaci zan samu rayuwata a haka ba, Baba ma ya dawo kamar ba shi ba ko shekaranjiya sai da ya aiko Inna A'i ta kawo min daddawa da kayan yaji mai y

awa, ita ma tana da kirki sosai, ko kanen na tana kula da su sosai kamar yayanta, dawo da su da Baba yai a hannunsa ba karamin dadi n ji ba Wallahi”

“Ai yanzu kowa kirki zai miki Falmata, saboda anga kina auren mai arziki, da dai a dane za ki fi gane ma

i son ki da gaske da mai miki sheri, ita kanta Tumba da zata samu damar rabarki soyayya zata nuna miki”

“Haka ne, ko tana ina yanzu? Wannan matar ta cutar da ni sosai”

“Wallahi ni a yadda na ji wai tana cikin garin nan gidan wani kawunta”

“Da gask

e ashe bata koma kauye ba? ”

Khadija ta mere baki.

“Hmm ina zata iya zaman kauye ta saba da birni, ba shiyasa tai yadda tai ta aure Babanku bayan mijinta ta mutu”

“Su ma ai yau da gobe gajiya za su yi”

“Wallahi kuwa ai ni idan ban ga Tumba a t

iti tana bara ba, burina ba zai cika ba”

Cewar Khadija tana mikewa tsaye ta dauki atamfar ankonta, sai Falmata ma ta mike tsaye da cikinta tana fadin.

“Ni dai idan akwai babbar ki siyo min”

Khadija ta mata wani kallo.

“Iyyyyy yayi matar manya

wato kin bar bangarenmu ko? To dole sai kin saka irin ta mu Malama”

Falmata ta yi dariya.

“To ai ina son kalar atamfar ne, ko bayan bikin ne na rika sakawa”

“Eh na ji dai, sai kin saka kalar ta mu, ko kuma na kawo kayan lefena duk mijinki ya siy

a min masu tsada sai mu zama daidai”

Falmata ta yi dariya.

“Ai zai siya miki indai mijina ne ba shi da matsala, Amaryar ba kya laifi, zan miki order kaya na musamman gurin yar gidan Mai Fata, kayanta na da kyau sosai”

“Yauwa kawata haka nake so d

ai, a gyara ni”

Falmata ta kai mata duka.

“Khadija ba ki da kunya”

“Ke kina da kunya kika yi ciki ne? Ana ganinki ai an san me kenan”

Dariya sukai dukansu sannan ta raka kawarta har gurin gate, sannan ta dawo ta kwashe plates din da suka ci ab

inci ta kai cikin ta gyara ko'ina na falon, sannan ta haye sama tai alwala tai sallah ta azahar tai addu'a tai ma mijinta sannan ta mike tsaye ta nade carpet din ta aje a muhallinsa, ta sauko downstairs ta shiga kitchen ta soma dora girki, sai biyar ta gam

a komai tuwon shinkafa tai miyar taushe sannan ta dauko komai ta kawo dinning da jera duk da ta san mijinta ba mutum ne mai son cin abinci a dinning ba, musamman da cikinta ya girma din nan ya fi son su zauna kasa su ci abinci a tare.

Bayan ta gama koma

i ta shiga tai wanka ta shirya cikin jar abaya ta saka hula ta zauna saman gadonta tana kallon tv, after like 30 minutes wayarta tai ringing sai ta mika hannunta ta dauka ganin number Sirleem yasa ta murmushi.

“Hello”

“Babyn Baby?”

“Na'am ya aiki

n?”

“Da godiya i miss you”

“I miss you too”

“Fada min me zan siyo miki?”

“Bana son komai kuma karka mana takeaway na dafa tuwo”

“Oh baby ke da kanki?”

“Yes”

“Kin saba alkawari”

“Na ji zan iya ne, kuma ai likita yace na rika motsa ji

ki”

“I love you, kuma ina big surprise da zan miki ina tafe da shi?”

“Minene?”

“Idan na fada miki ai ta zama ba surprise ba, ina tafe da shi ke dai ki shirya kawai”

Kamin tace komai ya yanke wayar yana murmushi, mamaki ne ya cika ta jin yace ya

na tafe da surprised na minene, tana ta tunani kala kala amman ta kasa cankar ko minene, tana zaune a dakin har ta ji karar bude gate, wanda hakan yai daidai da kiransa a wayarta.

“Ban yarda ki leko ni ba, kuma ban yarda ki fito ba”

Shine abun da ya

fada mata a wayar sai gai shiru tana sauraren wayar da be yanke ba har ya fita motar ya rufe, sannan ya nufo falo manne da wayar a kunnesa ya bude ya shigo sannan ya ce.

“Za ki iya fitowa yanzu”

Aje wayar tai ta sauko saman gadon tana jin gabanta n

a faduwa for no reason, tafiya ta fara yi kadan kadan kamar wanda bata son fita daga dakin, kamin ta kai hannunta ta bude kofar dakin ma wani aiki ne, a hankali ta bude kofar dakin ta fito ta janyo kofar ta rufe ta fara saukowa a hankali, da Sirleem ta far

a arba ya sauko mata da sakon murmushi, sai ta mayar masa kamin idonta ya sauka gurin Ameer da ya mike tsaye daga zaunen da yake yana kallonta, idonsa cike da hawaye tsayawa tai cak tana kallonsa hawaye na sauko mata, sai kuma ta sauko da gudunta har sai d

a Sirleem ya tsorota ganin cikin dake jikinta, sanin zata iya rumgumar Ameer ko kuma shi ya rumgume ta yasa Sirleem yai saurin riketa ya rumgume sai ta fashe da kuka.

_________

Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke

cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku zo ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubb

are kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amm

a ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number  09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan h

ar waje kasar nan muna aika kaya.

Address: Nasarawa Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.

68

*Khadeeja Candy*

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank

, then send the evidence via 08036126660*

Kuka tai sosai kamin ta samu natsuwa, sannan Sirleem ya rikata suka zauna saman kujera daya, Ameer kuma yana zaune a dayar kujerar yana kallonta idonsa cike da kwalla.

“Momy ta fada min komai, na fahimci

komai a kuraren lokaci...”

Ya fada hawaye na sauko masa, Falmata kan kuka take tana kallon dan'uwanta tana jin wani irin shaukin kaunarsa na ratsata, bayan kanen da take da su yanzu ma tana da wani yaya. Sirleem ya sake ta ya nufi kitchen ya dauko musu

ruwa da cup ta zuba ma Ameer ita kuma ya dauka ya bata da kansa ta sha.

After ya sha ya aje cup din yana murmushin takaici.

“I wonder how ban gane cewar ke jina ce ba, na tafi na bar gida ina da dan wayo na, amman sai komai ya soma shafe min a kai,

and the most painful thing”

“An shafe maka komai ne saboda barin gidan da kai ba a banza ba ne, na san kana som Mama a yadda ka lake sai ka dawo kusa da ita kadai ya isa ya sanar da kowa ba da son ranka ya bar gidan ba, amman na san shirrin na Umma ne”

Ya daga kai.

“Haka ne ni kaina ina ji a jikina kamar ba a banza ba, saboda na saka zuwa neman mahaifiyata, bayan kuma tana cikin rai a kullum, na yi sa'a a lokacin da na bar gida, na yi nisan zango ban san inda zan je ba kawai dai na ji ina bukatar

nisa da gidan ne, Allah yasa na hadu da abokin Daddy shi ya dauke ni ya kai ni gida gurin Daddy, tun daga lokacin sai na fara fuskantar wata wahalar daga gurin Inna Kulu (Uwargidan Daddy) a kullum ina mafarkin Mama ina ji kamar zata nemi inda nake amman sh

iru, na sha wahala kamin Allah ya budewa Daddy ya zama babban mutum kamar haka, sai kuma na kara samun wata sa'ar na aurin Momy da yai mace mai hakuri da sanin ya kamata, ganin irin wahalar da nake sha a can yasa Daddy ya maida mi hannun Momy saboda bata d

a yara kuma tana nuna tausayi da kulawa a gareni sosai, Matar nan ta rike ni kamar ita ta haife ni, ban san zafin rashin uwa ba saboda ita, sai dai hakan ina fatar wata rana zan ga mahaifiyata, ashe lokaci ya kure min”

Ya fashe da kuka.

“Da Mama tan

a raye, ta ga yadda ka zama da ta yi farinciki”

Sirleem ya rumgume matarsa dake ta kuka yana lallashinta.

“Yadda Allah ya tsara abu haka yake kasancewa, kin ga da Allah ya so sai yayi ki a gidan masu hali inda ko ciwon kai kika yi sai an shiga damuw

a, Allah yana da iko da power da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login