Showing 282001 words to 285000 words out of 304903 words
cikin tsoro domin har yanzu be yarda ba.
“Ya akai ya zama yaro? duba dai”
Sirleem yayi murmus
hi tare da mikewa tsaye.
“Baba zan tsaya a waje Fatima za ta warware muku komai inshallahu”
Ya nufi kofa daga Tumba har Baba da Amaryar tasa kallonsa suke har ya fice. Baba ya kalli Falmata.
“Ban gane ba, daman can ke kin san yaro ne?”
Sai t
a girgiza kai ta fara bashi labarin farkon haduwarsu har zuwa aure da abubuwan da suka faru, tun Baba na tsaye har kai ya dauko kujera ya aza ya zauna yana sauraren Falmata, tana fada Tumba na kuka Naja ma ta rafka uban tagumi tana kallonta. Sai da ta kai
aya sannan Baba ya share hawayen da suka cika masa ido yana fadin.
“Allah ya dubi zuciyarki da maraicinki, da kuma halayenki na kirki da kika rike shiyasa ya bude miki kadan faga falalarsa da kuma rahamarsa, na sani na cutar da ke iyakar cutarwa, kuma
har ga Allah bana jin dadin abubuwan amman ya zamin kamar dole na musguna miki, mahaifiyarki ma na mata...”
Ya fashe da kuka, daman tun da hankalinsa ya dawo yake cikin damuwar abubuwan da ya aikata, Falmata ma hawaye take, Tumba na kukan nadama da dana
sani.
“Na tabbatar idan na mutu a halin nan, sai Allah ya hukunta ni domin yaya ma suna da hakki akan uwaye kamar yadda uwaye suke da hakkin akan yaya”
Falmata ya matsa kusa da shi tana hawaye.
“Ba halinka ba ne Baba, da can ba haka kake mana b
a, idan har akwai wani hakki nawa da yake kanka Wallahi n yafe maka shi duniya da lahira, kuma ina rokon Allah wanda ke tsakaninka da Mama ya daukar maka, na jidadi Baba yanzu ka gane gaskiya”
“Hakika ba hali ba ne, halin wacan bakar matar ne, tun da ta
shigo rayuwata komai ya lalace min, dangina ma yaushe rabon da na je ganinsu? Ta zallumci ni ta cutar da ni, na sa na ci amanar uwar yayana kuma na ci amanar yayana, Allah ya isa tsakani da ke Tummmba Tummmba Allah ya tsine miki albarka, yarana kuma da ki
ke ikirarin ba ki iya zama da su zan dawo da abuna cikin gidana kina da rai zaki gan ni da wata matar na auro mai son yayana, ke kuma Allah ya tsine miki albarka, babu irin cin amanar da ba ki yi ma yarinyar nan ba, babu kalar sherin da ba ki mata ba, kuma
ni ma kika min, ina jin son yata a zuciyata ina tausayinta amman ban isa na nuna ba”
Tumba ta hade hannayenta biyu tana wani irin kuka da bata taba mafarkin zata yi ba, domin ko a lokacin da hadarin ya faru hankalinta ya bace bata san zafin ciwon da ba
kincikin cirewar da kafarta tai ba sai daga baya, sai abun ya zame mata kukan zuci wanda ya fi na idanuwa zafi da bakinciki, domin ta rasa kafarta ga hannu kuma sai ruwa yake.
“Malam ka dubi girman Allah ka yafe min, dan'adam ajizi ne”
“Ajizo na ce A
jizo, da can ba ki san da haka ba sai yanzu da Allah ya kama ki? Ai ko wannan kadai ya isheki ishara, ga shi nan baki ga hannu ba ki ga kafa, kuma yarinyar da kike ma fatan sheri gata nan kin jefata cikin alheri ba tare da kin sani ba, ba ki isa ki hana ab
un da Allah yai mata ba, gashi ijaba nan kin gani Allah ya kaita a matsayin da babu wanda ya taba taka shi a cikinmu, Allah yai miki albarka Falmata ke kuma Tumba Allah ya tsine miki, kuma Wallahi babu ni babu ke daga yau daman can ba ni wani rabon mugun i
ri dake, ki hada komai na ki bar min gidan na saki”
Naja ta fashe da wani irin kuka ta rugo da gudu ta zube gabansa.
“Baba dan Allah kai hakuri”
“Ni ba ubanki ba ne, tafi can ki nemi ubanki kuma na kara mata saki daya ya zama biyu”
Tumba ta da
ga hannunta nan daya ta fashe da kuka tana ihun da duk wanda ke makotaka da su a kusa zai ji.
“Ba ki shiga uku ba, tukuna nan yanzu na kara miki wani sakin daya sai ki shiga ukun, kuma ina rokon Allah ya tsine miki albarka”
Falmata ta rufe baki da s
auri jiki na rawa jin irin sakin da Baba ya jerawa Tumba a take. Kukan da take ne yasa makota suka rika shigowa suna tambayar ba'asi, Baba abun da Baba ya boye daga kan abubuwan da take saka shi yana yi har zuwa wanda take yi ma Falmata, sai a lokacin ne m
utane suka san gaskiyar abun da yake faruwa, domin kowa yana mata kallon mutuniyar kirki saboda yadda take nunawa Falmata kauna a gaban idon mutane kamar zata hadeye ta, babu abun da ya bawa mutane mamaki kamar maganar auren Falmata, a nan wasu suka yarda
domin kowa yayi mamakin jin Falmata zata auri tsoho yarinya kyakkyawa kuma mai kananan shekaru. Duk wanda ya shigo gidan ya ji abun da ya faru sai mamaki ya kama shi, gashi babu bakin bada hakuri domin mai faruwa ta faru Baba ya riga ya aikatawa Tumba mai
gaba daya. Tumba kan kuka kawai take tana fadin ta shiga uku amana ta kamata, Falmata bata labarta musu wanda take aure ba balle su san fittacen mutum ne, sanin yaro ne yai shigar tsofi ma Baba ne ya fada, Naja kuma ana ciki kuka da jimamaki hakan yasa bab
u wanda ya san Sirleem ne, sai hakan be hanata zama abar kallo ba saboda tufafin jikinta da kuma gidan da aka kaita domin duk wanda yajr walimarta ya ga gida abun da ake kira da gida, har wadanda ba su je ba ma sun samu labarin irin gidan da aka kai Falmat
a.
Sai kusan goma na dare Falmata tai ma Baba sallama yana ta saka mata albarka, yana mata addu'a har da hawayensa har lokacin yana jin bakinciki da nadamar abun da ya aikata. Sai bayan da Falmata ta wuce ne ya duba kayan da Sirleem ya bashi ya ga turaruk
a masu tsada da kamshi gaske ga kuma kudin da za su haura 70k a ciki.
“Allahu Akbar Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar, Allah kai mata albarka”
Ya fada yana share hawayen idonsa. Falmata ta isa gurin da Sirleem ya aje motarsa tana hawaye
, tana jin kamar ace mahaifiyarta tana raye ta ga wannan ranar, ta dayan bangaren kuma zuciyarta na cike da farincikin dawowar Baba a hayyacinsa, tana taba motar sai Sirleem ya mika hannunsa ya bude mata motar ta shiga ta zauna ta rufe. Sirleem na kallonta
ya san akwai wani abu, hannunsa ya kai ya kama hannunsa ya dora a kirjinsa.
“Haba dai karki ce min tausayin matar can kike”
Ta kalleshi.
“Baba ya sake ta, ta rasa kafarta kuma hannunta yana ruwa”
“She get what she deserved”
“Rayuwa abar ts
oro ce Baby, wani lokacin Allah yana kyale bawa yai ta abun da yake so, idan ya tashi taba shi kadan zai taba shi amman sai ya zama abun tsoro, duk da irin makircinta bata hana Allah yi min abun da ya kaddara min ba, kuma gashi ta fara riskar sakamakonta t
un a yanzu bayan hukuncin da zata je ta tarar a lahira”
Ta lumshe ido hawaye na sauko mata.
“Daman duk wanda za ayi wa hassada ko kuma a cutar da shi, to zai yi ta samun cigaba ne, kuma zai ga riba hakuri a duniya kamin ya riski ladar lahira, I love
you...”
Bude idon tai ta kalleshi sai ta ji wani irin farinciki ya lullubeta marar misaltuwa.
“Alhamdulillah”
Ta furta sai ya ari numfashinta.
“Yeah Alhamdulillah da Allah ya ba ni mata irinki”
Ta yi murmushi shi kuma ya tashi motar yana t
ukawa da hannun daya yayinda dayan hannunsa yakr rike da hannun babynsa, time to time yake kissing din hannun kamar wani abun da ya zame masa dole. A zatonta gida za su wuce kai tsaye sai ta ga sun dauki hanyar zuwa Family house din su Hajiya Babba wato in
da take zaune a yanzu, this is the second time da zai kaita gidan bayan zuwansu na farko a lokacin da ake shirye shirye fitar da Hajiya Babba India, ya je tare da Falmata ya nemi yafiyarta Falmata kuma tai mata bankwana, a lokacin Falmata ta yi zaton Hajiy
a Babba zata mata wulakanci ne ko ta mata wani abun, sai dai babu ko daya ta kanta take ma, kana ganinta kasan tana cikin ciwo, a Lokacin kam Sirleem ya shiga cikin tashin hankali sosai wanda ya saka Falmata ita ma ta shiga damuwa ganin mijinta ma a cikin
damuwar, kusan kullum idan ya taso daga aiki sai ya je gurin Hajiyar, kuma be fasa bacin rai ba saboda halin da ta koma, bata iya komai da sashenta daya, bakinta kuma yaki dawowa daidai, komai take ci sai ya zubo mata ta gefen bakin haka ma yawu ke sauko m
ata gwanin tausayi, gaba daya ta canja kamar ba ita ba, cikin kankanen lokaci jikinta ya koma kamar na tsofi, sau uku ana fitar da ita waje amman babu wani canji kuma idan sun auna basa ganin komai, Jurry kam sau daya aka fitar da ita saboda ciwon kan da y
a saka ta gaba nan suka ce ba su ga komai ba, ana dawowa da ita sai abun ya kara kamar an takaloshi sai ya taba kwakwalwarta har ta kai tana yin wadansu dabi'u da halaye irin na masu tabin hankali, zata zauna ayi fira da ita cikin mutune sai dai da an fara
zata fara barin zance tana dariya irin na masu fama da hauka, hakan ya saka komai na rayuwarta ya tsaya cak bata fita ko'ina daga gida sai gida.
Sirleem yayi bakin harabar katon gidan da ya kusa gida ukun wani mutum, sannan ya bude motarsa ya fita kamin
ya zagayo har Falmata ta bude ta fito.
“Ba mu siya mata komai ba”
“Babu abun da babu a cikin gidan nan, babu abun da zata nema ta rasa, ni kaina wani lokacin sai na rasa abun da zan riko mata, saboda ba komai take iya ci ba”
Sirleem ya bata amsa
sannan ya nufi kofar shiga Falmata na biye da shi a baya, suna shiga falon yan jikokin gidan suka fara musu sannu da zuwa, sai ya rika daga su yana saukewa, sannan ya shiga ciki ya gaisa da wadanda suke manyansa Falmata ma ta gaisa da su kana ya nufi bang
aren da dakin Hajiya Babba yake, domin bangare aka ware mata mai komai a ciki har da yar aikinta ita ke mata komai har abinci hakan kuma idan akai na gida gaba daya za a dauko a kawo mata a falonta. Kausar da Karima dakinsu daya, Jurry ce kawai ke da daki
dabam saboda yanayinta. Da sallama ya shiga Kausar din ta amsa masa tana murmushi kana ta kalli Falmata.
“Anty Fateema sannunku da zuwa”
Falmata ta washe mata hakora tana jin girman da ta bata har cikin ranta.
“Kauwa Kausar ya gida?”
“Lafiya
Kalau”
Kai tsaye Sirleem ya wuce dakin Mahaifiyarsa, Falmata kuma ta zauna a falon tana kallon katon Plasma, Kausar taje ta dauko mata ruwa da lemu ta aje mata.
“Ga ruwa na san dai kun ci abinci”
“Alhamdulillah, na gode”
Kausar na ta kokarin j
anta ta fira ita kuma ta kasa sakewa sai jifa jifa take saka baki a maganar, har Sirleem ya fito ya kira ta ta shiga ciki su gaisa da Hajiya. Kamar dai wacan karon wannan karon ma da dan tsoro Falmata ta shiga cikin dakin ta gaisa da Hajiya Babba, sai ga H
ajiya Babba na amsa mata kamar ba ita ba, sai dai kam ta kurawa Falmata ido sai kallonta take, (Hausawa sun ce dan hakin da ka rena...) Tana cikin dakin Karima ma ta shigo suka gaisa a mutunce, sannan tai musu sallama ta fito, sai da Sirleem ya koma ciki y
ai mata sai da safe sannan ya fito suka kama hanyar gida shi da matarsa.
FADIME POV.
_1 Months later..._
Inna ba ta labarta mata komai ba har aka fara gyaran gidan, mutane sai murna suke shigowa suna musu da Allah sanya alheri, suna fadin Fadime
ta janyo musu alheri ta taimaka musu, ba karamin farincikin Fadimr takr ba, ganin za ayi musu gida irin na zamani, sai dai hakan be hana ta shiga damuwa ba, kusan kullum sai ta yi ma Inna maganar Shattima tana fadin matarsa ta huta, kaza da kaza. Inna dai
bata ce mata komai sai da aikin yai rabi, wanda hakan yai daidai da tafiyar da za'ayi Yola, a tunanin Fadime tare za a tafi da Inna da Bappa sai ita, domin a da har kirarin cewa take ita ba zata je ba, sai da Inna tace idan ya ji ba zai jidadi ba bayan du
k hallacin da yai mata kuma zata ja ya bata da ita har abada kamar yadda Wasim yai, hakan yasa ta janye kudinta na cewa ba zata je ba, sai dai har ga Allah ba dan tana son zuwa ban saboda Shattima zai auri wata ba ita ba, hakan yasa bata ma sake bin ta kan
wayarsa ba. Sai da ana saura kwana biyu su tafi sannan ta fada mata ba da ita za'ayi tafiyar ba.
“Saboda me Inna?”
Fadime ta tambaya tana kallon Inna da ke murmushi.
“Tare za ku tafi da su, Su Uwani da Dije, mu zamu zo daga baya ne”
“Miyasa
to?”
“Su suka ce a kawo ki da wuri wai akwai yan abubuwan da za ayi miki kamin lokacin biki”
Ta turo baki gaba.
“Bana so, waye yace haka?”
“Matar Sarkin ita ta fada min da kanta a wayar Bappanki, ta fada abubuwan da za'ayi amman ban rike sunan
ayensu ba”
“Ni dai bana so abar ni sai kun tashi tafiya sannan”
“Gyara fa za ayi miki”
“To lalacewa nai balle a gyara ni, ni dai a kyale ni bana so”
“Kin taba ganin anyi amarya babu gyara?”
Inna ta fada da dariya, sai Fadime tai mata wani ka
llo na mamaki, can kuma zuciyarta ta raya mata zolayarta Inna take.
“Inna Wallahi bana son haka, zan miki addu'a Bappa ya karo wata Wallahi”
Ta fada har idonta na cika da hawaye wai ita ala dole ta ji haushi. Inna ta yi dariya.
“Wollah ba wasa n
ake miki ba, amman idan kin je can ai za ki yarda”
“Inna ban gane ba, yi min da hausa”
Ta fada tana dukawa gaban Inna tsabar son ta ji komai, Inna ta yarfeta da hannu.
“Ke ar kina Fulani kina fadin ayi miki da hausa, arrrr Fulani da abun kunya”
“Eh na ji, fada min wacece Shattima zai aura?”
“Ke ce mana, ba shiyasa za a tafi dake jibi ba”
“Ya za'ayi na yarda?”
“Na taba miki karyar?”
“Aa”
Ta girgiza kai. Inna ta soma bata labarin tun a lokacin da Mai Martaba ya nada wasu mutanen ci
ki har da Waziri suka zo neman aurenta cikin sirri ba tare da duniya ta sani ba, kuma Bappa ya sallama musu ba tare da ya nemi izininta ba, akai komai a sirrance domin su a can basa son a bayyana Bappa ma a nan baya son a bayyana hakan yasa babu wanda ya s
ani sai yan'uwansa. Inna ta yi zaton Fadime zata tashi ta fara rawa ne tana murna saboda jindadi, amman sai ta ga akasin haka a gurin yarta, wai yau Fadime ce ta saka hannu ta rufe fuskarta da sunan kunya.
“Wallahi Inna kunya na ke ji”
Ta fada wani
kalar dadi na rufeta, Inna dai ta yi dariya tana girgiza kai
“Ashe kina da kunya”
Fadime ta tashi ta bar gurin da gudunta, ba Inna kadai ba har Bappa sai Fadime ta koma tana jin kunyarsa, fadar irin murna da dadin da take ji za'a mata aure kan har ba
ya misaltuwa, tun ranar ta fara ayyana irin yadda za a rika bata girma idan ta auri Shattima, ta dayan bangaren kuma tana misalta yadda za ta yi girki.
“Da safe in ce masa ina kwana”
Ta yi dariya tare da rufe ido duk kuwa da kasancewar ita kadaice
a sabon dakin na Inna.
“Da rana na dafa masa taliya ko shimkafa da miya ko wani abun na kawo masa lemu da ruwa, na ce sannu da zuwa”
Ta yi wani murmushin jindadi, sai kuma ta mike tsaye tana gyara sabon gadon Inna na masu karamin karfi.
“Kullum n
a gyara gadona na yi shara na goge komai, idan ya dawo na ce sannu da zuwa, da dare na hau gadona na kwanta shi kuma na shimfida masa bargo,.... Aa be dace ya kwanta kasa ba, sai dai ya kwanta a gado ni sai na shimfida bargo na kwanta a kasa”
Ta rumgume
hannayenta tana jin kamar ga nan ma dakin mijin, ko dan damuwar da mata suke idan za su tafi su bar iyeyensu Fadime bata yi.
“Ita kuma Ammy kullum zan gaishe ta na duka mata har kasa, ko Nana da take kanwarsa duka mata zan yi ai ance ayi ladabi da biy
ayya...”
Haka tai ta surutunta tana misaltar yadda za ta yi idan anyi auren, tun daga ranar bata sake gaishe da Inna a tsaye ba sai dai ta duka har kasa haka ma Bappa, kuma bata yarda ta hada ido da su domin indai kunya ce tana jin kunyarsu a yanzu kam
. Ana gobe za ayi tafi Inna tace ta je tai ma kawayenta bankwana amman kar ta fada