Showing 276001 words to 279000 words out of 304903 words
/>
“Ba waya ba ce”
“Minene?”
Inna ta tambaya cikin mamaki bayan ga karar abu tana ji.
“Memory ne na hade”
Cewar Fadime tana mitsika idon na rashin gaskiya.
“Ina
na taba jin memory na waka a cikin mutum? Ina kika gan shi?”
“A lokacin da na je can birni na tsince shi sai na hade da ruwa, shiyasa yake waka yanzu”
“Kuma be tashi waka ba sai a yanzu? Fulani ba za ki daina halinki ba ko?”
Kyalkyalewa tai da dar
iya ta fiddo wayar da har ta gaji da ringing ta tsinke.
“Na san ba ku iya karbewa ko kuma ku yi min fada shiyasa na boye ta, Shattima ne ya ba ni ita”
Inna ta buge mata baki kamar wanda tai sabo.
“Ke ki rika cewa ranka ya dade, Fulani ba ki da na
tsuwa”
“To ranka ya dade ne ya ba ni wayar”
Tana cikin fadin haka wayar ta sake ringing, tashi tai da sauri tana kallo red da green din toch din dayan ansa saka received dayan kuma hang up sai ta taba green din tana kallon yadda call din ya fara tafi
ya sannan ta kai a kunnenta.
“Hello”
Inna ta kura mata ido tana ta kallonta cike da burgewa. Ita kuma ta nufi gurin da aka daure shannun tana ta hello hello ba a amsa mata ba, sai ta sauke wayar ta kalli kiran ta ga yana tafiya sai ta maida wayar a
kunnenta.
“Hello Wasim....”
Ta fada tana fatar ta ji muryarsa ya amsa mata, sai ta ji muryar Shattima.
“Wasim ya ce zai kira ki ne?”
“Aa ni ban ma sake ganinsa ba, amman ai zai iya ganin an ba ni waya ya kirani tun da yana tsafi”
“Wato ba
ki cire shi a ranki ba ko?”
Ta yi shiru idonta na cika da kwalla.
“Ina son Wasim, ba zan iya cire shi a raina ba, yana da kirki sosai”
Shattima ya katse kiran gaba daya yana jin kamar ta soma masa mashi a kirji, kiran da yai mata na albishir ne s
ai dai abun da ta fada masa yasa ya ji baya bukatar cigaba da waya da ita, tsaye tai da wayar a kunne hawaye na sauko mata.
“Hello.... Hello... Assalamu Alaikum....”
Tun tana hello har ta gaji ta fara sallama, jin shiru yasa ta sauke wayar tana kal
lon awarwaron da ya saka mata, sai kawai ta fashe da kuka.
ZAINAB POV.
Tsaye take gaban wani karamun zafi dake ta kwarar da ruwa, lokaci lokaci take kai hannu ta share hawayen da suke cika mata ido tana rumgume da hannayenta, sai kallon ruwa ta
ke. Duk abun da take Wasim na zaune saman wani dutse yana kallonta, tausayinta ya cika masa zuciya sosai, he know how hard it's ka bar komai na ka ka dawo rayuwa inda baka saba ba, kuma da mutanen da baka saba ba, cikin wani addini na dabam da al'adar da b
aka saba gani ba, saukowa yai ya ta ko zuwa inda take tsaye ya tsaya gefenta yana kallon ruwan da take kallo.
“Akwai ciwo ko? Kina jin wani yanayi na dabam, hmm haka na ke ji saboda rabuwa da Fatime, amman na fi jin tausayanki, saboda ke kin rasa komai
ni kuwa wanda na ke kawai na rasa”
Ta kalleshi shi kuma yana ta kallon ruwa, ya cigaba ba tare da ya kalleta ba.
“Wani lokacin be kama mu dauki komai mu rike shi a rai ba, komai mai wucewa ne, ina jin yadda kike ji saboda ina jin kamar wani bangare
na rayuwata, kuma ina jin kamar zan iya zama silar farincikin idan kin ba ni dama”
Ta sauke kai kasa a yayinda shi kuma yake kallon fuskarta.
“Za mu bar garin nan saboda ki samu farinciki kuma ki sake, ki cigaba da rayuwa kamar yadda kike saba”
T
a kalleshi tana murmushi idonta kuma na zub da hawaye.
“Har da kai?”
“Eh, to me zan yi idan na zauna a garin? A duk lokacin da na tuna abun da suka min akan Fatime zai na ji bana bukatar zama garin, kamar yadda ke ma na san garin ba dadi yake miki ba
”
“Bana jindadi, amman ina kokarin kafa rayuwata a nan ne saboda mahaifiyata tana nan, babu inda ya fi min dangina”
“Ba tafiya zaki yi ki barsu har a bada ba, zaki rika zuwa kina dubasu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso, ko ba komai za ki fi jin
dadin rayuwa a inda nutane masu irin addininki suke rayuwa sama da nan, maganar mahaifiyarta ki kuma ki barta”
“Saboda me?”
Shiru yai yana kallonta kamar mai fargabar abun da zai fada mata, sai ya mika mata hannunsa.
“Ina son ki yarda da ni Zaina
b, ina son ki aminta da ni, ki ba ni dama kuma ki sake jikinki da ni, ta yadda zan iya yakar kucin dake zuciyarki, ina son na shimfida miki wata sabuwar rayuwa wanda ni da ke zamu manta da komai mu yi farinciki kamar kowa...”
Hannunsa ta kalla sannan ta
kalleshi gabanta na bugawa da mugun karfi da kuma sauri a lokaci daya.
“Me ya faru da Iya?”
Sai da ya hade yawun bakinsa sannan ya ce.
“Iya ta mutu tun a ranar da na rabo ta da ke, cikinta ya kumbura sosai muna isowa nan sai ya fashe saboda kan
karun maitar dake ciki”
Baya baya tai wasu zafafan hawaye na sauko mata, saurin rikota yai ganin zata fada a cikin zafin ruwan, sai ta durkushe a masa jikinta na rawa ta rike warkin dake jikinsa da karfi kamar zata yagashi ta fashe da kuka mai karfi.
“Kenan na rasa kowa... Na rasa kowa.... Na rasa kowa...”
Ta maimaita har sau uku muryarta na rawa, hawaye na sauko mata kamar ba gobe, lokaci daya idon Wasim ya cika da hawaye.
“Ba ki rasa kowa ba Zainab ina tare da ke har abada”
Ya fada tare d
a dukawa ya rumgumeta sosai ta yadda zata yarda har a yanzu akwai wanda ya damu da ita kuma yake tare da ita.
_________
Ina mata matan kwalisa Matan da suka ansa sunansu na Mata? Ina wadanda ke cewa mun yi mun yi bamu ga amfaninshiba? Hmmm to ku z
o ga Yar gidan Maifata ta zo maku da Al ajabu, dan tsugunno, gumba da tsimi da Zuma daban daban, maganin sanyi na maza da Mata. Ga kuma garurruka irinsu mallakau sabuzu kuwa, sa bahaushe saibi, Dan hubbare kafi malam aiki, ke kadai ke da miji, dahuwar kaza
, tattabara, ciccibi da dai sauransu. Ba anan kayanmu suka tsaya ba, muna hadin amare na musamman turaren sutura turaren tsugunno turaren wanka da na daki da na jiki duka 4amare nasu na musamman ne, amma ga tsuhuwar da ke son komawa yarinya itama zata iya
zuwa ahadata kai abundai sai wanda ya gani, dan haka karkubari abaku labari, domin neman karin bayani zaku iua nemana ta wannan number 09029891757 ko 08169311410, muna aikawa ko'ina a fadin kasar nan har waje kasar nan muna aika kaya.
Address: Nasarawa
Samaru Area gurin masallacin mai sola Gusau Zamfara state Nigeria.
63
*Khadeeja Candy*
*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 300 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*
3 MONTHS LATER...
Fadime na tsaye bakin bukkarta dafe da waya a kunnenta sai faman dariya take. Yadda dariyar take isa a kunnen Shattima sai ta saukar masa da natsuwa har ya samu damar murmushi.
“To yanzu fada me nake yi?”
Yayi shiru yana kamar
mai tunani.
“Kina tsaye bakin kofar bukkarku”
Ta wara ido tana dariya.
“Wallahi ka canka daidai, dan Allah waya koya maka?”
“Wasim”
Ta sake yin dariya.
“Wallahi Wasim be ko ya maka ba, ai baka san shi ba baka taba ganinsa ba”
“Na hadu
da shi ban fada miki ba ne kawai, kuma yace kar na fadawa kowa wannan lakanin”
“Hahaha ban yarda ba, sai na ganka a gabana”
“Rufe idonki”
Ta rufe kamar yadda ya bukata, sai ya mike tsaye daga kan kujerar da yakr zaune ya dauki apple daya ya nufi
windows din dake dakin.
“Ki fara siffanta ni da irin sifar da kike son ganina zan bayyana yanzu”
“Na san kai fari ne, ina son na ganka a cikin green din yadi, da bakar hula kana kamshin turarenka, kana murmushi kana kallona”
Murmushi yai.
“Gan
i nan zan taba ki...”
Saurin buden idon tai a zatonta da gaske ne, sai ta ga babu kowa a gurin.
“Ba ka iya ba, kawai kana canka ne”
Murmushi yai sauti.
“I can't wait to see you Fateema...”
Ta yi shiru tana murmushi.
“Idan na fada cewar
kana kira wai ba a yarda da ni”
“Ba na ce ki daina fadawa kowa ba?”
“Kuri na ke yi ai”
“Kurin me?”
Ta yi dariya da yar siriyar muryarta, ba ta ce komai ba har na tsawon lokaci.
“Zan aje waya, amman kamin na aje fada min abun da kike so”
“Karatu dan Allah ranka ya dade, ina son karatu ka ga Bappa na yana jin maganar ka dan Allah ka masa magana ya bar ni na yi likita kamar kai”
“Hmmm miyasa sai likita? Why not lawyer ko wani dabam?”
“Aa irin na ka dai”
“To ai kin kusa zuwa nan sai
a saka ki makaranta kawai”
“Waye zai kawo ni?”
Yayi shiru yana jin kamar yayi subul da baka.
“Yan'uwanki mana, very soon za a kawo ki”
“Tare da wa?”
“Yan'uwanki”
“Da gaske?”
“Na taba karya?”
Ta yi dariya har da kyalkyalawa ta rufe
ido kamar yana gabanta. Shi ma murmushi yai he can't say bata son shi amman zai iya tabbatarwa duniya izuwa yanzu Fadimr bata da wanda yake saka ta nishadi da sauraren labaranta any how kamar shi, all her silly questions zai bata amsa be taba jin ya gundu
ra ba duk da kasancewar ba mutum ne mai son yawan magana ko tambaya, but he can't tell why idan Fadime ce zai tsaya ya saurarenta kuma ya amsa mata, kuma be tana gajiya da kin kiran a waya ba, ita kuma da ta iya kullum za a jera masa filashin ya fi a kirga
haka ma Bappanta da duk wanda take da number shi.
Bayan ya katse kiran ta koma cikin bukkatarta ta aje wayar da screen dinta ya gama cin ubansa a hannunta saboda faduwan da wayar take any how, fitowa tai ta nufo inda Inna take zaune tana gyaran shinkafa
ta zauna kusa da ita.
“Inna wai zamu ta fi yola?”
Inna ta kalleta.
“In ji wa?”
“Ranka ya dade ya fada yace wai za mu tafi Yola”
“Eh”
“Gurin me?”
“Gurin Aurensa mana”
“Aurensa kuma?”
“Eh”
“Aure zai yi?”
“Eh ba kin ce ba k
i son sa ba?”
Take idonta ya cika da kwalla gabanta yai mugun faduwa.
“Amman be fada min ba, Inna da gaske?”
“Eh mana ba kin ce baki son shi ba”
“Ni ban ce ban son shi ba, na dai ce ina son Wasim, kuma na ce garin ya min nisa, amman ai yana da
kyau kuma yana da sarauta”
Inna ta kalleta da kyau.
“Ashe kina da hankali, har kin iya kwadayi Fulani?”
Hawaye ne ya sauko mata, har ga Allah a lokacin da Bappa yai mata maganarsa ba ta ce bata son shi ba, tace dai ita tana son Wasim, domin har
kusan dukanta Bappa yai a lokacin amman bata dauka aure yake nufi ba.
“Kuma ai cewa yai Fulani za ki iya auren ranka ya dade be ce yana so na ba”
Ta fada tana jin wani irin kololin bakinciki na ta so mata kamar ta hade zuciya ta mutu. Mikewa tai ts
aye ta nufi bukkarta hawaye na sauko mata, if ta san Bappa yana nufin Shattima yana son ta ta ya za a iya cewa aa? Tana tana son Wasim amman shi ma Shattiman ai tana sonsa musamman a irin wannan lokacin da yake kawar mata da kewar Wasim, kuma yake yawan fa
ranta mata rai.
“Kenan yanzu wata zai aura?”
Hawaye ya sauko mata, sanin cewar ba za ta iya fadawa Bappa cewar yanzu ta aminta ba, ko ma ta aminta ai ba a a fasa auren ba, amman shi be fada mata haka ba kuma be fada mata cewar zai yi aure ba.
“Y
anzu ai zai dinga ganin na masa butulci...”
Ta fada kamar gaske irin na yan matan nan da suka dade tare da sarauya daga karshe suka yaudare shi.
“Daman ba ni da sa'a babu mai cewa yana so na, Wasim ne kawai ya ce haka shi ma kuma ya tafi ya bar ni w
annan ma haka”
Ta dauki wayar ta jefar a kasa iya karfinta tana jin wani kololon bakinciki na taso mata, hakan be wadatar da ita ba sai da ta saka fada ta taka wayar tana hawaye.
“Bana son wayar bana son komai”
Ta fashe da kuka marar sauti tana j
in cewar laifin na Bappa ne, da be fahimtar da ita ba har ta gane. Fitowa tai tana kuka ta zo gurin Inna tana fadin.
“Kuma Wallahi ba zan je bikin nan ba...”
Inna ta yi dariya ta soma mata magana da halshen fulatanci.
“Kishi kike kenan?”
“Ni b
ana kishi kawai dai ina jin bakinciki, kenan ni ba zan yi aure ba? Ba ni da farin jini... Ban san wa na gado ba”
“Ubanki kika gado, waya ce ki ce ba ki so? Ke wai har yanzu ba za ki daina halinki ba ko Fulani?”
“To a dawo baya a tambaye ni, ni ba cew
a na yi bana so ba, cewa na yi ina son Wasim shi ma ai da ne, yanzu na rasa kowa”
Inna bata sake bin ta kanta ba, domin maganar cewa bata san wa ta gado ba ya batawa Inna rai kuma ta san da ita take.
“Inna dan Allah idan Bappa ya dawo ki ce masa a b
ar wacan maganar, amman karki ce ni na ce”
“Sai ki fada masa da kaki”
Tashi Fadime tai ganin da gaske Inna take zancen auren Shattima, daukar abun tai ta saka a rai kuka ta sha b dan kadan ba tana tunawa yadda tai ta fama a baya babu saurayi mai sont
a, tun da ta shigr ciki dakin bata fito ba har akai sallah azahar sannan ta fito tai sallah, Inna na fadin ga abincinta bata kula ba ta koma ciki ita ala dole abun duniya ya isheta. Gashi sai tunanin Shattiman take yadda yake mata da kuma dan zaman da tai
a can ta sabo da shi, bayan shi yanzu kan bata da wanda take ganin zai iya zuwa ya ce yana sonta ko ya so ma. Kuka tai sosai har sai da fatar idonta ta soma ciwo, Inna bata dauki abun da gaske ba har sai da akai la'asar ta ga Fadime ta fito ta yi alwala ta
koma ciki ta yi sallah kuma bata fito ba.
“Fulani Fulani...”
Tana jin Inna na kiranta ta ki ta amsa, domin ta daura damarar kin cin abinci da sakewa saboda abun da Inna ta fada mata. Inna ta yunkura zata tashi kenan sai ga sallama wata bakuwar fusk
a tare da wata Lanti yar'uwar Amo, sosai gaban Inna ya fadi ganinsu a cikin gidan. Ta amsa musu a sanyaye tana mika musu gaisuwa cikin karfin hali zuciyarta na raya mata ko dai wani abu suka zo su yi ma Fadime ko ita ko kuma Amo suka maido dakinta.
“Sa
nnu da zuwa”
Inna ta fada sannan ta nufi bukkarta ta dauko musu tabarma ta shimfida musu, ko kallon tabarma ba su yi ba suka ce.
“Aa ba zama ya kawo mu ba, ina maganar zama aure ya kare”
Inna ta ji gabanta ya fadi.
“Kaya mu ka zo kwasa?”
“
Lafiya dai?”
“Allah dai ya kyauta idan Jauro ya dawo ai sai ki tambaye shi”
Lanti ta sake fada sannan ta bukkar Amo ta bude rufin da akai ta dage labulen zanen ta shiga ta fara to da kayanta, yan tsuman kara sai yan tarkacenta, wanda suke tare kuma t
ana shirya kayan tana kullewa a zane, ta dauka ta kai wajen mai yar gof din da suke tare yana sakawa har suka kwashe komai tsab Fadime bata leko waje ba, Inna kuma na tsaye tana kallon ikon Allah zuciyarta na raya mata abubuwa kala kala, sai dai fi tunanin
mutuwa Amo tai duba da tsawon lokacin da aka kwashe ba amo ba labarinta.
“To Amo dai zama ya kare sai ki shimfida tabarma dakinta ki kara, ki biya bukanki bukatarki ta biya”
Lanti ta fada sannan ta sa kai ta fice, Inna na maida mata da martani.
“Ba ni da boka ba ni da malam sai Allah, komai aka min Allah ne mai kare ni kuma mugun abun ta ne ya koma kanta”
Kalaman da Inna take ne yasa Fadime fito tana kallon bukkar Amo da aka bude, tana jin lokacin da ake kwasar kayan amman ta ki fitowa sai da
ta ji Lanti na fadin zama ya kare. Zuwa tai ta leka bukkar ta ga babu komai ciki sai dan abunda ba a rasa ba marar amfani.
“Kenan mun huta mun huta mun huta”
Ta fada tana rawa kamar ba ita ba.
“Allah yasa ma ta mutu can mugun abun ta ya bita, mun
huta da dangin mayu”
Rawa take har da juyawa jamar ba ita ce ta gama kuka ba, Inna dai sai kallonta take domin idomta ya nuna kuka tai amman yanzu tana murna an saki Amo.
Bappa be dawo a sai yamma kamar yadda ya saba, tun kamin Inna ta