Showing 240001 words to 243000 words out of 255051 words
(number). Wannan dai ba
ɗ
ayan bane, wani sabon Boka ne gagarumi da Maryama ta tabbatar
musu cewa aikinsa wane wancan! Daga yanda ma ake yi a wurin ba ka ganin kalar talauci a wurin ka san harka ce ta manya don kowacce ta sha shadda mai dandasheshan kyau sai kuwa daidaiku masu leshi. Su da suka yi shigar atamfa ma sai suka raina tasu kwalliya
r. Ba don komai ba sai don ba su zo da tsadaddun ba na gani a fa
ɗ
a. Hankalinsu na kan aikinsu.
Sai da layi ya iso kansu suka yi zumbur suka miƙe, ganin su na kokarin shiga tare mai tsaron wurin ya dakatar da su. Cikin Hausarsa da ba ta fita sosai ya
dakatar da su.
"Ba'a shiga mutum biyu komai kusanci."
Jin haka suka dubi juna jin abin banbarakwai wai namiji da suna Hajara. Ba su ta
ɓ
a zuwa an musu iyaka da shiga wurin Boka tare ba, karshe dai ganin mutumin na harararsu ya sa Hajiya Batool t
a ja baya.
"Soma shiga bari na yi jira."
Hajiya Zeenatu ta shige ita kuma ta koma ta zauna.
Kwarjini iyakar kwarjini mai bada tsoro shi ta gani a fuskar wanda aka kira da Gamsheƙa, fuskarsa babu
ɗ
igon walwalwa. Tana zama babu tambaya ya ne
mi sanin sunanta kawai kafin ya soma motsa wasu irin ƙaho da duwatsu da ke cikin wani ƙaton abu kamar tire kamar kuma ba shi ba. Sai da ya gama ya dubeta ya shiga kora jawabi.
"Mijinki da kika yiwa asiri mai suna Husseini, ya dawo hayyacinsa ya sake k
i, ya kuma auri wacce a duniya kika tsana, kuma burinki bai wuce na ganin kin hallakata ba. Sai dai kuma ki sani, tuni kin makara don soyayyarsu babu karfin shai
ɗ
ancin da zai iya hallakata. Amma ina mai tabbatarmaki juya tunaninsa abu ne mai sauki idan kin
aikata duk abinda za mu sanya ki babu musu."
Hajiya Zeenatu wacce idanunta ya rufe nan da nan ta hau gyada kai tamkar ƙadangaruwa.
"Wallahi a shirye nake, ko menene zan aikata idan har burina zai samu cika."
Ya jinjina kai da yin murmushi m
ai kama da na mai jin kashi.
"Shikenan, a yanzu za sadu da ke ta gaba da kuma baya, daga karshe zan
ɗ
ebi abinda ya fita daga jikinki na najasa na ha
ɗ
amaki wani ƙullin magani wanda za ki tabbatar kin yi yanda ki ka yi, kin fesa a fuskarsa. Sai kuma w
ani tulu da zan ba ki wanda ke dauke da zucciyar mutum soke da allurai, shi ne mafi hatsari cikin ayyukan da zan maki. Kar ki kusa ki bari ya fashe, muddin ya fashe ki sani komai zai iya faruwa da ke, wannan hukuncin ya rage ga aljanun da suka satomin zucc
iyar. Don haka kin yarda kin amince za ki iya?"
Hajiya Zeenatu wacce tun sadda ya yi batun saduwa ta baya ta yi turus, kirjinta ya shiga dukan tara-tara, abu ne da ba ta ta
ɓ
a aikatawa ba, bar ta dai da aikata zina shima a baya ne kafin shigowar jarumi
kuma namijin duniya Hussein rayuwarta. Daga shi babu waki namiji da ta ƙara yiwa kallon abin marmari.
'Ki tuna fa, wannan namijin kike kwa
ɗ
ayin maidoshi rayuwarki yanzu Zeenat, kada ki yi sake. Wannan ce kadai mafita.'
Wani
ɓ
angare na zuciyarta
ta mata tuni, nan da nan ta dubi Gamsheƙa da har ya soma gundira da shirunta.
"Na amince. Zan kiyaye dukkan sharu
ɗ
a."
Ya miƙe tsaye ya ba ta umarnin ta biyoshi. Daga haka ya nufi uwar
ɗ
aga bayan sakin labulen window, hakan ya sa Maitsaron ya f
ahimci shugabannasa ya shiga aiki. Wannan yasa bai yi gigin lekawa ba.
Sun kwashe kusan fiye da awa ana abu
ɗ
aya don Gamsheƙa dai ya samu ya da yake so, a karshe ya fito ya bar Hajiya Zeenatu da
ɗ
ibar abinda ya umarceta a kwalba sannan ta mike ta fad
a bandaki ta dauraye jiki ta fito. Koda ta dawo ta iskeshi har sannan ba walwala kamar ba shi ne ya gama kukan mage ba.
Gani ta yi ya ha
ɗ
amata komai ya miƙamata sannan aka yi bayanin kudade ta biyashi da kudin Ƙasar don tun a Damagaran suka yi chan
ji.
Koda ta fito mai tsaron ya ba Hajiya Batool damar shiga, ita kuma ya ce ta fice don baa kara zama idan an fito, hakan laifi ne babba. A gaggauce ta fita, yaron Maryama zai karbi tulun hannunta dake cikin kwali ta yi saurin dakatar da shi ta ce ya
bar shi. Don ji ta ke idan har ba ita ce ta riƙe ba to fa komai zai iya faruwa. Duk fargaba ta cika zuciyarta.
Tana nan zaune a motar har kusan shudewar awa guda kafin Hajiya Batool ta karaso, ita har da hawayenta ma don ita kadai ta san me ta ke ji
a bayanta tun abinda ya gudana tsakaninta da Gamsheƙa. Hajiya Zeenatu ta kalleta kawai don ta san duk kanwar ja ce. Ita ba tulu sai wani kwalba a cikin kwali, ba su ba junansu labari ba sakamakon ba su daya ne a motar ba, haka suka kama hanyar gidan Marya
ma kowannensu da abinda ya ke saƙawa. Kamar yanda kowanne ke tunanin bala'in da zai sameshi idan har suka yi gangancin
ɓ
ata aikinsu.
***
ADAMAWA
Kwanakin da suka biyo baya, banda soyayya ba abinda Hussein da Ramlat ke gurza, gaba dayansu sun
sauya sun kara wani fresh da kyau. Hafsat ba ta bar aron wayar Ramlat a faƙaice ba tana gaisawa da Tahir. Ita dai Ramlat a tsorace take da hakan sai dai ganin Hussein bai ta
ɓ
a kamata da laifin ba yasa ta
ɗ
an ji nutsuwa ka
ɗ
an.
Ranar da ta cika sati
ɗ
aya cif a garin Adamawa, tana zaune a falonta, dawowarta kenan daga sashin Dada. Hussein ya shigo fuskarsa ka
ɗ
ai ka kalla za ka san yana cike da tsantsar farin ciki. Hannu kawai ya waremata ba musu ta ƙarasa ta rungumeshi. Ya kuwa
ɗ
agata cak yana juyi da i
ta, dariya ta yi bayan ya sauketa ƙasa yana nishi da riƙe ƙugu.
"Heart, kin fa ƙara nauyi."
Ta turo baki irin na shagwa
ɓ
a
ɓɓ
un yara, ya yi murmushi da jan karan hancinta kafin ya rungumota ta baya.
"Albishirinki."
"Goro."
"Alhamdu
lillah, bisa la'akari da workkng experience dina da kuma credentials, Yayanmu ya samarmin aiki a wani Kamfanin gine-gine. Sosai su ka yaba da komai nawa "
Ta juyo ta ba shi kyakkyawan sumba a kumatu. Ganin ya jefata da wani kallo ta kauda kai tana mur
mushi don har sannan wani lokacin Hussein dinta kwarjini ya ke mata.
"Congratulation, Allah Yasa a fara a sa'a. Ya kara daukaka."
"Ameen dearest one."
Daga haka ya jawota ya hau yi mata ra
ɗ
a a kunne. Daidai sadda wayarta ta yi ringing, kasa
ncewar shi ne a kusa, ya
ɗ
auma, ganin baƙuwar lamba sai ya
ɗ
aga kawai, bai kai da sallama ba muryar namiji ya ratsa dodon kunnuwansa.
"Assalamu Alaikum, Adda barka da rana. Taheer ne."
Wani irin kallo ya ke bin Ramlat da shi, Ramlat gabanta ya fa
di, ta sani dai a dazun Taheer ya kira ya ce yana son magana da Hafsat zai mata wani albishir, ta ce ya bari idan ta shiga gidan sai ta kira. Shaf ta mance, kuma ba ta samu shiga ba sakamakon wankin undies dinta da ta tsaya yi. Jikinta ya bata akwai mats
ala. Ba ta gama tantancewa ba sai da ta ga Hussein ya miƙamata wayar ya kuma ƙuramata idanu. Ta kar
ɓ
a da rawar hannu, gaba daya ta ru
ɗ
e, tunda suka yi aure ba ta ta
ɓ
a ganinsa a wannan yanayin ba kuma ma adalilinta sai yau.
I just published
"BABI NA SITTIN DA BIYAR" of my story "Ƙarfen Ƙafa". https://www.wattpad.com/1032619087?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Rufaida-Umar&wp_originator=WqGcOpyrKLCeYJ2pB6S21O2rofM3hfkPhk
l8xHn5YliOXRIEhSFgVvGwVllJASGRLQwGf8a%2FEFI9gUseG%2BLsfaQfid671L2Bpg0RFziPc0xIuxqo35SEHCqXV8izbKgB
🕯
️
*ƘARFEN ƘAFA*
🕯
️
_*Rufaida Umar*_
Bismillahir Rahmaanir Raheem.
65)
_*Assalamu alaikum masoyan
karfen kafa. Ina ba ku hakuri mai yawa. Na so kwarai na ha
ɗ
a post din nan da na karshe na aiko gaba daya, sai dai na sani kun yi hakuri iyaka, makaranta da ma sauran abubuwa ke
ɓ
oyeni da hana ni typing. Saboda damuwar da ku ka yi na hakura zan soma posting
wannan, daga shi kuma sai BABIN KARSHE in sha Allah. Ku yi hakuri, na tabbata duk wanda aka ba hakuri baa aikatamasa daidai ba. Amma kuyi hakuri. Ina kaunarku fisabilillah.*_
"Hello. Taheer ba..ta..ba ta kusa."
Daga yanayin muryarta
ya fahimci akwai matsala, bai kara magana ba ya katse wayar yana mai dana sanin kiranta duk da irin gargadin da ta yi mishi akan muddin ba ita ta nemeshi ba su yi magana da Hafsat, kar ya yi gangancin kiran wayarta.
Hussein juyawa kawai ya yi ya wuce
ɗ
akinsa, ta dage goshi tana kiran sunan Allah, shakka babu laifinta ne ko me ya faru. Ta sa
ɓ
a umarninsa na hana Hafsat waya, tunda yanzun ba amfani, abinda ya ke gudun, tana yi da wayarta.
Ramlat ta numfasa, tunani take ta bishi ko ta kyaleshi zuwa
anjima ka
ɗ
an? Sai dai idan ta rabu da shi, tana tsoron kada ya ƙi cin abinci alhalin daga yanayinsa kadai ma ta fahimci ya kwaso yunwar.
Mikewa ta yi tsam ta nufi dakin. Ba ya nan, alamar an kunna ruwa yasa ta fahimci yana ban
ɗ
akin. Ta nemi wuri gefe
gadon ta zauna, ta
ɗ
an jima zaune kafin ya fito
ɗ
aure da tawul a ƙugunsa sai karami a hannun yana share ruwan gashinsa. Bai ko kalleta ba ya yi gaba zuwa gaban madubin, da saurinta ta karasa ta bayansa, ganin abinda ta ke shirin yi, wato rungumoshi, sai k
awai ya juyo fuska ba walwala hakan ya dakatar da ita, ta sunkuyar da kai har idanun sun cicciko da kwalla.
"Don Allah ka yi hakuri, ba zan ƙara ba. In sha Allahu an yi na farko da karshe."
Bai ce mata komai ba ya juya ya bar gaban madubin bayan
ya gama abinda ya kai shi. Ramlat jikinta duk ya yi sanyi, ta sa hannu ta dauke hawayen da ya gangaro. Shi kuwa gogan, yana kammala shirinsa cikin kananun kaya ya feshe jikinsa da turaruka masu kamshi, ya fice. Ta bi bayansa da sauri ganin ya dauki mukulli
n mota, da wani irin gudu da ba ta san ta iya ba ta rigashi isa da ƙofar ta tare. Duban tsakar ido suka yiwa juna, kowannensu sai da yanayinsa ya sauya. Ba tare da ta dauke idanunta ba ta ce.
"Don Allah ka saurareni, nayi maka laifi ka yi hakuri ka ya
femin."
Kamar ba zai tanka ba sai kuma ya kare tamke fuska.
"Tun yanzu zan yi hukunci akan abu, ki nunan bai maki ba har ma ki goyawa wannan abun baya, wane irin kallo kike son na yi maki? Ke a yanzu sai dai ki ba wani labarin abinda ya gudana ts
akaninmu da uban yaronnan, duk wannan ma bai min ciwo ba kamar yanda har kika iya take umarnina. Ko ban hanaki ba, tunda har kika ga na raba ta da wayarta kin san me nake nufi. Ban wuri na wuce."
Maimakon ta matsa sai kawai ta noƙe kafa
ɗ
a gami da mara
iraice fuska, kallonta kawai ya ke yi. Daga yanayinsa ta soma fahimtar ya soma saukowa don haka ta sanya dukkan hannuwanta ta rungumoshi ta kwantar da kai a saman kafa
ɗ
arsa.
"Ka yi hakuri, na tuba ba zan ƙara aikata laifi irin wannan ba. Please Haske
na."
Shirun da ta ji har ta fidda ran zai sauko, ta soma kokarin janye jikinta ya riƙo ƙugunta dakyau, fuskarsu ya ha
ɗ
e wuri guda yana bin karan hancinta da kallo kafin ya maido idanunsa cikinnata.
"Kinsan ba na iya fushi da ke ko?"
Ta yi m
urmushi ta lumshe ido gami da gya
ɗ
a kai duk a lokaci guda, a hankali kuma ya shiga aikamata saƙo mai kashe jiki. Karshe dai Hussein fitar da bai yi ba kenan, dama sanadin bacin ran da yake ciki ne ya tilasta masa son fita. Can ta janye jikinta ganin yanda
ta matsu da jikin ƙofa.
"What?" Ya fadi da dusasshiyar muryarsa. A shagwa
ɓ
e ta amsa.
"Yunwa."
Ya yi murmushi gami da
ɗ
aga rigarta ya shafi cikin. Lumshe idanu ta yi.
"Allah Yasa mun samu ƙaruwa."
Ta harareshi da wasa kawai ta juya
ta bude kofar, ya biyo bayanta don shi kansa yunwar ke cinsa. Sai da suka kammala ba cikinsu hakkinsa kafin kuma ya miƙe ya shiga
ɓ
angaren Dada. Ramlat dai jikinta ya yi sanyi don har tausayin Hafsat ya kama ta, ta tabbatar yau kam Hussein ba zai
ɗ
agamata
ƙafa ba.
Aikuwa hukuncin da ya dauka a kanta mai tsauri ne don har makaranta ya ce ta zauna sai ya yi magana sannan ta ci gaba da zuwa, amma fita dai ko nan zuwa farfajiyar gidan ce ya hanata. Ya kuma rantse muddin ta kara gangancin yin waya da Tahe
er sai ya sa
ɓ
a kamanninta. Da wannan bakin cikin ya bar Hafsat ya fice abinsa.
***
NIJAR-KANO
Sun
ɗ
au hanya miƙaƙƙa daga Maradi don dawowa Nijeriya, garin Kano. Zuƙatan kowannensu farin ciki ne marar misaltuwa, duk da irin wata azaba da su ke j
i a tsakanin mazaunansu, hakan bai sa sun kasa yin murnar samun nasara ba. Kowaccensu ta matse kwalin aikin da ta kar
ɓ
o a ƙasan ƙafafu, idan kuwa wuri ne mai gargada, sai su yi maza su riƙe dakyau a hannunsu. Har suka isa Kano tulun nan yana matse da su.
Gidan Hajiya Zeenatu aka soma zuwa, suka rabu da Hajiya Batool direba ya yi gaba da ita. Ma'aikatan na ta kallon Madam din tasu riƙe da kwali, abinda suke ta tunani bai wuce ko meye a cikinsa ba. Ita kuwa tana shiga
ɗ
akin ta samu wuri mai kyau ta ki
llaceshi. Yanzu gaba daya tunaninta shi ne na tafiya Adamawa a gobe-gobennan, don ta fi son komai ta yi shi da gaggawa sai dai kuma yanda ta ke jin bayanta naaa azabar da radadi da ciwo, dole sai ta ji sauƙinsa. Don haka ba ta zauna ba, bandaki ta shiga ta
ha
ɗ
a ruwan
ɗ
umi. Sai dai koda zamanta wani uban ƙara ta saki na azaba. Ranar dai wuni ta yi jiki ba dadi don har da su zazza
ɓ
i. Haka ta samu labari daga Hajiya Batool, ita kam har wani ruwa ta ke fitarwa.
Wasa-wasa zazza
ɓ
i ya tsananta ga Hajiya Zeen
atu, har washegari da ta ke fatan tafiya Adamawa, abin ya gagara. Dakyar ta iya daukar waya ta kira likitanta. Har gidan ya zo ta kira Emma a waya ta ba shi iznin a shigo da shi. Ya karasa har dakinta, ya yi mata allura. Koda wasa ba ta bari ya san
ɗ
aya
ɓ
angaren na ciwonta ba, yana kammalawa ya fice abinsa. Aikuwa wani wahalallen bacci ya yi awon gaba da ita.
Ta fi awa hudu tana bacci, kafin ta farka, ba laifi ba kamar sadda ta kwanta ba, kusan ma babu zazzabin sai uban gumi da ta ke yi. Wayarta ta j
awo, ta bude rututun missedcalls da ta gani na Manajanta mai kula da shagon gwal-gwalanta. Kafin ta gama shanye mamakin, wani kiran ya ƙara shigowa. Ta
ɗ
aga da saurinta.
"Hello! Hajiya, gobara! gobara ta cinye shaguna har da namu! Ga wuta har yanzu an
kasa tsayar da ita!"
Daga jin yanda ya ke zancen a matukar rikice ya ke don ba laifi shima yakan ha
ɗ
a da nasa jarin ya juya. Wani irin miƙewa tsaye da Hajiya Zeenatu ta yi, sai ga ta a kan ƙafafunta, jikinta ko'ina ya
ɗ
auki rawa, shi kenan dukiyar da
ta ke taƙama da shi yanzun ka
ɗ
ai a duniya.
"Me ka ke cewa Bala? Me kake nufi wai?!"
Inaa! babu kwakkwarar amsa, tana ta hello amma kamar babu service ga kuma hayaniyar jama'a ta cika wurin. Ai ko mayafi ba ta tsaya
ɗ
auka ba, mukullin motarta ka
wai ta
ɗ
auka ta fito hankali tashe. Ma'aikatan na ganinta suka nufota.
"Hajiya lafiya?"
"Ba za ku gane ba! Yi sauri budemin gate! Gobara a sabon gari!"
Hakan da ta fada duk sai suka fahimci inda zancen ya dosa tunda duk sun sani tana da shag
o a sabon gari, wato dai an samu matsala, da sauri Emma ya karbi mukullin ya ce ta bari ya kai ta ba ta da nutsuwar yin tuƙi. Ba musu ta miƙa masa jiki na rawa ta koma mazaunin kusa da direba. A hanya kamar za ta yi tsuntsuwa, duk irin gudun da Emma ke sha
rarawa ba ta gani. Tuni ta nemi ciwo ta rasa.
Cunkoson ababen hawa da na yan sanda har ma da motocin kashe gobara, ya sa dole Emma sai wuri ya samu ya ajiye motar suka karasa da kafa. Hajiya Zeenatu na ganin yanda shagon ya ƙone ƙurmus babu abinda ya
bari kawai sai ta fa
ɗ
i yanke jiki ta fa
ɗ
i. Nan fa mata da maza aka yi kanta, bakinta tuni ya karkace tana fidda yawu, idanunta kuwa kamar mai harara garke. Emma da ma wasu aka taimaka wurin daukarta zuwa asibiti, Manaja ya yi danasanin kiranta a