Showing 27001 words to 30000 words out of 174924 words

Chapter 10 - Haihuwa-Da-Hanji-Complete

wurin sanyin

tiles na ratsa ta har wani baccin ya

ɗ

auke ta.

Ta makara don tana bude idanunta ta ga haske d

aga Window, da sauri ta miƙe ta shige bayi

tayi saurin yin alwala ta zo ta gabatar da Sallar asuba tana sallame wa bata wani zauna Adu'a

ba don tsoron laifi abincin jiya da ya ƙanƙare saboda sanyi ta cuccusa kan ta fito riƙe da plate

ɗ

in ta nufi inda ta

ga sun fito jiya.

Tsaye bakin kofan kitchen ta ci karo da mommy sanye da hijabi, duk da zuciyarta ya buga haka

ta ƙarasa ta zube a ƙasa tana gaisheta.

"Sannu isasshiya sai yanzu za ki fito? Ban gaya miki aikin ki shara da wanke wanke bane, sai

kar

fe nawa ake shara a gidan ku?"

Murya a sanyaye tace

"Ki yi haƙuri"

Tsaki ta ja kan ta juya cikin kitchen

ɗ

in

"Talatuwa miƙo mata kayan sharar nan da mopping ta ajiye su chan baya don bana son

kallonta gangar abincin da yarana za su ci ban san me za

ta iya jefawa ciki ba ko jini ko tsoka"

Abubuwan sharan wata dattijuwar ta fito mata da su, ta kar

ɓ

a ta fara share parlorn zuwa dining

area daga nan bayan ta gama ta shiga mopping da goge-goge aiki ba baƙonta bane don

wannan a wurinta mai sauki ne sossa

i ma, haka zagi ko hantara duk ta riga da ta saba sai dai

ba rayuwar da take fata tayi ba kenan, ba rayuwar da take buri ba kenan tana so ta ga tana

karatu tana so ta ga tana hulda da mutane kaman kowani dan Adam, tana so taga ana hira da

dariya da ita

kaman yadda ta samu gidan Aunty zee, sai dai da kaman wuya wai guguwa da

auren nesa.

A gefe ta tsaya tana kallon Talatuwa dake ta aikin shirya abincin mutanen gidan bisa dining

bayan ta gama ta dubi Afeefah tace mata

"Ki zuba turarukan wuta 'yan dai-

dai a cikin wanchan abin ki kunna" ta ƙarasa tana nuna mata

burner, show glass

ɗ

in ta tafi a hankali cikin natsuwa ta bu

ɗ

e ta

ɗ

auko ta saka ta kunna yadda

aka gaya mata ta koma bakin kitchen

ɗ

in ta tsaya tana cewa Talatuwa ta gama..

"Akwai abincin ki na

saka miki a plate

ɗ

inki ki

ɗ

auka kije ki ci sai yaran sun gama karyawa tass

sun wuce makaranta ake wanke-wanke"

Da to ta amsa kan ta

ɗ

auka ta fice, a hanya ta gamu da Ishaq so take ta gaishe shi amma

kaman walƙiya haka ya wuce ta, bata damu ba ta shige



ɗ

akin da yake da sunan nata ta rufo

kofan.

Ba za ta ce rayuwa a gidan yayi mata tsanani ba, saboda kwata kwata aikinta bashi da yawan

da zai dameta, tana idar da Sallar asuba take zuwa tayi share share da su goge goge ta

ɗ

auko

abincinta daga nan ta

tafi, sai wuraren sha

ɗ

aya take komawa dining ta tattaro duk abubuwan

da suka

ɓ

ata na karyawan ta fitar waje ta wanke ta kawo bakin kitchen ta ƙira talatuwa ta

shigar, lokacin ita kuma Talatu za ta fiddo mata da abubuwan da ta bata na rana za taje ta tar

a

su wurin wanke wanken ta rufe ta

ɗ

auki abincin ranar ta ta tafi, sai bayan la'asar za ta fito tayi

wanke-wanken haka na dare sai wuraren takwas tara. Ba Ta da abokin hira don talatuwa

tsakaninsu ki yi kaza ne kar ki yi kaza ita kuma amsar ta

ɗ

aya a ko

mai to.

Su iliya gudunta suke bata sani ba ko sun samu labarin ita

ɗ

in annoba ce oho, bayan Hajiya da

suka gamu sau

ɗ

aya 'yan mata ukun ko ganinsu bata sake yi ba, kaman yadda bata sake saka

saleem a idanunta ba tun ranar da ya kawo ta zuwa yau da tak

e neman sati uku.

Bata sani ba shin rayuwar zai cigaba da tafiya a haka ne ko zai sauya? Shikenan ta sallamar da

burin ta na yin karatu kenan?Shikenan ta tabbata Mayyar za ta ci gaba da rayuwa ita ka

ɗ

ai

tamkar a fursuna kenan? Bata da mai bata amsa.

Da misalin ƙarfe biyu na dare chan cikin baccinta ta ji kaman ana buga mata ƙofa, a

ɗ

an tsorace

ta farka sai ta ji ana ambaton sunanta

"Afeefah! Afeefah!!"

Tun ranar da ta sanya kafafunta cikin gidan yau ne karo na farko da ta ji sunanta na fita a bakin

wani hakan ya sake razana ta, da ta kasa kunne kuma sai ta ji kaman Muryar salim a maimakon

ta ji sauƙi sai ta ji tsoro ya sake dabaibaye ta. Me yake yi a kofar

ɗ

akin ta da wannan tsohon

daren? Ashe bai ma manta da ita ba yadda tayi tunani?

Miƙewa tay

i ta nufi kofan wani zuciyar na cewa idan kuma hajiyarshi ta ganshi fa? Allah ya isa

fa zata mishi sanadiyarta, sai ta girgiza kai tana dakatawa.

"Afeefah saƙo zan baki ki bu

ɗ

e don Allah, na san kina jina please bu

ɗ

e ba zan jima ba"

A hankali yayi mag

anan amma ta ji shi tsaff kasancewar dare ne, ta gya

ɗ

a kai tana ba zuciyarta

tabbacin saƙo kawai zai bata ya juya ba wani abu bane, da sauri ta je ta bu

ɗ

e kofan sai suka

tsaya chakk idanunshi cikin nata yana ƙare mata kallo kusan seconds biyar bai ce kom

ai ba sai

ita ce tayi ƙarfin halin

ɗ

auke idanunta daga kanshi ta

ɗ

an duka ta ce

"Ina kwana Ya salim?"

Ɗ

auke idanunshi yayi ya lumshe su ka

ɗ

an ya saki ajiyar zuciya mai dan nauyi, matsota yayi

sossai ta matsa baya tana kallonshi da manyan idanunta, ya l

eƙa

ɗ

akin ka

ɗ

an kan ya dawo

baya, time ya kalla inda seconds ke reading, babbar leda jumbo dake hannunshi ya ajiye mata

don baya so ya shiga

ɗ

akin nata ba da wannan dare ba, kai ko da rana ne ma baya jin zai iya

kebewa da ita inuwa guda ko don addini da

ya haramta hakan.

"Ki kula sossai za mu yi magana"

Yana kai nan ya juya ya fice, ta bishi da kallo har ya

ɓ

ace mata kan ta runtse idanunta tana

kokarin mayar da kwallarta ta tura kofar ta rufe, ledan da ya fi ƙarfinta ta shiga ja har gaban

katifa ta b

arshi nan ba tare da ta bu

ɗ

e ba tayi kwanciyar ta, sai dai duk yadda ta so baccin ya

sake

ɗ

aukar ta baccin ya ƙi zuwa, tuni ta bu

ɗ

e idanunta ledar ta janyo gabanta ta shiga bu

ɗ

ewa

a hankali.

Da wani bargo mai taushi ta fara cin karo kaman ya san tana

matuƙar bukatar bargon don tana

shan wahalar sanyi da aka fara shiga, gashi bayin ta babu ruwan zafi wani lokacin hatta alwala

da kyar take iya yi, wanka kam ba'a magana in dai tana so tayi sai ta bar ruwan a rana wuraren

sha biyu zuwa karfe biyu nan ma

da kyar za ta watsa bata gama tunanin ba ta ci karo da kwalin

heater, irin wanda ake maƙalawa jikin bokiti

ɗ

in nan a kunna ta

ɗ

ora shi kan bargon tana

ɗ

an

murmushi, ta sake mayar da hannunta ciki ta zaro hijabai ninkakku har kala hu

ɗ

u kuma duk za

su iy

a kai mata ƙasa Brown, Ash, purple da onion colour su ma gefe ta ajiye su, ta sake mayar

da hannu ciki ta zaro kananun catons na biscuit da wasu small chops dai waenda za su dan

kwana biyu basu lalace ba daban daban masu

ɗ

an yawa, har da su five Alive ka

nanu catons

uku. Ganin abubuwan dake ciki sun kare ta

ɗ

aga ledan domin matsarwa don ta sake kallon

sayyayarta sai taji da

ɗ

an motsi a ciki, ta bu

ɗ

e gaba

ɗ

aya ta ci karo da ƙaramin kwali jikinshi da

zanen waya, bu

ɗ

ewa ta yi ta ci karo da karamar Villion m

ai kyau da tsari Dukda keypad ne

amma sossai ya mata kyau, fuskar wayan ne yayi haske alamun a silent yake saƙon akwati na

SMS ya bayyana tare da sunan.

"Saleemullah"

Sai ta saki murmushi karo na farko ta bu

ɗ

e saƙon.

"Ba ki yi bacci ba?"

Numfashi t

a sauƙe kan ta shiga reply don ta iya sossai a wayan Aunty zee da ma wasu 'yan ajin

su na islamiyya lokacin da take zuwa makaranta ta amsa da

"Eh, Na gode sossai da saƙon ka duk abinda ka saka a ciki kaman ka san ina da buƙatar su"

Bata ajiye wayan ba t

a ƙurawa screen

ɗ

in ido chan sai ga reply

ɗ

in shi.

"Na kasa samun natsuwa da tunaninki zuciyata ita ta lissafo min duk abin da zuciyarki ta raya

tana da buƙata. Kin ga ko zuciya bata ƙarya"

Ta karanta saƙon ya fi sau abin da ya fi sai ta rasa amsar bash

i, bata motsa ba har wani saƙon

ya sake shigowa daga gareshi.

"Na san baki jin daa

ɗ

in yadda kike zaune amma kiyi haƙuri zan yi iya ƙoƙarina in ga na yi

settling komai, za ki yi karatu har sai kin ce ya isa, ga wayan nan zan dinga yi miki saƙo ki

tabbat

ar kina yi min reply, duk kuma abin da kike so do not hesitate ki sanar da ni zan kawo

miki. Akwai full qur'an a memory

ɗ

in idan kin ji ka

ɗ

aici ki rage lokaci da shi kin ji?"

Tana murmushi a lokaci

ɗ

aya idanunta na zubar da kwalla ta rubuta

"Wallahi s

amun mai irin zuciyarka sai an tona Yayana, na gode na gode Allah ubangiji ya ba ni

ikon saka maka"

Ta tura tana murmushi

"Never mention my dear, ki kwanta kar ki makara da safe byeee"

Ta sake sakin murmushi kan tayi reply

"Allah ya ba mu alkhairi Soj

a Mai kirki"

Dariya yayi daga

ɓ

angaren shi ya rubuta

"Au akwai marasa kirki ne?"

"Eh mana, abokin kan nan Dukda gaskiya ya fa

ɗ

a amma in a wrong way, su ne suke

ɓ

ata muku

suna ake yi muku ku

ɗ

in goro"

Ya girgiza kai yana cigaba da murmushi

"Ryan kenan!

Haka Allah yayi shi, oya sleep Good night"

Bata yi reply ba sai lumshe idanu da tayi razanannun idanunshi da yake zare mata su da sautin

dakakkiyar muryarshi suka dawo mata kaman yanzu yake yi, da sauri ta bu

ɗ

e idanun gabanta

na fa

ɗ

uwa ganin ita ka

ɗ

ai

ce sai ta saki murmushi a hankali ta maimaita sunan

"RYAN" tana lumshe ido.



🖤

Gureenjoh

🖤

HAIHUWA DA HANJI

(A True life story)

Fatima Muhammad Gurin

(Gureenjoh)

Wattpad-Gureenjo6763

Arewabooks-Gureenjoh

*FREE BOOK*

*013*

Sabo ne mai ƙarfi ya shiga tsakanin su ba na wasa ba ta sanadiyar wannan text message da

suke yi wa juna, yana matuƙar wuya ta sanya shi a idanu amma baya yini ya kwana ba tare da

sun

ɗ

auki mintuna masu

ɗ

an dama suna exchanging SMS ba, sai d

ai idan inda yake babu

network, idan kuma tana aiki ne wayan na maƙale a kunnenta tana sauraron karatun alarammar

Prof Isa Ali phantami wato sheikh Abba zari'a yana matuƙar yi mata daa

ɗ

i har ta roki Saleem da

in zai zo ma ya taho mata da alqur'ani ta ci

gaba da koyo don yadda yake karatun daidai da 'yan

koyo.

Yau ya kama Lahadi kusan duk iyalan gidan suna a gida in ka cire salim da rabon shi da gidan

ma an kwana biyu, da zazzabi ta tashi tana jin sanyin hunturu dake busawa na Huda jikinta,

kasancewa

r koyaushe hannunta na ruwa ne ko tana bakin pampo kuma sossai bazarar ya

shiga hakan ya haifar mata da mura da ta

ɗ

an kwana biyu dashi, a maimakon ya ragu ma na

safiyar yau worst ga ciwon kai mai tsanani da take fama da shi ko idanunta bata iya bu

ɗ

ewa d

a

kyau, a hankali kuma karo na ba adadi ta

ɗ

ago su da kyar ta kalli agogo kusan ƙarfe tara na

safe ko shara bata yi ba gashi babu wanda ya leƙo ta bare a yi mata uzuri, lalla

ɓ

a wa tayi ta

miƙe tsaye atishawa na ƙwace mata da ƙarfi ta ja hanci tana dafe

kai haka ta sauƙa ta zari

hijabai har biyu ta sanya saboda yadda a

ɗ

aki ma sanyin ya isheta bare ta fita waje, a hankali

take tafiya har ta isa main parlorn gidan daidai kofar kitchen ta hadu da Talatuwa.

"A'a yanzu kenan zan tafi bi

ɗ

ar ki, na gama ab

in kari tuntuni ina son fitarwa kuma ba'a yi shara

ba. Lafiya kam?"

Ta ja hanci tana

ɗ

an dafe kanta dake juyawa

"Wallahi mura ne ke damu na sossai, kaina kaman an

ɗ

ora min dutse"

"Ashhaa! Sannu Allah ya baki lafiya, idan Hajiya ta fito ki gaya mata za

ta baki magani. Yanzu ki

je ki kwanta bari ni na yi sha...."

"Ta Yi mene? Kwanciya ta zo yi gidan ne da masu gida suna kwance itama tana kwance?"

Sadiqa ta katse musu zancen da gadara.

"Wai na ga bata jin daa..."

"Kinga Talatuwa ba dake nake ba, ki je

ma ki fara shirin

ɗ

orawa friends

ɗ

ina abinci za su shigo

babu jimawa, ki tabbatar abin da za ki dafa zai ishi cin mutane shidda zuwa bakwai... Ke kuma"

Ta juya ga Afeefah

"Ki wuce ki je kiyi aikin ki, kuma ki tabbatar tana gamawa ba'a ajiye mana kwanuk

a a mawanki

kudaje suyi ta bi ba"

Kai Afeefah ta gya

ɗ

a bata ce komai ba ta wuce ta

ɗ

auko kayan sharar ta duƙa don fara wa, da

ƙ

arfi ta runtse ido jin kanta kaman zai biyo ta ya fa

ɗ

o haka ta cigaba da aikin cikin dauriya irin

nata, Sadiqa dake tsaye tan

a danna waya rashin maganan yarinyar ke matukar bata haushi ta

ja doguwar tsaki kan ta juya fuuu tayi

ɗ

akinta.

Afeefah ta gama sharan tana mopping kenan ta ji zuban kaya bisa saman kanta, baya baya tayi

Allah ya taimaketa ta dafe jikin dining table, t

a

ɗ

ago rinannun idanunta ta zubawa Samha da ta

watso mata kayan...

"Ni ki daina kallona, kurwata kurrr... Wa ma ya sani ko naman wanda ya fi ƙarfin ki kika ci ya

tsaya miki a wuya. Ki gama abin da kike ki wanke min kayannan sameera ta aiki Ishaq kuma in

a

da bukatarsu babu jimawa".

Bata jira amsar Afeefah ba ta wuce zuwa

ɗ

akin Sadiqa, dukkansu biyu suna zaune ne Samha

ta isa tace.

"Allah da gaskiyar ki Aunty sadiqa yarinyar nan ta samu wuri har wani iyayi take kaman ta Allah,

muka cigaba da zuba mata

ido babu wanda ya san me gaba za ta haifar kin ga har wani fresh

tayi ta kara kyau"

Sameera tace

"Ni na fi tausayin Yaya Salim don daga ganin yarinyar nan wallahi green snake ce, bana

tunanin idan da Mommy bata

ɗ

auki matakin da ta

ɗ

auka kanshi ba zai

rayu har yau, gwara mu

kasheta da aiki ta yadda zata gaji ta gudu"

Sadiqa tace

"Toh ai yanzu sai mu ci

ɗ

amarar hakan don na ga mommy ta fara mance zancenta, kin ga

idanunta kuwa? Wlh muddin yarinyar nan ta samu rana ba karamin shanya za ta yi ba".

Suk

a cigaba da tattaunawa akan Afeefah da idan an matse su ba za su iya fa

ɗ

an laifinta guda a

gare su ba amma da yake amfani da zancen mutane ya riga ya zama jinin

ɗ

an Adam sai ya

zamana kawai da gaske Mayya ce a gare su kuma idan bata bar gidan ba za ta iy

a raba

ɗ

ayan

su da rayuwarshi, haka kuma duk wanda ya nuna mata tausayi to fa shi za ta fara lamushewa.

Zaune yake cikin mota da alama abu yake dubawa don hankalinshi duka ya tattaru ne ga

wayan hannunshi, sanye yake da wani grey trouser mai taushi ya

ha

ɗ

a ta da cream Color shirt

da yafi yanayi da gashin mage tsabar taushinsa, high neck ce wuyan don idan da zai ja daga

sama zai iya rufe har hancinshi da rigar, Dukda wani irin sanyi da hazo da ya cike sararin

samaniya motar dake kunne cike take da sa

ssanyar iskar Ac ya ha

ɗ

u da ni'imtacciyar kamshin

shi da ma flavours da yake amfani da su na motan suka ba da wani kamshi na musamman.

A hankali sautin waƙan Alex Warren ta ordinary ke tashi, tsaki ya ja a karo na barkatai a ranshi

yake shirin fara masi

fa don baya ƙaunar bata lokaci sai ga wayanshi ya shiga ƙira, Bluetooth na

kunnenshi ya

ɗ

an danna.

"Allah Saleem zan yi tafiyata ka san na tsani

ɓ

ata lokaci"

Duk da a hankali yayi maganan alamun muryarshi ya nuna ya hasala kuma tabbas zai iya tafiya

ɗ

in don saleem ya shiga masa lokacinsa.

"Afuwan mutumina wallahi sai yanzu na tuna inda papers

ɗ

in nan suke, suna

ɗ

akina kuma

kyakyawar

ɓ

oyo na musu babu wanda zai san inda suke ban zaci boss zai tambaya bane da na

taho da su, please help me ka je ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login