Showing 69001 words to 72000 words out of 259716 words

Chapter 24 - MANNUBIYA COMPLETE

Unknown   

01 Sep 2026

90

/>
Yayi mata tambayar yana murmushi

Nan ma duk shiru sukayi dan dama itace me d’an baki to kuma Najeeb ya sako baki shiyasa ta ja tayi gumm!

Ganin suna b’ata masa lokaci ne ya sanya Yashjub dag’owa ya

kalli Munirat yace”Munira bani acc number d’in ki”

Dariya sosai Najeeb da Yassir sukayi.

Cikin nutsuwa ta karanto account number

Yashjub yana shirin turawa

Najeeb ya ce masa” wait mana!ba kaara?bari inyi ai wannan

aikin mu ne ba naka ba..”

Dama Munirat ta yi expecting kud’i ma su nauyi amman bata yi tunanin har 1.5M ba.

Murmushi tayi tace sun gode daganan ta mik’e tace “bara muje mu sauk’o da amaryar,da sauri Yashjub yace

“Wacce amaryar kenan?”ya fad’i hakan yana gyara zama

sannan ya d

’an had’e fuska.

Nan ma dariya suka yi hadda Siyama kafin Najeeb yace

“Kwantar da hankalinka muma mun gaji tafiya zamu yi muje mu huta,sai kuma ya kallesu yace ku saukk’o mu tafi.

“To”kawai Munirat tace daganan suka nufi sama gaba d’ayansu.

……

Nas

iha sosai

Aisha da Yahanasu sukayi mata bayan fitar su Munirat har sai da suka taso mata da tsumin kukanta,sannan Yahanasu ta yi welcoming d’inta warmly into their family.

Dare ya yi sosai sun san idan aka tsaya sallama shima wani b’ata lokacin ne shiya

sa iya su biyun suka yi mata sallama suka d’aukarwa su Jidda jakankunan su,da kyar kuwa ta saki hannun Yahanasu dan sai yanzu wani tsoro da fargaba suka rufeta gashi haka kurum sam sai ta ji bata so a tafi a barta ita kad’ai…..

Aisha ma har da y’ar kwall

ar ta haka nan tana hawaye tana waving d’inta har suka fice suka rufe mata k’ofar d’akin nata,dai dai du Jidda sun k’arasa hawowa dan haka suka yi sari suka suka basu jakankunan su suka ce su wuce gudun kar ma ta ji muryoyinsu ta ce za ta fito……..MANNUBIYA



(Book 2)

Page 20

Na

Humayrah Bulama

Mikiya Writers Association.

Tun lokacin da aka faara siyan baki dama Siyama ta turawa Ya Musbah message,shiyasa dai dai sun hau sama kenan Ya Nafi’u ya kira Aisha ya ce”su sa

uk’kk’o sun zo”

Sun so yi wa Manubiya sallama amman Aisha ta hanasu ta damk’a musu jakunkunan su tace su tafi…hakanan suka je suka yiwa Yash sallama tare da fatan alkhairi suka wuce.

Yahanasu ce ta d’auki Munirat a motarta dan ita bata fito da tata ba,

suma suka wuce….Yassir ma sallama kawai ya yi masa ya wuce.

Najeeb ne sai da ya d’an tsaya ya yi masa y’ar guntuwar nasihar rik’e alkawari da amana kafin shima ya yi masa sallama ya wuce Yash d’in yana ta godiya.

Sai da ya ga fitar Najeeb d’in tukunn

a k’arasa cikin motarsa ya dauki duk abubuwan da ya sissiya ya wuce cikin gidan,yana shiga ya maida main door d’in ya rufe yana mai sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya…kamar a mafarki haka yake ji wai yau shine Angon Manubiya!

Alhamdulillah

Alhamdulill

ah

ya yi ta maimaitawa kafin ya durk’usa ya sa goshinsa a k’asa ya yi godiya ma Ubangiji

Subahanahu wata a la!.

Kitchen ya nufa ya harhad’a komai da decorations d’in tukunna ya fito ya nufi sama.

Sai da ya fara duba d’ayan d’akin tukunna ya lek’a d

’akin gym d’insa dan dama ya san maybe anan su Aisha za su ce za su jera kayan gadon da suka nace sai sunyi…ai kuwa yana bud’ewa ya hango ta zaune a kan gadon wanda aka shimfid’awa wani had’add’en bedsheet mai tafe da wani k’ayataccen quilt da pillows fari

tas mai tsananin kyau da d’aukar hankali.

Ba kad’an ba ya ga d’akin ya yi masa wani irin masifaffen kyau tashi d’aya ya ji wani irin sanyi da annashuwa sun lullub’esa,gadon kana gani ka san ba mai tsada bane amman kasancewarta a ciki ya sanya ya ga gaba

d’aya kaff gidan babu wajen da ya kai ya wannan a kyau da basa peace of mind.

Sallama ya yi mata kafin ahankali ya fara takawa zuwa inda take…tun kafin ya kaiga k’arasawa ya fara jiyo sheshshek’ar kukan ta…..ba ita ba hatta shi zuwa yanzu heartbeat d’ins

a ya tsananta…itakam dama tun lokacin da ya rufe k’ofar falon ta fara jin inama akwai inda zata je ta b’uya!….

Yadda yake takawa zuwa inda take haka take jin takun nasa kamar a kan k’irjin ta yakeyi,sai da ya zo dai dai kanta tukunna ya ja ya tsaya kafin

a hankali ya durk’usa a gabanta yasa hannu ya yaye hular alkyabbar.

Shiruu kawai ta yi ta lumshe idanunta tare da damk’e hannuwanta guri d’aya wanda hakan ya sake bawa hawayen ta damar sauk’a akan kumatunta,ajiyar zuciya ya sauk’e yana mai jin takaicin

su Yassira yana sake lullub’esa dan ya tabbata har da bak’in cikin abunda sukayi mata ne yasanya tsadadden hawayenta k’in daina zuba,ba zai yi mata maganar ba ba zai sako ta a ciki ba amman idon sa idon su Yassira gobe tabbas sai ya ci uban su!.

A hank

ali ya mik’e ya zauna akan gadon gefenta kusa da ita sosai har cinyarsa tana gogar tata kafin a hankali ya sa hannayenshi biyu ya yi cupping fuskarta tukunna ya

shiga share hawayen nata da tombs d’inshi still yana rik’e da fuskar tata bai cika ba yana ka

llonta yanajin wani sanyi yana ratsasa.

Maimakon kukan ya ragu sai yaga hawayen nata ma k’aruwa sukeyi dan haka

ya janyota jikinsa yayi huggin nata da kyau ta yadda hatta yanayin yadda zuciyarsa take bugawa tana ji.

Kamar zai fashe da kuka ya ce

“Dan Allah ki daina! bana

k’aunar ganin hawayenki,inshaaAllah babu kuka a gidana ba zan baki reason ba da yardar Allah,na dad’e da yi wa kaina alk’awarin ba za ki yi kuka a gidana ba!zan baki dukkan farin ciki da jin dad’i!

kar ki fara karya min alk’a

warina tun yau pls,dan Allah ki daina kuka..”

Jin yadda yake ta had’ata da Allah itakuma ta gagara tsaida hawayen nata ne ya sanya ta d’ago a hankali ta d’aura hannun ta a kan bak’insa ta shiga girgiza masa kai alamun ya yi shiru ya daina rok’onta,at the

same ta samu ta tsaida hawayen nata.

Shirun kuwa ya yi ya shagala da kallonta yana mai shak’ar kamshin da itakanta da kuma d’umi da kamshin da hannun nata sukeyi wanda tashi d’aya ya ji yanayinsa ya fara chanzawa,Itanma dakyar ta iya d’auke idanunta a f

uskarsa ta sunkuyar da kanta k’asa tukunna Ahankali tace”Ina wuni!”tana mai jinta kamar ta fi kowa zama safe a duniyarnan kasancewarta rungume a k’irjinsa.

Murmushi ya yi mai had’e da dariya kafin ya lumshe idanunsa cike da shauk’i yayi kissing tafin hann

unta dake a kan bakinsa.

A hankali ta fara k’okarin zame hannun nata dan tashi d’aya sak’onsa ya dirar mata ya shiga ratsata ta ko Ina.

Ruk’o hannun nata ya yi da sauri kafin ya samu ya bud’e idanunsa da suka fara chanja launi,tukunna yace”Lafiya Alhamdu

lillah amarya ta kuma uwargidana”

Sunkuyar da kanta kawai ta yi

tana murmushi k’asa k’asa….dai dai kunnenta ta ji ya ce”Tunanin me kikeyi ne haka bayan gani a gabanki?”

Ya fad’i hakan cikin d’an turo baki sannan yana mai sake ruk’umk’umeta…

Yanayin

yadda ta ji k’irjinsa ya shiga bugawa fiyeda da ne ya sanya ta d’an d’ago a hankali tace”zan sha ruwa”

Dariya sosai ta basa amman sai ya dake,wata nannuyar ajiyar zuciya ya sauk’e tukunna ya cikata da kyar dan wani shauk’i ne yake jansa….mik’ewa ya yi

ya d’an daidaita kansa tukunna yace”muje!na had’a mana dinner a k’asa”kafin ya juya ya cire hularsa ya ajjiyeta a gefe tukunna ya mik’a mata hannunsa yace”Bismillah”

Ba kayan d’azu bane a jikinsa

amman shima wannan d’in fari ne k’al jamfa yanayin d’inki

n mai masifar kyau.

Ahankali ta mik’e tsaye

ta shiga gyara zaman alkyabbar ta harda sake rufa hular…Murmushi kawai ta ga yayi kafin ya matso ta sosai tukunna ya sa hannu a gaban rigar ya shiga b’alle bottons d’in alkyabbar,sai da yakai

har ciki inda bo

ttons d’in suka tsaya tukunna ya sa hannunsa a bayanta yad’an turota jikinsa kafin ya ja alkyabbar k’asa ta tafi ta fad’i a wajen.

D’inkin lace ne a jikinta…..ba k’aramin tafiya kuwa ta yi da shi ba dan lace d’in da d’inkin da ita kanta gaba d’aya suny

i masifar yin kyau!dama ita Allah ya yi mata sura mai kyau gashi d’inkin an yi sa ne style d’in fitted gown,yayinda d’ankwalinta ya d’an yi baya gashin gaban goshinta da rabin na kanta duk a waje sai

shek’i suke yi…..Shiyasa Yash ya ma kasa magana dan sh

i kam an tashi kansa,bai tab’a ganinta a irin yanayin nan ba bai tab’a samu ya k’are mata kallo kamar haka ba,gashi rigar kusan rabin k’irjin duk a net yake…

Ganin kallon yak’i k’arewa ne yasa ahankali tace”Muje”tana mai jinta gaba d’aya a takure ga wani

kunya da fargaba da suka lulub’eta.

Hannayensa ya sark’e around her waist cikin lumshe idanu da bud’esu yace”Anya dinner d’innan za ta yiu kuwa??na fara ganin dishi dishi wallahi…”

Da sauri ta d’an ja baya sai

kuma tayi gaba ta wuce ta gefen sa da h

anzari tana mai jin yadda k’irjin ta yake dukan uku uku.

Murmushi kawai yayi kafin ya juyo yana wani Irin kallonta tukunna da kyar ya d’aga k’afa ya fara takawa nan inda take tsaye ta juya ta basa baya tana wasa da y’an yatsun hannunta……..

Ya zagaya k’as

ashen duniya daban daban amman zai iya

cewa bai tab’a ganin mace mai kyawun structure kamar Manubiya ba har ma fuska bai tab’a ganin mace mai yanayin irin kyawunta ba….ya san kuma soul d’insu ne ya had’u saboda yanada tabbacin ko da ace ba haka looks d’i

nta suke ba he’ll definitely fall for her…

Tana tsaye ta ji sa a bayanta

kafin ta matsa ta ji ya yi sauri ya d’aura hannunsa akan flat tommy d’inta,kafin ahankali

yace”Seriously na daina jin yunwar”

Dasauri tace”Cikina har ciwo yake min tsabar yun

wa”.

Dariya ta ji yayi wadda har

sai da d’umin numfashinsa ya addabi wuyanta kafin a hankali ya yi kissing wuyan dan yadda d’ankwalin nata ya tunkushe ya zame both daga saman gshinta da kuma k’eyarta ya had’e da ribbon d’inta hakan ba k’aramin kyau yay

i masa ba….a yadda yake tsaye a bayanta

ba k’aramin kyau sajen k’eyarta da bak’ak’irin d’in sumarta suka yi masa ba

He can’t help but to appreciate

shiyasa ya sake sakar mata passionate peck a wajen, ya san zata matsa shiyasa ya yi saurin sake ruk’ota

da kyau da dukkan hannuwansa biyu.

Yadda jikinta ya fara karkarwa shi kansa sai da yayi mamaki…a hankali ya durk’usa ya d’ago k’afafunta ya tallafota ya d’auke ta gabad’yanta in a bridal style wanda hakan ya sanya ta runtse idanunta sannan ta yi saurin

zagaye hannayenta a wuyansa a haka ya nufi k’ofar ya fita da ita gwanin ban sha’awa.

Har suka nufi stairs bai ajjiye taba kuma bashi da niyyar ajjiyetan dan haka tace

“Inada nauyi fa”

Kallon d’an mitsitsin bakin nata yayi da idanunta da suke a lumsh

e har yanzu kafin

yayi murmushi yace

“Ni kuma Inada k’arfi..”

Bai ajjiyetaba sai da suka shiga cikin kitchen tukunna ya ajjiyeta a hankali,da kyar ta d’an zame hannayenta da ta sak’ale wuyansa da su suna masu shak’ar numfashin juna,sai da ta daida

ita tsayuwar ta tukunna ta fara k’ok’arin bud’e idanunta.

Facing juna sukeyi itada shi

shiyasa tana bud’e idon suka had’a ido yana yi mata murmushi kafin yace”I made it for you”

A hankali ta fara juyawa tun kafin ta gama juyawa tayi facing mini dinin

g table d’in

ta fara murmushi ba wani uban

decoration yayi mai yawa ba just simple and elegant amman ya yi masifar tafiya da imaninta…….flower bouquet ne mai asalin kyau a ajjiye a kan dining d’in da card a ciki,sai ballon guda d’aya babba da aka sak’a

le ta sak’k’o kan dining d’in da rose’s masu kyau

zub’e a k’asa da kuma kan dining d’in sai abincn da ya jera a kai drinks da chicken sai

candles da ya kunna y’an kad’an a kan dining tabble d’in.

A hankali ta ji ya yi hugging nata ta baya

kafin yac

e “Hope you like it”

Murmushi tayi ahankali ta jinjina masa kanta alamun ‘yes!’

Ajiyar zuciya ya fesar yace

“Alhamdulillah”

Kafin ya sake kwarin ruk’on da yayi mata yana mai sauk’e ajiyar zuciya a jere a jere.

A hakan suka tsaya kowannen su yayi

shiruu kawai.

Ita ta fara kawo k’arshen shirun sakomakon yadda ta ji yanayin tsayuwar tasu yana shirin chanjawa shiyasa ta d’an muskuta,numfashi ya fesar kafin yace”Oh sorry

Mu je ki ci abincin ko?”

Ahankali ta sa hannu ta fara d’aukar note d’in jikin

flower ta shiga karantawa,ai kuwa har da y’ar kwallarta dan ba kad’an ba kalaman soyayyar da ya rubuta suka shige ta suka ratsata…cikin jan hanci ta juyo tace”Thankyou,I love it and I love you more..”

Wani irin blushing ya shiga yi tukunna suka yi hugging

juna a wajen suna ji kamar su cinye juna dan so,sun jima a haka kafin ya ruk’o hannunta suka k’arasa kan dining table d’in suka zauna…Sam Manu ba ta ji dad’in cin abincin ba kuwa dan a kan cinyarsa ya d’aura ta kuma shi ya dinga bata a baki tana ci yana b

ata labari kala kala

Childhood d’insa da schools d’in da ya yi,sai da ya ga ta d’an sake kuma ta ci sosai

tukunna yace “suje su yi sallah”…..Loma d’aya kawai ya iya yi shikam kuma hakan ma dan ta tilasta masa ne saboda sam shi kam ba zai iya wani cin a

binci ba,ba wai baya jin yunwa bane kawai dai ya riga ya san bakinsa ba zai iya d’aukar taste d’in komai ba a halin yanzu.

Ganin kmar zai yi mata kuka ne yasa ta hak’ura ta tsaya kallon ikon Allah

Babba yana shagwab’a!

Sai da ta rurrufe ragowar abinc

in ta saka a dank’areren fridge d’in kitchen d’in tukunna ta yadda su fita d’in dan har ga

Allah bata so su fitan gashi gaba d’aya kunyar shi ita takeji ma shiyasa taketa k’ak’alo aiki.

Shi kam kallonta kawai yakeyi

yana rik’e da hannunta har ta yi

ta gama.

Ganin yana shirin d’aukarta kamar d’azu ne ya sanya ta fincike hannunta ta fice da sauri tana murmushi…murmushi shima yayi ya

fito a kitchen d’in yana y’ar dariya yace”First position fa nakeyi a race lokacin Ina skul!

Are you sure

zaki iy

a tsere min??”

Yayi mata tambayar yana nufota da d’an sauri

Sai da ta d’an rik’e k’asan gown d’in jikinta tukunna ta d’iba a guje ta yi sama

wanda hakan yasa ya fashe da dariya sosai dan bai yi expecting za ta iya gudu kamar haka ba shiyasa kamar ji

ra yakeyi ya bita shima a guje.

Batasan lokacin da tayi ihu ba

sanda ta juya ta ga har ya kusan kamota saboda

ba kad’an ba taji tsoron yadda ta ga har ya kusa kamotan,dan haka ta k’ara k’arfin gudun nata….saida suka kai cikin bedroom d’inta tukunna

ya samu nasarar cafkota!da sauri tace”Yi hakuri dan Allah”.

Dariya yayi sosai kafin ya d’auketa d’in da bataso….direct ya nufi toilet da ita,sai da suka shiga cikin shower glass tukunna ya ajjiyeta ya kunna gaba daya shower d’in da suke cikin wajen ya da

idaita d’umin ruwan.

Nervousness ne yasanya ta kasa cewa komai ta sunkuyar da kanta k’asa tana jira ya fita

ta samu ta yi wanka dan tana

buk’atar yin wankan….Ahankali taji ya matso ya zare d’ankwalin kanta za ta yi magana yace mata “shhh…”

Har sark

’a da d’ankunne sai da ya cire da ribbon,sai da ta ga

yana shirin cire gown d’in tukunna ta san da gaske fa yake,ba ta gama shiga mamaki da al’ajabi ba sai da ta ji ashe shi wankan ma tare yake so su yi…..da kuka da lallashi ta samu ya kyaleta ya fita

da kyar,sai da ta fito har closet ta zuge glass d’in wajen ta mayar ta rufe tukunna hankalinta ya d’an kwanta ta koma cikin massive bathroom d’in ta rufo k’ofar…. brush ta fara yi da sabon toothbrush d’in da su Aisha suka jera mata

tukunna ta yi taking w

arm bath

cikin nutsuwa da kwanciyar hankali ta d’auro alwalla ta fito.

Ta san Yashjub zai yi fushi amman idan ta fito sakawa k’ofarta key zata yi

sa k’arata da safe dan wallahi wani irin fargaba kunya

da tsoro ne suke adddabarta

sannan sai hauha

wa sukeyi,ita sai yanzu ma ta ga wautarta da bata yi sauri ta bisa ta rufe k’ofar tata ba d’azu sanda ya fita.

Tana wannan tunanin ta fito daga cikin bathroom d’in

d’aure ta d’an guntun towel gashin kanta na d’igar ruwa dan ya riga ya jik’a mata shi tun

d’azu,tana k’arasawa tsakiyar closet d’in suka had’a

ido da shi ta cikin glass d’in sanye cikin jallabiya fara k’all!yana durkushe yana bubbud’e

akwatunan ta yana neman abu

motsin ta ya ji shiyasa ya

d’ago ya kalli wajen ai kuwa suka had’a ido.

Ja ta

yi ta tsaya chak

ta kasa gaba ta kasa baya.

Murmushi kawai ya yi ya d’auki

hijabin nata da yake nema ya mayar da akwatunan ya rufe ya mik’e ya nufi inda take….yadda yaga duk ta diririce sai da ta basa dariya

da tausayi,shiyasa yana zuge glass d’in y

a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login