Showing 12001 words to 15000 words out of 259716 words
Yash d’inta haka yake disga ta.
A bud’e su Jidda suka bar k’ofar
dan a tunanin su shigowa za ta yi
Har manubiya ta d’auke idanunta daga kanta amma
ita Yasmeen din ta kasa,kallonta kawai take yi tana sakewa….sanye take da dark army green din jilbab har k’asa,yanayin yadda ta yi parking gashinta ta d’aure igiyoyin
jilbab d’in ba k’aramin kyau ya k’ara mata ba….…’’Hi Yasmeen’’d’in da sir Najeeb yace mata ne ya dawo da ita daga duniyar k’arewa Manubiya kallo,da sauri ta kawar da kanta ta mayar gareshi kafin dakyar ta samu ta d’an k’ak’alo murmushi tace’’Najeeb,
Ina w
uni!’’
Ta fad’i hakan tana d’an murmushi.
D’an lek’awa ya yi,ya hango Yash suna gaisawa da su Jidda bai ga fuskokinsu ba
dan sun bashi baya ne iyakar
gefen fuskar Manubiya ya samu ya gani.
Juyowa ya yi ya kalleta kafin yace ‘’ya na ganki a bakin
k’ofa?’’ya yi mata tambayar yana tsare ta da idanuwa
Ajiyar zuciya ta sauk’e kafin tace ‘’ko da na zo ma na kusan 20 minutes tukunna da kyar aka bud’e min,ashe madam ce a ciki shiyasa,Itace yayar tamu ko?’’ta yi mishi tambayar tana kallon Manu.
Direc
tion d’in da yaga tana kallo ya kalla tukunna ya d’anyi murmushi ya juya ya kalli Yasmeen d’in sannan yace’’Yeah itace!ba ku gaisa ba ne?mu je cikin mana..’’
Girgiza kai kawai ta yi kafin tace ‘’Yace ma in ban bar nan ba sai ya karya ni,ma gaisa wata r
ana bara in wuce’’
Ta fad’i hakan tana d’an yin gaba sai kuma ta juyo tace ‘’am d’azu na ga miss calls d’inka sorry ina driving ne shine na saka wayar a silent’’
Ajiyar xuciya ya sauk’e kafin yace‘’it’s about Ya’isha!kin dai san halinta.Anyways na g
a kamar kina sauri ki je kawai za mu yi magana anjima’’
‘’Ok’’kawai tace kafin ta juya ta yi gaba….
Shiruu Najeeb ya yi yad’an bita da kallo har ta b’ace ma ganinsa a ransa yana tunanin menene yake damun Yash haka ne,shi shi kad’ai iyayenshi suka hai
fa he always wish inama ace yanada siblings
shiyasa har gobe yake mamakin Yash ya rasa dalilin da yasa baya appreciating gift d’in da Ubangiji ya basa.
Girgiza kai kawai ya yi kafin ya shige cikin d’akin bakinshi d’auke da sallama,ahankali
duk suka
amsa kafin Manubiya ta d’ago cikin girmamawa ta gaidashi
Murmushi yayi yace ‘’Lafiya ya
gida ya mai jiki?’’
‘’Alhamdulillah’’ta ce
daganan ta sunkuyar da kanta
Kusa da Yash ya d’an matsa tukunna yace masa’’Ya jiki?’’
Kamar ba zai amsa
shi ba sai kuma yace ‘’Alhamdulillah,ai
na d’auka ba za ka shigo ba’’
Murmushi Najeeb d’in ya yi
kawai ya girgiza kai kafin ya mayar da idanunsa a kan su Jidda da suka ce masa ‘’ina kwana’’a tare,sai da numfashinsa ya yi sama
sakamakon ido biyu
da sukayi shi da Siyama.Dakyar ya samu ya iya ce musu ‘’lafiya Alhamdulillah’’
sannan ya yi sauri ya d’auke idanunsa daga kan Siyama wadda ita bama ta san yana yi ba dan suna had’a ido ta sunkuyar da kanta.
Manubiya ya kalla kafin yace’’ya na ganku duk
a tsaye?ku zauna mana
Itan ma sistern ki ce?’’
Ta san sun had’u da Jidda ranar a asibiti shiyasa ta fahimci Siyama yake nufi dan haka tace’’Eh,k’anwata ce,cousin
sister’’
Ahankali yace’’MashaaAllah’’
Sai kuna ya sake cewa’’ku zauna mana’’
‘’T
am’’
Jidda tace
daganan suka juya suka nufi sofa ita da Siyama suka zauna
Shi kuma ya zauna a gefen Yash kan gadon.
Manubiya ya sake kalla yace
‘’Amaryar mu ba za ki zauna ba ke??’’
Da sauri Yashjub ya juya ya na mishi wani irin kallo
Dariya
Najeeb yayi kafin yace
‘’Sorry!’’sai kuma ya kalli Manu yace ‘’Amaryar Yashjub shi kad’ai!ki taimaka ki zauna’’
Ahankal ta juya da niyyar zuwa inda su Jidda suke amman sai
ya sa k’afa daidai inda za ta bi ta wuce,dukda k’afar ba ta wani kafeta sosai
ba amma ta fahimci sarai abunda yake nufi
zuwa yanzu ta riga ta san halin Yash ta san ba k’aramin abu bane a wajensa yanzunnan sai ya ja mata ta ji kunya a gaban su Jidda muddin ta k’i yin abunda yake so
shiyasa kawai sai ta nemi waje ta zauna a kujer
ar mai jinya
tana mamakin sa a d’ayan b’angare na zuciyarta kuma
tana mamakin Sir Najeeb
mutumin da da ko kallon kirki baya yi mata daga frowning face sai ciccin magani
amman yanzu wai shine haka kamar zai goyata.
D’an zungurin Yash sir Najeeb d
’in yayi ganin yadda yake kallon Manu
K’asa k’asa yace masa’’kar ka
cinye ta da ido mana..’’
Dariya Yash d’in yayi shima k’asa k’asa kafin kawai ya d’auke kansa daga kan Manubiya ya maida kan Najeeb yace’’wanne munafurcin Yasmeen ta shirga maka d’az
u’’
Shiruu Najeeb yayi yana kallonshi kafin ya mik’e tsaye yace ‘’za mu yi magana dakai anjima sai kuma ya kalli Manu yace’’bari in bawa bak’in mu ruwa’’…tun lokacin da su Siyama suka koma chan gefe suke zauna yake ta so ta juyo ya sake kallonta amman
tak’i
Suna zaune abun su hankalinsu na ga wayar Siyama…ya san hakan bai dace ba bai kamata ba sannan ko a ta b’angaren sa shima sam double dating ba ya cikin tsarinsa dad’indad’awa kuma ga Yashjub a wajen abun zai yi kamar cin fuska sannan ya san yana yi
n wani move Yash d’in zai gano sa shiyasa tun d’azu yake ta tausar kansa amman duk yadda ya so sam ya gagara hak’ura….dan haka ya yanke shawarar kai musu ruwa
he don’t mind ya zama waiter as long as zai samu ya kalli fuskarta one more time.
Muryar M
anubiya ce ta katseshi jin tana cewa‘’Laa,a’a fa,yanzu ma za mu tafi su Baba kawai muke jira’’
Da sauri Yash ya kalleta yace
‘’Nooo!dan Allah ki kirasa ki ce ya zauna a gida ba sai ya zo ba ai na warke.’’Sai kuma ya juya ya kalli Najeeb
Yace’’ka ga
abunda ka janyo ko??’’
Murmushi Najeeb yayi kafin yace ‘’Sorry’’tukunna ya kalli Manubiya yace ‘’ki kirasa ki ce ba sai ya zo ba’’.
Da sauri ta d’ago ta kalli Sir Najeeb d’in tace’’Allah in ma nace kar ya zo ma fad’a zai yi min,ya riga ya gama shi
ryawa akan zai zo d’in.’’
Dafe kai Najeeb ya yi yad’an fesar da iska kafin ya zaro waya yace’’okay,bari ni
in gwada yi masa magana’’
Yana gama fad’in haka ya koma chan gefe kare da waya a kunne.
Shiruu suka yi kafin chan Yashjub yace’’yanzu duk
za ku saka ni jin kunya wallahi
Allah yasa ya hak’ura da zuwan’’
Shiruu Manu ta yi kawai ta sunkuyar da kanta k’asa
Turo baki yayi ya b’ata rai tukunna yace’’yanzunnan a
gaban idona kika gama eye contact da Najeeb,ni kuma kin wani sunkuyar da ka
i k’asa’’.
Tana shirin yin magana
Sir Najeeb ya dawo ya ce
‘’ai suna bakin gate ma’’
‘’Innalillahi!
Najeeb ka kashe ni’’
Yash ya fad’a kafin ya mik’e tsaye kawai ya na zabgawa Najeeb d’in wata uwar harara.
Bai dad’e da mik’ewa ba
su Baba
suka k’araso
Shi da mai sunan baba da ya Nafi’u da ya Musbah da Muhsin waenda suka had’u da su a hanya,ba k’aramin dad’i Manubiya ta ji ba ganin yadda Yash ya gaida Baba cikin tsananin girmamawa.
Da kulawa Baba
ya amsa yana mai tambayarsa ya jiki dag
anan ya yi mishi jaje
da adduar Allah ya kare gaba
kafin ya masa gaisuwa.
Daganan suka gaisa da su Musbah suma suka yi masa
kamar yadda Baba ya masa.
Yash ya dad’e bai had’u da Yaron da ya shiga ransa tashi d’aya kamar Muhsin ba,d’an
sukuti Yar
on so chubby gashi fari tass kalar ajebo no 1
dan in ka kalli Muhsin ba za ka tab’a cewa a wahala ya taso ba,yanayin round face d’in shi irin na Manubiya ga
Yaron da ladabi dan sai da ya d’an durk’usa tukunna ya gaida shi,tashi d’aya Yash ya fara addu
’ar Allah yasa Manu ta Haifa masa irin wannan wai!!ranar bai san ya zai ji ba,zai iya bada komai nasa dan ya samu ya ga wannan rana.
Har kanshi Yash ya d’an shafa yana tsokanarshi da d’an auta
aka yi dariya mai sunan Baba ma yanata tsalle tsallen shi
Yaran sun burge Yashjub kwarai dan yana matuk’ar son yara.
Manubiya ce ta bawa Baba kujera ya zauna ita kuma ta ja su Muhsin suka koma wajen su Jidda,su ya Musbah suka tsaya a tsaye.
Sun d’an jima suna alhini
kafin Baba ya sanar da Yashjub d’
in ‘’ai Daddy ma ya kirasa ya ce yana so za su zo ayi tambaya da abubuwan al’ada
sannan yace d’aurin auren nan da kwana goma za ayi inshaaAllah in an gama daidaita komai.
Yace d’an uwanshi kawai yake jira za su taho daga uk yau
Gobe inshaaAllah za su
zo tare’’.
Tsananin murna da kunya ne suka sanya Yash kasa cewa komai,ya sunkuyar da kanshi kawai ya kasa had’a ido da Baba.
Sir Najeeb ne ya ce Allah ya nuna mana Allah ya tabbatar da alkhairi yasa za ‘ayi damu’’.
A tare gaba d’ayansu suka ce ‘’Am
een’’har Yashjub daganan Baba yace’’Allah ya ci gaba da kareka Allah ya k’ara sauk’i,na ji dad’in ganin jikin naka haka,da aka ce ka yi hatsari na firgita sosai amma ganin ka haka ya kwantar min da hankali Allah ya k’ara lafiya
Allah ya ji k’an driver
d’inka
Ya ci gaba da tsare ka a duk inda kake’’
Cikin tsananin jin dad’i Yash yace’’Ameen ya rabbi na gode sosai Baba’’
Daga haka suka mik’e suka yi masa sallama suka tafi Yash yana ji kamar ya janyo Manubiya ya rik’eta ta ci gaba da zama da shi
…..
Ba su dad’e da tafiya ba likita ya shigo,yana shigowa kuwa Yash ya fara masa mita yana cewa
‘shi dai a sallamesa’,dariya likitan ya yi kafin yace ai na riga na sallameka Yasmeen har ta kira su Daddy ma
allura na zo in yi maka ga kuma discharge
papers ka yi signing sai ka dinga zuwa follow up kuma akai akai’’
sai a sannan Yash ya yi murmushi a ranshi yace ‘Alhamdulillah’’
Dan kamar a k’an k’aya haka yake jinsa.
Sai da aka yi masa allura likita ya sake duba hannun tukunna Yash ya yi signing
papers ya yi wa likitan godiya ya fita.
Bai jima ba ya aiko wata nurse da sabbin magunguna karb’a kawai Yash d’in ya yi ya d’an dudduba kafin ya ajjiye a gefe ya ci gaba da xaman jiran su Daddy.Yana nan zaune boredom ya ishe sa dan haka ya mik’e ya fita
domin ya shak’i fresh air kafin a zo d’aukar sa.
Yana fita waje motar Yassir ta danno kai,dama Yashjub ya san maybe Daddy Yassir d’in zai turo dan yanzu a kaff gidan
kusan shine kad’ai yake zaman banza a yanzu,a take tausayin k’anin nasa ya lullub’e
shi,sam ba shi da wani abun yi
gashi shekarunshi sun kusan kaiwa talatin amma ba shi da wani source of income mai k’arfi,shares d’in shi na companyn Daddy kawai garesa wanda a ko da yaushe yake adduar Allah ya taushi zuciyar Daddy ya sa ya k’arawa Yas
sir wani abun.
A ganinshi ya kamata a k’ara mishi dan bai kamata ace yana namiji wanda anytime from now zai fara tara iyali amman shares d’insa ya kasance dai dai da na mata ba,kuma kullum yana zaman banza.Yasan komai laifin Yassir ne tunda ko company d
’insa ma da hannunsa ya lalata,baya san zuwa aiki wani lokacin sai 11 zai ci uban kwalliya ya je
ko cikakken awa biyu ba zai yi ba haka zai fita ya shiga gari.
Amman no matter what haka za su dage su ci gaba da taimakon sa dan hannunka ba ya tab’a rub’e
wa ka yanke ka yar.
Yana wannan tunanin Yassir ya yi parking a gaban shi ya fito ya zagayo a ranshi yace’’Mutumin da ya kamata in je visiting grave d’insa shine na zo d’auka daga asibitin zan maidashi gida garau!
Anyways I have better plans for you…..’’
Dakyar ya k’ak’alo wani d’an guntun murmushin yak’e
yace’’hi’’
Murmushi shima Yash d’in yayi
Yace ‘’Follow me’’
daganan ya juya.
Binsa ya yi kamr yadda ya buk’ata,suna zuwa cikin d’akin Yashjub ya k’arasa ya d’auko
takardun da suke cikin
jakar computer d’in shi da wani a cikin k’aramin envelope ya
dawo nan kan sofa inda Yassir yake wanda ya nemi waje ya zauna kawai yana binshi da ido .
A tsaye ya tsaya ya mik’a masa takardun,sai da yace’’ungo mana’’
Tukunna Yassir ya janye idanuwans
hi a cikin na Yashjub ya maida kan takardun ya sa hannu ya karb’a ya fara duddubawa.
Tashi d’aya ya fahimci na mene ne sai kuma d’ayan takardun mota ne motar da ya dad’e yana ta yiwa Yash d’in nacin ya siya masa…
Ajiyar zuciya ya sauk’e bayan ya gama d
uddubawa kafin
ya ajjiye takardun a gefenshi ya d’ago ya kalleshi yace ‘’What’s the catch??’’
Although Yashjub dama bai yi expecting Yassir ya huce da wuri ba amman
sam bai ji dad’in yadda ya yi ba dan ko d’igon murna bai gani a fuskar Yassir ba.
K
ud’in da ya kashe ya siyi motar ba wani abu bane a wajenshi amma wahalar da yasha wajen registering da had’a mishi company d’in nan
ba kad’an bace.Ganin ransa yana shirin b’aci ne yasa yayi saurin cewa ‘’Auxubillahi’’a cikin ranshi
sannan ya fesar da i
ska ya
mayar da hankalinshi ga Yassir wanda ya tsareshi da dara daran idanuwanshi tun d’azu,cikin sigar lallashi yace
‘’I was wrong Yassir sorry,amman fa still stay away from that girl saboda yanzu haka Daddy ya na zargin ita take kai kanta gareka ne,k
ar ka
shiga tsakaninsu abun ba zai yi kyau ba,idan kuma ka san son ta kakeyi tsakani da Allah
to ka yi magana a aura maka ita
Munada yarinya mai shekaru 17 a gida inda ace ita taga abunda ni nagani ranar a kai da Munirat mai kake tunani?..
anyways
ya riga ya wuce ka yi
laifi pls ka gyara nima kuma na yi laifi
I’m sorry.
Company d’in na yi maka ne saboda inaso inga kaima ka tsaya da k’afafunka,dukda kana b’oyewa but na riga na san abunda yake faruwa a
building d’inka,pls Yassir
Put all your
hard work into this new one yakamata ka farka ka fara abunda zai fishsheka.
Sannan motar na siya maka ne
As
Peace offering
ka yi hak’uri akan abunda na yi maka that very day ya kamata ace na fahimci ka riga ka girma.’’
Ya k’arashe maganar yana mu
rmushi
Dakyar Yassir ya samu ya k’ak’alo murmushi shima ya mike tsaye
Hugging Yashjub ya yi kafin yace’’na gode’’
Tapping shoulder d’in shi Yashjub d’in yayi tukunna yace’’We’re good right??’’
‘’Of course we are’’
Yassir d’in ya ce daganan ya
cika sa ya sake cewa ‘’na gode’’
Murmushi duk sukayi daga haka suka had’a y’an kayan Yashjub
Yassir ne yakira wata cleaner ta tayashi kai wa mota
Yashjub kuma ya je ya rufe duk wasu bills daganan suka kama hanyar gida.
A motar ma Yashjub hira yay
i ta jan Yassir da shi,yana basa
ideas da yadda zai janyo mutane da yadda abubuwa suke da yadda zai fi mishi sauk’in samun income.
A fuska kam ba laifi
Yassir yayi iyakar bakin k’ok’arin shi dan sam bai bari Yashjub ya yi tunanin komai daga gareshi
ba amman fa a zuciyarsa ji yake kamar ya mutu…..saboda bashi da shi
shi talaka ne shitakai har Yashjub ya ci mishi mutunci
kuma yake k’ok’arin bribing d’in shi da mota mai tsada.
Sannan shine ma zai nuna mishi yadda zai yi business da ragowar abubuwa
wato kenan shi an maida shi ma bai san komai ba.
Shi ya kamata ya zama shi yake rabon kud’i da abubuwan alfarma amman kullum akasin haka ake samu,kullum sai dai Yashjub ya basa ya bawa wasu.
This has to end!!!!!
Dukda Daddy shine sila
amman yafijin h
aushin Yash
tunda shike da kud’in yanzu
Ya tabbatar inda ace Daddy
bai ci mishi fuska ya fifita Yash tun farko sama da shi ba to da tuni haka ba ta faru ba!da tuni shima yanzu yanada successful company da estates kamr Yash………
Yasmeen tana isa
gida direct wajen Mommy ta nufa,tsabar
rashin tunani da tsananin son kai su fa ala dole sai dai a tarwatsa maganar auren gaba d’aya kuma a yi musu farrak’u.
Tana zuwa ta zayyane wa Mommy yadda Yash ya
shanyata a bakin k’ofa tanata uban bugu baya
n ya bud’e kuma ya disga ta ya hanata shiga inda yake bayan ya san Manubiya tana ciki kuma tana ji tana ganin komai sannan da k’annen Manubiyan suka zo ya mutunta su ya amsa gaisuwar su da kulawa ita kuma aka barta a tsaye a bakin k’ofa su suka shige ciki
Kamar zata fashe da kuka ta d’aura da cewa ‘’Mommy kinga yadda yarinyar take kallon mutane kuwa ‘akan hanci’mun had’a ido da ita amma ko gaishe ni bata yi ba……MANNUBIYA
(Book 2)
Page 06