Showing 249001 words to 252000 words out of 259716 words
ta kasa yi duk ta gigice……
Shi kansa tausayin Manu d’in ya addabesa kunyar kallon ta ma yakeyi shiyasa kawai yace mata bari ya mayar da Hudan gida(dan zuwa lokacin dare ya yi sosai)
kar
ta d’aga hankalinta zai san abunyi….Huda ta so ya barta tare da Manubiya har a san abunyi amma yace mata “A’a su tafi gidan”
Hakanan ta bata kwarin guiwa,daga haka suka fita suka tafi suka barta ita kad’ai a wajen cikin masifa tsoro da tashin hankali dan
ma a office aka ajjiye ta ba a cell ba.
Ana tafiya da Manu k’awar Kausar ta yi mata waya ta sanar da ita.
A gate su Mommy suka ajjiye Kausar suka wuce…su kansu Mommy da Kausar d’in sun sha jinin jikinsu dan yadda su Yasira suka had’e rai suka k’i kula
su ya ishi ya sanya su fahimci ba su ji dad’in abun ba….
Tana shirin shiga ita da mai aikin ta da jaririnta kawai ta ji an fincikota ta yi baya kamar zata fad’i sai kuma ya mayar da ita ya buga mata kanta da jikin gate d’in yana huci….suna had’a ido da
shi ta kalli mai aikin nata tace”wuce mini ciki da Yaro”
Sai da Yarinyar tagama shiga tukunna ta kallesa tace”Yassir!I wasn’t expecting you!”
Sake matsowa daff da ita ya yi tukunna yace”na ji labarin abunda kika aikata a Yarona saboda baki san ciwon sa b
a ko?
Wallahi wallahi Kausar ko da wasa kika sake yunk’urin cutar mini da Yaro to ba zaki sake ganinsa ba! Mahaukaciya kawai!”
Daga haka ya sake bugata da jikin gate d’in har sai da ta yi k’ara tukunna ya juya ya wuce,dan a mugun zuciye yake dama…har yau
Daddy ya ma k’i ya sauraresa duk ya bi Abokan Daddyn yace su yi masa magana ya yi laifi ne a shirya su dan Allah amma dukda haka ko saurarensa Daddyn bai yi ba gashi he’s broke!!!
like totally…..
Motarsa tana barin wajen Kausar ta yi tsaki,a ranta tace
”na dai kusan ya da kwallan mangoro in huta da k’uda!”
Saboda ta gama shawo kan su grenade ta basu 4 million gobe inshaaAllah za su saki videos d’in Yassir polisawa sojoji dss duk sai sun turamawa….
Yassira ce ta sanar da Yahanasu halin da ake ciki!
I
ta kuma Yaha ta sanarwa su Daddy da su Ummi da su Ya Musbah…
Abbakar da Ya Musbah ne suka fara zuwa dan a lokacin suna tare aka kira Ya Musbahn.
Suna shiga suka ganta a zaune ita kad’ai ta yi shiruu ta zabga uban tagumi, waani irin tausayinta ne ya lullu
b’e Abbakar bai san lokacin da. Hawaye ya zubo masa ba!!
Tana d’agowa da ta gansu kawai sai ta fashe da wani irin kuka ta tashi ta k’arasa ta fad’a jikin ya musbah tana kuka abun tausayi fad’i takeyi”na hak’ura da Ya Yash na hak’uba da shi har abada a g
abansa aka tafi da ni amma bai ce komai ba!
Ina sonshi kamar Raina amma wallahi na hak’ura da shi mak’iya ba za su tab’a barinmu tare ba!”
Sosai Abbakar ya ji guilty conscious ya lullub’esa,tunda aka ce masa an kama Manubiya hankalinsa ya tashi dan hak
an baya cikin tsarinsu…
A ransa ya shiga cewa”Tabbas ya biyewa sharrin zuciya ya cutar da wadda yakeso da sunan so…
Tabbas Manu bata yi deserving haka daga garesa ba idan ya ajjiye soyayya a gefe ko dan friendship d’insu sam bai kamata ya yi mata haka ba
….
What was he even thinking? ta ya akayi ya bari shaid’an ya rinjayi zuciyarsa har haka???
Ta ya ya kasa gane Manubiya ta Yash ce ko da ya aureta zuciyarta ba tasa baceba!ba zai tab’a samunta yadda yake so ba sai dai ya wahalar da kansa da ita ya lalata
musu rayuwa da farincikinsu gabad’aya…kallifa yanzu a halin da take a ciki amma cewa takeyi ‘tana son Yash kamar ranta!!!’
How can he be this selfish to the person who stood by him through thick and thin his first sannan kuma last love?!”
Bai yi auni ba
kawai ya ji hawaye sun wanke masa fuska da sauri ya juya ya fita zuciya fall danasani!…….
Kusan duk a tare su Anty Umma Baba Daddy Yaahanasu suka isa wajen har da Duputy Governor saurayin Yahanasu wanda tana gaya masa ya taho…ai kuwa yana saka Baki a
al’amarin aka saki Manu tare da bata hak’uri…..
Sai a lokacin ne kuma Yash suka zo shi da Aslam wanda ya je ya dadd’akosa a event centre d’in (dan kowa ya watse amma shi ya kasa tafiya,yana inda duka barshi)
bayan ya ajjiye Hudan.
Hakanan Aslam ya g
aggaya maasa abunda matar tasa tace…yace masa duk sharri ne gashi gashi Hudan duk ta gaya masa komai ita Kausar ce ta saka d’anta a buhu ita maid d’in bakinsu d’aya sannan jakar Manu babu komai a cikin ta! Huda ta gani.
saka mata sarkar aka yi daga baya y
anzu su fara zuwa idan abu yak’i ci yak’i cinyewa sai su je su d’auko Huda ta bada sheda….
Suna zuwa suka tarar an sake ta suna ma shirin tafiya!
Sai a lokacin Yashjub ya ji kamar ya rufe kansa da kansa da duka!!!
Da mugun kyar ya samu ya d’aga k’afaf
uwansa ya nufe ta yana zuwa dai dai inda take ta juya ta kamo hannun Ya Musbah tace masa”take me home!pls…”
Zai yi magana tace masa”plsss”hawaye suna masu bin k’uncinta
Zasu yi mata musu Daddy yacewa Ya Musbah ya tafi da ita…..dan shi kansa ya ji mugu
n mugun haushi abunda ya ji Manu tana gayawa Yahanasu Yash d’in ya yi mata…ko a wanne irin Hali kake a ciki ai bai kamata ka bari a tafi da matarka a gaban idanunka ba!.
Duk watsewa suka yi aka barshi da Aslam a wajen…sai a lokacin Aslam ya dafa kafad’a
rsa yace”Allah ya kare gaba”
daga haka ya juya ya wuce ya tafi dan tabbas Yashjub yana buk’atar space!…ya san menene damuwa da k’unci shiyasa suna yin ido biyu tun d’azu ya fahimci Yash yana cikin masifa..dan haka ya tafi yana mai yi masa addu’ar Ubangiji
ya yi masa maganin damuwarsa……
Shi Yash bai ma lura da Abbakar ba sai da aka gama watsewa chan ya hangesa a zaune ya yi shiruu ya yi tagumi..kafesa kawai ya yi da idanuwa suna had’a idanu ya mik’e ya nufosa,a zuciye Yashjub shima ya nufi Abbakar d’in
tabbas yau kam ko shi ko Abbakar…..
…..suna zuwa kusa da juna Abbakar ya yi sauri ya durk’usa a gaban Yash ya rik’e k’afafuwansa da hannu bibbiyu ya fashe da kuka…
Da farko Yashjub ya d’auka wani sabon plan d’in Abbakar d’in ne yin hakan,shiyasa a zuciy
e ya fara k’ok’arin wafce k’afarsa sai da ya ji Abbakar d’in yana kuka yana neman yafiyarsa ya na zaiyyano masa dukkannin abunda suka yi shi da su Yasira da Kausar tukunna ya fahimci nadama ce ta zowa Abbakar d’in dan haka zuciyarsa ta d’anyi sanyi jikinsa
ma haka…..
Babu abunda Abbakar ya b’oye bai gaywa Yashjub ba ya kuma nuna masa proof a wayarsa sannan ya gayamsa yadda suka yi da Manu d’azu komai ya fad’a tun daga farko har zuwa k’arshe…
Dare ya yi sosai amma hakanan Yash ya tisa k’eyar Abbakar suka
nufi gidansu Manu…….
Da farko cewa ta yi bazata sauraresa ba Allah ya so Baba ya ji lokacin dan haka ya fatattake ta zuwa parlourn Bak’i wajensu…ta yi mamakin ganinsa tare da Abbakar amma sai kawai ta zauna ta juya kai ba tare da ta kula ko wannen su ba…
.
Kamar yadda Abbakar ya yi masa bayani hakanan ya maimaita sak a gabanta ya tashi ya kaimata proof ya nuna mata a wayrsa yana kuka ya durk’usa a gabanta yace”dan Allah dan Annabi ta yafe masa!!!…….”
Manubiya ba ta iya kallonsa ba da kyar tana kuka s
osai ta mik’a masa wayarsa tace”ya tashi ya fita ba ta son ganinsa!”
Dama ya yi expecting hakan daga gareta amma ya ji dad’in nauyin da ya sauk’e a kansa dan haka ya mik’e ya yi musu addu’ar Allah ya barsu tare ya kawar da idanun mak’iya daga kansu daga h
aka ya sa kai ya fice….
…..sometimes we have to live with the fact that ba fa komai ne abunda muke so zai zama mallakinmu..asalima wasu lokutan abun kwata kwata ba alkhairi bane a rayuwarmu!sannan idan muka tilasta muka nace akan sai mun samu abunnan to f
a in banda koma baya da dak’ile kai babu abunda muke yiwa rayuwarmu!!
Tabbas inda ace ya raba Manu da Yash da ya tarwatsa rayuwar mutane uku da shi da ita da Yash har gaban abada kuma ba zai tab’a samun farin cikin da yake nema ba.Ya godewa Ubangiji da ya
wayar masa da kai ya nuna masa gaskiya..ya san yana son Manu amma zai yi k’ok’ari ya manta da ita ya yi moving on a rayuwarsa ya nemi farin ciki ya daina mayar da kansa baya yana b’atawa kansa lokaci.
Abbakar yana fita Yash ya mik’e ya k’arasa inda M
anubiya take nan a zaune tana kuka….a hankali ya sa hannu ya dafa ta wanda hakan ya sanya ta juyo da sauri ta fad’a jikinsa ta fashe da wani irin kuka..cikin kukan tace”yanzu ta tabbata ba zan haihu ba kenan??”
Da sauri ya sa hannu ya toshe mata Baki ya
ce”fad’arsu ba fad’an Allah baceba sannan abunda suka yi miki bai isa ya hanaki haihuwa ba sai da izinin Ubangiji..ki kwantar da hankalinki tun a wanchan lokacin na fara shirye shirye akwai Doctor d’in da za ki gani a Berlin anytime from now zai bamu Ap so
on na sani…ki daina kuka Manu na san Ubangiji zai bamu haihuwa InshaaAllah Allah ba zai barmu haka ba..na dad’e da yin believing akan zaki haifa mini Yara inshaaAllah zamu zama parents muma...”
Sosai ya ci gaba da kwantar mata da hankali har sai da ya ga
ta daina kuka hankalinta ya d’an kwanta tukunna ya kyaleta.
Cikin sharar hawaye ta d’ago ta kallesa tace”inaso insan abunda yake damunka tun kwanakin baya..kar ka b’oye mini dan na san kana da damuwa bayan wannan!!”
Shiruu ya yi ya d’an k’ura mata id
o kamar ba zai ce komai ba sai kuma yace”Ya’isha ta rasu!rana d’aya suka rasu ita da Inna..ban san wanne tudu wanne gangare ba amma Mommy ce sila,a jeji ma taje zata binne ta ko sutura ba ta yi mata ba….
kuma har yau bata gayawa kowa ba…
Tun a ranar nake
k’ok’ari nake so in d’auko y’an sanda a tafi da ita amma na gagara kulle mahaifiyata da Hannuna..kuma shirun nan da na yi ni kaina na san ban kyautawa Ya’isha da kaina da kowa ba!!!….”
Kukan da ya ci k’arfinsa ne yasanya sa yin shiruuu…kafin chan yace”Ma
nnubiya na tsorata da lamarin Mommy na firgita sosai Mommy ta firgita ni al’amarin ya gigitani da yawa….”
Yadda yake kuka yana magana ne ya sanya ta rungumesa itama tana kuka kamar ranta zai fita…..
Sun fi awa d’aya a parlourn kafin ta je ta samu Baba Al
lah ya so ta bai yi bacci ba nan tace masa”za su tafi!”
Dare ya yi sosai sosai amma bai Hana ba dan ya ji dad’in shiryawar da suka yi tunda har tazo ta ce zata tafi ya san komai normal dama bayaso ta yi yaji ta zo ta kwana masa a gida….hakanan ya je suka
yi sallama da Yash ya sanya musu albarka..suka wuce gida tare…..:
Washegari da sassafe su Manu suka hau shiri dan za su fita su fara shirye shiryen tafiyar da ta taso musu saboda jiya cikin dare suka yi receiving letter daga babban likitan da zata gan
i a Berlin..zai gansu in the next ten days.
Tun a masallaci ya sanar da Daddy yace masa”Manu tun jiya ya dawo da ita yau kuma zasu fara shirye shiryen tafiya zataje ta ga Doctor”…
suna gama shiri sun fito kenan Yashjub yana reverse kawai suka ga Muni
rat ta kutso kai cikin gidan sanye da baban Hijabi ta yi k’iba sosai fuskarta ta kukkumbura dan da kyar Yash ma ya iya ganeta Manu ce dai tana ganinta ta ganeta.
Fita duk su biyun suka yi suka tsaya suna kallonta har ta k’araso garesu…….
Jiya su Ju
nior basu koma gidansu ba direct daga wajen Manu gidan Daddy suka wuta kawai suka kwana a nan!
Suna zaune da shi da Daddy Yasmeen Yahanasu da Ummi suna breakfast Yash da Manu suka shigo….
Murmushi Daddy ya yi haka itama Ummi da suka gansu
Suna shirin y
in magana Yash ya k’araso cikin parlourn ya ware murya ya shiga kwala kiran “Kausar!!!”
Da mugun k’arfi.MANNUBIYA
(Book 2)
Final Episode.
Na
Humayrah Bulama
Mikiya Writers Association.
Idanunta biyu a lokac
in Yaron ya dameta da kukan yunwa dan rabonsa da abinci tun jiya kafin ta tafi wajen makeup.
Kamar ba zata je ba sai kuma ta mik’e ta nufi k’asan..
Duk mik’ewa su Ummi suka yi suna buk’atar k’arin bayani…tashi d’aya Ummi ta tafi Luu zata fad’i sakamoko
n ganin Munirat da ta yi ta shigo tana hawaye,da sauri Daddy ya yi saurin rik’eta shima ya mayar da hankalinsa ga Munirat cikin kid’ima yace”Munirat!!”
Duk sai a lokacin su Yasmeen suka lura da ita Kausar kuma ta yi turuss ta ja ta tsaya ta gagara k’aras
owa k’asan idanunta kyam!! a kan Munirat….
A zuciye Yash ya k’arasa ya fincikota ya wurgota tsakiyar parlourn wanda sai da ta kai k’asa ta zube tsabar yadda ya yi cilli da ita….cikin tsana da kyama ya k’arasa ya tsaya a gabanta ya ce mata”ina d’anta????
”
Gaba d’aya kowa kansu ya yi dan babu wanda ya fahimci inda Yash d’in ya dosa….
Ganin an zagaye su asirinta yana shirin tonuwa ne ya sanyata ta mik’e cikin in ina tace”Ya Yash D’an wa kuma???ban gane ba..”
Mahaukacin Marin da ya zuba mata sai da ha
ncinta da bakinta suka fashe cikin tsawa yace”Kausar ina d’anta!????”
Dafasa Daddy ya yi jikinsa yana karkarwa yace”Yash me kake magana akai haka ne mai ya faru??
Dai dai nan Hajiya mama da Yadira waenda suka ji ife ifensa suma suka sauk’o k’asan……
Ji
kinsa yana wani irin karkarawa yace”Daddy ka barta ta bani amsa sannan ta yi bayani da bakinta!!
Sai kuma ya kalli Kausar a karo na uku ya daka mata tsawa yace”Kausar ina d’an Munirat???”
Luuu Ummi ta tafi da zube!!saboda dama ita tunda Munirat d’in t
a shigo da ta kalleta ta fahimci kamar haihuwa ta yi kuma sai da Yash d’in ya fara waennan maganganun tukunna kwakwalwarta ta shiga tariyo mata alamomi da dama data gani a tartare da Munirat d’in kafin ta gudu……
Salati duk y’an parlourn suka d’auka dan
suma sun fara d’aukar haske yayinda Kausar ta fashe da kuka ta durk’ushe a wajen tace “wallahi ni bansan mai kake magana a kai ba…..”
Zuwa yanzu Yahanasu da Manu da Munirat sun samu Ummi ta farfad’o dan haka Munirat ta mik’e ta k’arasa inda take ta tsay
a tace”Kausar baki fahimci abunda yake nufi ba?har kin manta yadda kikayi ta kuka kina rok’ata in rufa miki asiri kenan???”
Kallon kallon aka fara yi kafin Daddy ya shiga gaban kausar ya tsaya a gaban Munirat yace”ki yi mana bayani dalla dalla!”
….
Hawa
yenta ta share kafin ta fara magana”Daddy ku yafe mini na biyewa sharrin zuciya da son da nake yiwa Yassir na jefe kaina halakar da nakasa fuskantarku da tabon ya sanya sai da na gudu na bar gidan nan dan ba zan iya facing kowa ba!!
Yassir ya yaudareni da
kalmar so ni kuma na biye masa…haka muka taru da ni da shi muka dinga tafka b’arna har ta kaini ga samun ciki,kuma Likita ya tabbatar mini muddin na yi yink’urin zubarwa to kodai in mutu ko kuma in rasa mahaifata…shiyasa na dawo na samu Yassir dan a lokac
in ma har mun rabu…sai da na dinga kuka a gabansa Ina magiya jinina ya hau
na shiga masifa mai tayin yawa tukunna ya yarda zai taimakeni,hakanan ya kaini wani gida flat mai two bedroom ya zuba mini kayan abinci ya yi gaba yace idan na haihu in kirasa s
ai mu kai Yaron gidan marayu…….
Ban sake ganin Yassir ba sai da cikina ya cika wata na biyar kwatsam suka zo mini da shi da Kausar suka ce min Kausar ta yi b’ari suna buk’atar idan na haihu in bata Yaron a samu a rufawa juna asiri…da farko ban yarda ba da
n ko da Yassir yace za a kai Yaron gidan marayu jinsa kawai nake yi amma na gama tsarawa Ina haihuwa zan bar garin da d’a na mace ko namiji saboda Ina matuk’ar son abuna.
Magiya kuka da kuma nuna mini alfanun yin hakan da yadda za mu taimaki juna da Kausa
r da Yassir suka yi ne ya sanya na chanja ra’ayina na amince idan na haihu Kausar sai ta karb’a ni kuna sai in dawo gida gareku ba tare da kowa ya san abunda ya faru da ni ba in yi rayuwa ta kamar farko.
Tunda na haihu na ji ba zan iya bata d’ana ba….da
mugun kyar na amince bayan Yassir ya lallab’ani amma a jiya da na ji yana waya ana sanar masa abunda Kausar d’in ta yi wa Yarona ya sanya na fahimci bayarda shi a Kausar is the worst thing I can do
dan haka na dawo kawai ku karb’i Yarona ku bani inason a
buna wallahi ba zan iya rabuwa da shi ba ba zan iya bar mata shi ba,daganan ku yafe mini ku yafe min na san na yi muku laifin da ni kaina ba zan iya yafewa kaina ba.”
Cikin