Showing 120001 words to 123000 words out of 259716 words
sannan itama ta bud’e idanunta.
Gaba d’aya fanfunan dake a jikin shower d’in ya ware musu
wanda hakan y
asa ta sauk’e wata k’ak’k’arfar ajiyar zuciya.
Ganin yana shirin fara zuge mata zip d’in rigar tata ne ya sa da sauri ta ce”Dan Allah A’a su Yahanasu fa suna waje!
Idan muka gama wankan ta ya za mu fita??”
Murmushi kawai ya yi yana kallon ta yace”Kar ki
damu kafin mu gama mu fita na san za su fita su
ba za su zauna a d’akin ba.”
Ya fad’i hakan yana sake k’ok’arin ruk’ota yana mai jin wani so da k’auna da kuma tausayin ta suna ratsashi
Add’ua kawai yake yi Allah Ubangiji ya sa tunanin sa ya zamo gask
iya.
Turo baki ta yi ta d’an ja baya da dukkan ragowar k’arfin da take ji kafin tace
‘’A’a ni dai,kuma Allah ka daina d’aukata a gaban su Daddy dan ni yanzu ban san ma ta Ina zan fara kallon su ba”
Shiruu kawai ya yi yana kallon ta yana wani irin m
urmushi
kafin a hanakali ya matsa yace
“Sorry!ki yi hak’uri about
earlier but dan Allah kar ki sake
Har yanzu zuciyata zafi take yi.”
Ta fahimci mai yake nufi dan haka ta had’e rai tace
‘’A tunanin ka na fad’a jikin sa da gangan ne?‘’
Shiru
u yai yana kallon ta dan shi sai yanzu ma ya yi wannan lissafin…a hankali ya fesar da iska ya matso ya yi cupping face nata a cikin tafukan hannunsa sannan yace
‘’Mu bar maganar pls na ji na yi laifi misunderstanding ne I shouldn’t have shouted at you th
at too in public ki yi hak’uri ki yafe wa Babyn ki um…..”
Ya yi maganar yana mai lankwasar da kai.
Cikin d’aura hannayenta a kan nasa tana k’ok’arin kwatar fuskarta tace
‘’ Kai d’in Babba da kai ai ba Baby bane sai dai in kwace mini suna kake son yi
Kalli fa yadda ka fini tsayi”
Murmushi ya yi yana mai farin cikin yadda ta huce nan da nan a hankali yana kallon kyakkyawar fuskarta ta cikin ruwa da yake rushing a ta koina na jikin su yace
‘’Ok,let’s see waye ne Babyn……’’
Kamar yadda ya fa
d’a ko da suka fito da ga wankan ba kowa a d’akin sai akwatunan su.
Murmushi kawai ya yi ya bud’e ya d’auki towel ya cire vail dinta daya rufa ya d’aura kafin Ita ma ya d’aukar mata towel ya nufi toilet d’in.
Kamar za ta fashe da kuka haka ta fito,ita
kam bata san da wanne ido za ta ke kallon y’an gidan ba…d’azu ya d’auke ta yanzu kuma ya sa su Yahansu sun fita sun bar musu d’akin….
Jiri take ji sosai shiyasa ta nemi waje ta zauna a kan gado tana ganin uku uku.
Da kyar da taimakon sa ta shirya cikin
wata English dress har k’asa mai dogon hannu,sama sama ya yi mata drying gashinta ya saka mata hula da ga nan ya durk’usa a gaban ta yace
‘’za mu je asibiti ne ko a kira doctor gida?’’
A hankali tace
‘’Ba na jin dad’i jiri nake yi kuma inaso in kwa
nta”
“Ok” kawai yace
Daga nan ya mik’e ya k’arasa ya d’auko wayar sa ya danna kiran family doctor d’insu…
Suna gama wayar ya koma inda take ya saka ta a jikinsa kafin yace
‘’Me kike so?me kike sha’awar ci in je in nemo miki??”
Girgiza kai kawai
ta yi tana jin zuciyar ta tana tashi
dan sunan abinci kawai da ya ambato gaba d’aya sai ta ji kamar za ta yi amai.
Sake rungumota ya yi tsan tsan kafin yace
‘’Ki fad’i ko menene zan nemo, ba zai yiu ki zauna a haka ba.”
Ahankali tace
‘’Allah ba n
a son cin komai ni dai’’
Yana shirin yin magana wayar sa ta d’auki k’ara..ganin sunan Yahanasu ne yasa ya d’auka ya kara a kunnen sa….
Earlier
Su Yashjub suna wucewa
su Mommy ma suka nufi sama ba tare da b’ata lokaci ba,parlourn ya rage saura Daddy
da Yassir wanda ya ke jin zuciyar sa tana wani irin tafarfasa
Tabbas zargin sa a kan Kausar ya tabbata kenan son Yashjub take yi idan ba haka ba meye na kuka?sannan ta wani wuce sama da gudu!
Shi kuma Yashjub wai shin shi ya fi kowa sa’a a duniya ne
ga mata nan kyakykyawa Allah ya basa ga d’aukaka da success ga farin ciki sannan yanzu kuma har zai haihu dan in ba da kyar ba ya san Manubiya ciki gareta…yanzu idan ta yi ciki yana ji yana gani haka za ta haihu ba tare da ya same ta ba??! sai dai ya samet
a as mama kenan fa..inaa ba zai yiu ba!
bayaga haka ba zai tab’a yarda Yashjub ya sake samun wani farin cikin apart from wanda ya ke a ciki kafin ya mutu ba….
Runtse idanunsa ya yi da k’arfi sakamokon sarawar da kansa ya shiga yi.
Mik’ewar da Daddy ya y
i ne ya dawo da tunanin sa cikin parlourn a hankali ya bud’e idanunsa da suka rine sukai jazur!bai gama dawowa daidai ba Daddyn ya wuce sama ranshi fes yana murna da adduar Allah ya kawo masa first jika d’insa d’an gidan Yashjub lafiya tabbas za‘a ga gata!
.
Daddy yana wucewa su Ummi ma suka fito
Direct sama suka nufa yayinda Munirat ta d’an tsaya dube dube tana ganin wucewar su ta zauna kusa da Yassir.
Da sauri ya mik’e ya kalleta da kyar ya yi mata murmushi yace
‘’Daddy cewa yai in bisa sama, we wi
ll talk later.”
Daga haka ya wuce ya barta zaune a wajen ita kad’ai.
Tsabar tsananin tashin hankali mai tafe da dana sani Munirat ba ta san lokacin da ta fashe da wani Irin kuka ba….
Direct sama side d’in Kausar su Mommy suka nufa…Yasira da Ya’isha ne
suka shige cikin d’akin wajen Kausar d’in suka shiga bata Baki…dukda ba kuka take yi ba amman ajiyar zuciyar da take sauk’ewa ya ishi ya fahimtar da kai tsananin tashin hankalin da take a ciki.
A parlourn Mommy Baba larai Yadira Yusra da Yasmeen suka t
saya dan har ga Allah su Yasmeen bama sa so su had’u da Kausar tsabar tsananin tausayinta da suke ji.
Mommy kam tashin hankali
ne ma ya hanata k'arasawa ciki…itama ta kanta take yi.
Cikin rashin jin dad’i Baba larai ta ja Mommy gefe tace
‘’Khadija
sam kin chanja
gaba d’aya,bari ki ji wallahi ke kike dawo da aiki baya
Ban san mai ya faru mai ya sa yanzu kike kasa danne kanki ba.
Tun da suka tafi na ce miki ki dinga jan Yarinyar nan a jiki a san halin da take ciki a chan amma kin kasa,kamata ya y
i ki dinga kiranta akai akai amma na sha ganin misscalls d’inta ma a wayarki ba ki d’auka ba.
Idan fa an yi abu ba wai zuba ido za ‘a yi a nad’e hannu a jira aiki ya ci ba kai ma sai ka bada gudummawar wayo da kissa tukunna sannan kuma ka shiga jikin mut
un ta yadda za ka fahimci abun ya yi ko akasin haka,amma sam kin kasa!gaba d’aya Ummi da Manubiya sun chanja ki..yanzu ko d’azu da Ummi ta hana Manubiya cin girkin ki ta kwaso ta sama na san kin fahimci zarginki take yi ko?
Sannan itama Manubiyan kalar k
allon da take yi muku da taga kuna nan nan da ita a iyaka yau kawai ai kinsan na mamaki ne ko?.
Ko da ace su Yadira sun yi fushi da su ko fad’a ko wani abun makamancin haka it’s okay amman ke kina yi tashi d’aya komai zai tab’arb’are na gaya miki na gaya
miki amma kun kasa ganewa gaba d’aya kun bari zuciyar ku tana controlling d’in ku
Gashi yanzu in ba da kyar ba Wallahi ciki gareta kuma ban san tayaya akayi hakan ta faru ba.
Kun k’i yarda ku shiga jikin ta balle ku san kalar tsari da addu’o’in da take y
i a samu a san abunyi.Yanzu na tabbatar inda ace kina waya da ita akai akai kuna video call kuna hira da ita sosai da tuni a cikin watanni ukun nan za mu fahimci abunda mukayi bai yi ba kinga da sai a sake sabon shiri da wuri amma sam kun k’i ku bani had’i
n kai kinga kuwa ai dole a yi ta ganin ba daidai ba…
Da kyar Mommy ta shak’i iska ta fesar kafin ta sa hannu ta yafito Yasmeen.
Yasmeen tana k’arasowa ba tare da shakku!thinking twice ko tunanin wani abu ba
Mommy tace”Ki rubutawa Ya’isha allura yanzu
kafin mu sauk’a k’asa..muna sauk’a za mu je ki gwada Manubiya ,idan kika gwada ta kika ga alamun ciki gareta kar ki bari a yi test kowa ya gani a tabbatar kawai ki ce musu ba ta da ciki!,na san ai ba za su fahimta ba,sai ki yi mata allurar da Ya’isha za t
a siyo miki ba tare da kowa ya gane ba!
A had’o allurar da ta ciwon jiki da ta hana amai.
Kin fahimci allurar da nake nufi???”
Ahankali cikin tsananin mutuwar jiki da rashin jin dad’in abunda Mommyn take shirin saka ta ta aikata Yasmeen d’in tace ‘’eh
,Mommy”
sai kuma ta yi shiru kafin ta sake cewa “amma Mommy kina ganin Ya Yash ba zai fahimta ba?besides idan aka yi allurar ai za ta yi miscarriage kuma za‘a gani sannan za ‘a fahimci ciki gareta amma na yi k’arya nace babu.’’
Cikin fushi Mommy tace ‘
’kin fi ni sanin abunda nake yi ne?tunda nace miki haka ayi kawai!mu samu mu fara yin maganin matsalar da ke a gaban mu gadan gadan,next..za mu san abun yi shima’’
Shirun da ta ga Yasmeen d’in ta yi ne yasa cikin tsananin fushi ta sake cewa’’za ki iya k
o ba za ki iya ba!?”
Ahankali Yasmeen ta had’iye wani abu da take jin yana taso mata sannan tace ‘’Mommy!
i took an oath to help people!ba wai in kashe rai ba!,baya ga haka kuma
dukda ban so cikin nan ya kasance a jikin Manubiya ba na so ace a jikin
Kausar yake amma no matter how na tsani Manubiya babyn jikin ta na Ya Yash ne..
Maganar gaskiya Mommy ba zan iya kashe Babyn nan tashi d’aya ba.Inaga in dai abunda kuke so kenan gara kawai a nemo doctor mu biya sa ya yi mata allurar amma ni kam a gaskiya
Mommy ba zan iya kashewa Ya Yash baby tun kafin ya zo duniy…..”
Mahaukacin Marin da Mommy ta d’auke ta da shi ne ya hanata ci gaba da magana.
Cikin tsananin fushi da tashin hankali Mommy tace ‘’dan ubanki ni za ki nunawa jini!,kin bi kin wani hak’ik’ance
Ya Yash!Ya Yash!Ya Yash d’in da bai damu dake ba tun farko sannan ana so a gyara Abu a had’a kanku kafin wata ta tarwatsa shine za ki yi mini wa’azi?ni za ki kunyata Yasmeen ni za ki yiwa taurin Kai???.”
Cikin huci ta fara ja da baya tana cewa
“Shikenan
! na tsame hannuna
daga yau kowa ya yi ta kansa tunda kallon muguwa kika fara yi min’’
Da sauri Yasmeen tace ‘’A’a Mommy ba haka bane dan Allah…’’
Tun kafin ma ta gama magana Mommy ta fice daga d’akin ta banko k’ofa.
Ko gani sosai ba ta yi tsabar ta
shin hankali…tunda take bata tab’a Jin tsana irin ta yau ba.Da kyar ta samu ta k’arasa d’akin ta tana shiga ta fashe da wani irin kuka tana hango failure gadan gadan..
Tabbas Baba Larai ta yi gaskiya dan gashi tun da Manubiya ta shigo a hankali abubuwa su
ke going against her abubuwan da a da suke y’an k’anana a wajenta yanzu gashi suna shirin fin k’arfinta..duk yadda ta yi da Ummi sai ta botsare sam ta kasa ta shiga tsakaninta da Daddy Daddyn kansa da farko kamar sun samu kansa amma yanzu ya burkice ko su
Yasira ba kasafai yake hira da su da Dariya kamar da ba,yanzu kuma gashi y’ar cikinta ta yi going against her!me ya fi wannan bak’in ciki?kuma ta san in ba da kyar ba sai su Yasmeen d’in sun dasa ayar tambaya a kanta duk a ta dalilin mak’urar da Manubiya t
a kai ta. Tabbas sai yanzu ta sake fahimtar Baba larai dan gashi tun da Manubiya ta shigo rayuwar Yash duk abunda ta tsara baya tafiyi mata yadda take so,in banda fitina da b’acin rai da k’alubale babu abunda take fuskanta,a
tak’aice dai a hankali a hank
ali kenan Manubiya sai ta yi mata tumb’ir!!inaaa aikuwa ba zai yiu ba she won’t allow it wallahi sai dai a mutu!.
Mommy tana fita Yasmeen ta kalli Baba larai tace ‘’ Baaba ki yi mata bayani dan Allah”
Da sauri Yasira wadda k’arasowar su yanzu guri
n tace
“Mai ya faru?
Kallon ta ta yi ta kalli Ya’isha kafin ta shiga zaiyyane musu abunda ya faru….
Kamar Ya’isha za ta rufe Yasmeen da duka haka ta shiga surfa ruwan bala’i tana cewa”Ashe baki da lisssafi ban sani ba? Har yaushe kika santa da har za k
i tausaya mata dan wanann ba wai Yashjub kike tausayawa ba ita kike tausayi.
To bari ki ji in gaya miki idan har wanann Yaron ya zo duniya wallahi ko k’ofar gidan wata rana baki isa ki taka ba!,kin ga daganan sai in ga ta k’arshen zumunci da tausayin d’
an d’an uwa!
Ki na gani dai kwanan ta uku tal a cikin gidan amma da muka je korar mu ya yi!
Ki bar ganin wai Daddy ya tsawatar masa yanzu ance mu je anytime wallahi a kwana a tashi watarana Daddyn ma bai isa ya ce komai ba,indai Yarinyar nan ba ta yi wa
je ba to ba mu da kwanciyar hankali a cikin gidan nan
Ke kin san su waye talakawa idan suka samu guri kuwa???
sai ta raba sa da kowa ta handame komai daga ita sai y’ay’an ta
gashi uban dukiyar family karakakaff duk tana hannun sa’’
Cikin son fahimt
ar da ita Yusra ma tace
‘’Yasmeen tunda har ga abunda Mommy tace miki ki yi kawai mana kin fi ta sanin daidai ne?’’
Ahankali Yassira wadda tun d’azu ba ta yi magana ba , ta fesar da iska kafin ta kalli Yasmeen ta ce ‘’ki rubuta za mu je mu siyo yanzu
ni da Ya’isha…abun da Babba ya hango k’arami bai Isa ya hanga ba’’
Cikin rashin jin dad’i Yasmeen d’in tace
‘’Wai me yasa baza ‘a samu mutum d’aya a cikin ku wadda za ta kalli issue d’innan daga point of direction d’ina ba??”
Wani wawan tsaki Ya’is
ha ta ja kafin tace
“Ai dama na riga na sani,na san sai kin yi taurin kan naki da kika saba!
Yasira kawai ki zo mu je zan yi
browsing mu siyo kuma wallahi idan muka kawo dole sai kin yi
dan babu wanda kika Isa ki gwadawa taurin kai anan!.’’
Tana gam
a fad’in haka ta juya ta fice fuuuu zuciyar ta kamar ta b’ullo waje.
Still cikin son fahimtar da su Yasmeen tace
‘’in da ace mun san zamu aikata haka da bamu barta har ta rayu dashi a wata k’asa daban ba
Infact da bamu barta ma ta shigo gidan ba.”
Cikin tarar numfashinta Baba larai tace
“Yasmeen ke shaida ce wanne irin abu ne ba a yi ba amman sai da ta shigo
Y’an uwan ki da mahaifiyar ku sun fiki gaskiya fa….”
Cikin katseta Yasmeen d’in tace”to Baaba sai ku duba ku ga yadda akayi ta fama d
’in amma sai da auren nan ya d’auru shin ba za ku yi lissafin watak’il wannan cikin shine rabon da ke a tsakanin su wanda Ubangiji ya k’addara sai sun yi auren kuma sai ya zo duniya ba??ba za ku yi tunanin mai za ta kasance da mu idan muka dage muka ce sai
cikin ya fita ba??”
Shiruu kawai Baba larai ta yi tana kallon ta.
Ahankali Yasira wadda itama tun farko tsarin bai yi mata ba tace
‘’ Yasmeen ki yi abun da ake so ki yi kawai!!as far as I know Mommy ta fi ki sanin duk waennan abubuwan so definitely
akwai abun da ta hango sannan kuma inaso ki sani duk yadda za ki so Yashjub bai kai yadda za ta so shi da shi da abun da zai Haifa ba,dan haka tun da har kika ji tace haka akwai dalili Babba!
We re suppose to stick together kar kanmu ya fara rabuwa tun a
nan!
mun fi ki yawa dan haka Ina shawartarki da ki yi hak’uri ki yi abunda kowa anan yake so ayi.’’
Shiruu d’akin ya d’auka kafin chan Yasmeen ta sauk’e ajiyar zuciya tukunna ahankali tace”okay!bara in rubbuto”
daga haka ta juya ta fita.
Ahankali
Yasira ta fesar da iska…ta rasa ganin ta inda abunda suke shirin aikatawa ya kasance daidai ya kuma dace ace su yi!
Tabbas itama a cikin zuciyar ta a bayan Yasmeen take d’ari bisa d’ari
Amman kuma akwai abunda Mommy ta hango tabbas!
wannan shine dali
linta na bin bayan Mommyn dan ta san in dai Mommy za ta iya cewa a kashe d’an d’an cikin ta
to tabbas lamarin Yashjub da Manubiya ya wuce tunanin su,ya fi k’arfin iyakar abunda ta gaya musu suka sani.
………..
Bayan kamar 40 minutes,
Su Yashjub suna z
aune har da Yahanasu wadda ta kawo wa Mannubiya tea take sha suka ji ana knocking.
Sai da Yashjub ya kalli wayar sa ya ga likitan bai kira sa ba tukunna ya kalli Yahanasu yace “ta bud’e