Showing 45001 words to 48000 words out of 260401 words
wannan Labarin Nimcyluv
🤘🏼
Ayushercool
🍷
Zee kumurya
💘
*
[9/30, 8:55 PM] Abk: *DARE DA DUHU*
_Brigh pens
✍
️
_
Nimcyluv
Ayushercool
Zee Kumurya
P11
Domin samun complete litattafanmu, ku yi following
ɗ
in wannan accounts
ɗ
in a Arewabooks
https://arewabooks.com/chapter?id=6316f4af434cfeb9e7fe2949
https://arewabooks.com/u/nimcyluv
https://arewabooks.com/book?id=
Elegant online writers
LITTAF
IN DARE DA DUHU, ₦300 NE KACAL, ZA KU TURA TA WANNAN ACCOUNT ƊIN
0116886423 Sulaiman Na'ima s union Bank.
KU TUNTUƁI WANNAN LAMBAR DAN TURA KATIN WAYA NA NAIRA 500 TA WANNAN 09047871750
DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI, KU TUNTUƁE MU AKAN WANNAN LAMBAR 0706306
5780\09047871750
MUNGODE.
Cak ya tsaya kamar wanda aka dasa shi a gurin cikin rashin sanin abun yi, shi kansa ya rud'e balle kuma ita, cikin rawar murya ya ce. "I'm
.so.. sorry Yaya."
Juya masa baya ta yi da sauri tare da ƙanƙame jikinta g
uri guda, kamar za ta yi kuka ta ce. "Salman! I said get out please!"
Bai ce komai ba ya juya ya fice daga
ɗ
akin cikin wani irin yanayi na sanyin jiki.
"Ya dai? Ko wani abu ne ya same ta?" Abbi dake duban sa bayan ya dawo ya zauna, ya fa
ɗ
i haka.
Daidaita nutsuwarsa ya yi ya ce. "Nothing Abbi, tana wanka ne."
Gya
ɗ
a kai Khamal ya yi ya cigaba da latsa wayarsa.
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi jin ƙarar bu
ɗ
e ƙofa tare da fitar shi, kamar mai tsoron wani abu ta juyo a hankali, saurin
ɗ
aukar bra
r ta yi ta saka ta ƙarasa shiryawa, cikin wani hadadden less wanda aka yi masa
ɗ
inkin tea bubu. Ta yi kyau sosai duk da ba wata kwalliya ta yi ba, bayan ta feshe jikinta da tsadaddun turaren da Abbinta yake siyo mata, ta
ɗ
auki medium vail ta yafa sannan ta
fice, bayan ta
ɗ
auki Small handbag
ɗ
inta.
Tunda ta fito Na'ima ta kafe ta da ido wanda hakan yasa ta jin kamar za ta fa
ɗ
i, Salman ma jin ƙamshinta ya
ɗ
ago kansa a hankali yana kallon ta, a ransa yana yaba tsananin kyawun Yaya tasa. Ita kuwa Na'ima baƙi
n ciki ne ya cika mata zuciya, na kyawun da Abra take shi da kuma takaicin yanda Khamal yake siya mata suturu masu kyau da tsada, gami da duk wani abu na kwalliyar ƴa mace. Duk abun da ya gani indai na gayu ne sai ya siyo mata, idan ta yi magana ya ce, ai
ita ƴa mace ƴar kwalliya ce, idan bai siya mata ba wa zai siya mata? Ita ma babu yanda ta iya haka take siya matan saboda gudun kar ya gane har yanzu ba ƙaunar Yarinyar take yi ba.
"Kai Masha Allahu laƙuwwata illabillah, ƴata tafi kowa a kyau da iya
ɗ
au
kar kwalliya, gaskiya sai
ɗ
an Sarki ko
ɗ
an gwamna zan bawa, dan Ƴata mai tsada ce."
Na'ima ta fa
ɗ
i haka cikin murmushin da bai kai zuci ba.
Sai a lokacin Khamal ya
ɗ
ago ya dubi Abra, cikin murmushi ya ce. "To Allah ya kawo mana na gari." Lumshe ido
kawai Salman ya yi ya bu
ɗ
e bai ce komai ba.
"Sannu da hutawa Mami."
"Yawwa Daughter, kun dawo daga islamiyya ina sama ina shiryawa, sai yanzu na sakko, ya makarantar?"
"Alhamdulillah."
Ta fa
ɗ
a cikin siririyar muryarta.
Mayar da duban ta, ta
yi ga Abbinta ta yi masa sannu da gida, ya amsa cikin fara'a sannan ya miƙe ya ce su huce. Abra da ba ta inda za su je ba ta yiwa Mami sallama ta fara fita, ita wannan shiryawar da ta yi da niyyar ta tambayi Abbinta za ta gidansu wata friend
ɗ
inta, dan su
yi totorial akan last paper
ɗ
insu da za su yi ranar Monday ta literature. Amma kasancewar ba ta saba musu ba sai ta hak'ura ta fasa zuwan, tunda Abbi ya ce za su fita.
"Kai kuma lafiya kake ta bin mutane da ido?"
Cewar Na'ima tana duban Salman.
"L
afiya Mami, bari mu wuce sai mun dawo." Ya yi maganar tare da miƙewa ya fice.
Na'ima ta ce. "To Allah ya kiyaye, sai kun dawo
ɗ
in."
"Yaya! Angel."
Salman ya fa
ɗ
a bayan ya fito cikin ƙoƙarin cire moment
ɗ
in
ɗ
azu daga cikin zuciyarsa, na ganin ta n
icked da ya yi.
Abra dake tsaye ta
ɓ
ata fuska ba ta ce komai ba.
Ya ƙaraso ya tsaya a gabanta ya ce, "Kin yi kyau sosai." Tana ware manyan idanunta a kansa ta ce. "Ko? Kai da ba ka gajiya da fa
ɗ
ar haka as always." Ya ce. "Ai hakan ne shi yasa, kullum
fa ƙara kyau kike yi da wani irin fresh kamar sabuwar amarya." Ta ce. "Kai kuma fa? ai kai ma haka Handsome
ɗ
in Mami." Murmurshi ya yi cikin jin da
ɗ
in yabon shi da ta yi. A haka khamal ya fito ya same su suna hira gwanin sha'awa.
Wani ha
ɗɗ
a
ɗ
en gurin sa
yar da snaks da ice_cream dake cikin Nasarawa Khamal ya kai su, ya yi musu order na abin da kowa yake so. A hankali Abra take shan Vanilla ice cream
ɗ
in dake gabanta, duk da ba wannan ne first time da suka saba zuwa irin guraren nan ba, amma duk a takure t
ake jin kanta. Sai gyaggyara mayafinta take ta kasa zama guri
ɗ
aya. Salman dake gefenta yana lura da yanayin da take ciki ya ce. "Ko in baki a baki ne, na ga kamar ƙiwar sha kike yi?" A hankali ya yi maganar yanda Khamal ba zai ji ba.
Tura masa baki ka
wai ta yi ba ta ce komai ba. Murmurshi ya yi ya cigaba da cin meatpie
ɗ
insa, lokaci
ɗ
aya murmushin ya
ɗ
auke daga fuskarsa sakamakon four eyes da suka yi da wani matashin Saurayi da yake pacing
ɗ
insu, wanda ya ƙurawa Abra ido kamar zai lashe ta.
Wata
Uwar harara ya galla masa ya ce. "Yaya tashi ki je Mota ki ƙarasa sha, kafin Abbi ya gama mu wuce." Ya ƙarashe zancen tare da ajiye meatpie
ɗ
in hannunsa, dan ji ya yi gaba-d'aya ya fice masa daga rai.
Da mamaki take duban shi amma ba ta ce komai ba, K
hamal da ya ji abun da Salman ya fa
ɗ
a, ya dube shi ya ce. "Me yasa zaka ce ta tashi?"
"Abbi na ga sai kallon ta ake yi a gurin nan, kar ido ya yi mata yawa ta je ta ƙware."
Ya yi maganar da iya gaskiya. Murmurshi Khamal ya yi, cikin ransa yana jinj
ina al'amarin Salman, yanda yake acting akan Abra sai ka ce shine sama da ita.
"Ki tashi Please." Ya fa
ɗ
a yana narkar da idanunsa a cikin nata.
"Ka fiya takura Faris, mu jira Abbi ya gama mana, sai mu fita gaba-d'aya."
Ɗ
an ƙaramin tsaki ya ja ida
nunsa akan Matashin nan da ya kasa
ɗ
auke idonsa daga kan Abra, wani irin kallo yake wurga masa. Har suka bar gurin mutumin nan bai daina kallon Abra ba, Salman kuwa sai cika yake yana batsewa. Sai da Abbi ya yiwa Mami da su Ammi take away sannan suka tafi.
Suna hanya aka yi Sallar Magriba, hakan yasa Abbi tsayawa a wani Masallaci suka yi Sallah shi da Salman sannan suka wuce.
"Wai kai lafiyarka kuwa kake ta
ɓ
ata rai?"
Abra ta tambayi Salman cikin kulawa, bayan sun fito daga cikin Mota lokacin da suka
ƙarasa gidan Ammi."
"Babu komai, Ni ma kawai a haka na ji ni."
"Ka fiya rigima kai dai"
"Na kai ki?"
"Ka ma fi ni, Ni dai bana son ganin ka a haka, Please ka saki ranka ka ji
ɗ
an ƙanina." Ta ƙarashe maganar cike da shagwab'a.
"Sai kin ce mu
n Yaya gaskiya." Ya yi maganar yana wani shan kunu.
Dariya ta yi ta ce. "Ba zan fa
ɗ
a ba
ɗ
in, Sarkin son girma." Ba ta jira amsar shi ba ta wuce cikin gidan. Murmurshi ya yi tare da shafa sumar kansa ya bi bayanta.
Da sallama suka shiga main parlour
'n gidan, Ammi tana tsaye a dinning area tana yayyankawa Baffa fruits, Hajiya kuwa na kame akan kujera tana jan carbi mai dubu, da alama ba ta jima da idar da Sallah ba dan sanye take cikin Hijabi, ta ƙara tsufa amma har yanzu bakin nan nata yana nan bai m
utu ba.
Cikin fara'a da murnar ganin su Ammi ta amsa musu tare da yi musu sannu da zuwa, Ƴaƴan Shureim guda biyu da suka zo Weekend suka taho da gudu suna fa
ɗ
in. "Oyoyo Yaya da Ya Salman." Abra ta ajiye ledar hannunta ta rungume su a jikinta cikin murmu
rshi. Salman ya shafi kansu ya ce. "Oyoyo ƴaƴan gidan Ammi, kodayaushe aka zo gidan Ammi a gan ku."
Granny dake bin su da kallo ta cikin White medicated glass
ɗ
in dake idonta ta ce. "Su masu zumunci kenan ai, ku kuwa uwarku saboda baƙin hali ba ta barin
ku zuwa, ita ba ta zo ba ku ba ta bar ku kun zo ba." Ta ta
ɓ
e baki ta ce. "Ba ruwana ma dai, lazimi nake yi bazan ce uffan ba sai na gama tunda babu kyau ana yi ana surutu."
Salman ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita, ya ce. "Ai kin
ɓ
ata lazimin tunda kin
riga kin yi maganar, sai dai ki sake daga farko."
"Ka ci kanka, ni ba zan biye maka ba, sunan Allah nake ambata bana wani gar
ɗ
i Khamalu ba ko na wata gar
ɗ
iya Nai'ma ba, ato, a sarara mun a bar ni in yi abuna cikin nutsuwa."
Abra ta ƙaraso cikin pa
rlour'n hannunta riƙe da na Fadeela, Fadil kuma ya
ɗ
auko ledar da ta ajiye, zama ta yi a kusa da Granny ta gaishe ta,
ɗ
aga mata hannu ta yi tana ƙara fito da carbinta daga cikin hijabi tana
ɗ
a
ɗɗ
aga shi, ita a dole a ga lazimi take yi ba za ta yi magana ba.
Murmurshi Abra ta yi ta miƙe ta ƙarasa gurin Ammi ta gaishe ta, Ammi ta rungume ta tare da amsa masa mata. Daga nan ta wuce bedroom
ɗ
in Ammi dan yin Sallah.
Sai wajen goma da wani abu suka bar gidan, kamar kar su tafi saboda yanda ake tarairayar su, d
a yanda suke cin dariyar Granny, har Baffa ma ya sakko anata hirar da shi tare da Khamal wanda ya shigo daga baya, bayan sun gama gaisawa da mai gadi. Granny sai mitar rashin zuwan su gidan akai_akai take yi, idan Khamal ya ce makaranta ce ta sa ba sa zuwa
n sai ta ƙanne ido ta ce. "To ni ina ruwana ma da zuwansu da rashinsa, tunda ba wata tsiyar suke mini ba in sun zo? Sai dai ma su sace mun
ɗ
an tsirena da kilishina, da
ɗ
an Albarkana yake siyo mini ban sani ba." Da za su tafi ta ce kar su tafi su zauna su k
wana, Khamal ya ce gobe Monday akwai school sai dai in an yi hutu za su zo su yi hutunsu a nan insha Allahu. Sai ta tsuke fuska ta ce, "Allah ya raka taki gona."
Abra tana son su je gidansu Ammi sosai, saboda nisha
ɗ
i da farincikin da take tsintar kanta
a ciki, gashi ai ta nan_nan da su ana nuna musu ƙauna da kulawa.
Washegari da sassafe Khamal ya wuce Abuja gurin aiki.
G.Y BULAMA HOSPITAL AND MATERNITY.
A hankali take tafiya cikin sanyin jiki, tana sanye cikin fararen uniform na Nurses.
Ƙ
ofar wani office ta tura a hankali ta shiga bakinta
ɗ
auke da sallama.
Wani baƙin likita dake zaune a mazauninsa shi ka
ɗ
ai a cikin office
ɗ
in, yana operating system ya amsa mata Sallamar ba tare da ya
ɗ
ago ba. Ƙaraso ta yi ta zauna a
ɗ
aya daga cikin
kujerun dake gaban table
ɗ
in.
"Barka da safiya Doctor."
Sai a lokacin ya
ɗ
ago tare da yin murmurshi ya ce. "Kin tashi lafiya Jamila? Ya su Mama?"
"Lafiya ƙalau, na zo ai Sister Basira ta ce mun ka zo kana nema na."
Ya ce, "Eh, me yasa yau bak
i zo akan lokaci ba?"
"Abun hawa ne ban samu da wuri ba."
"Da kin kira ni ai, da na biyo na
ɗ
auke ki."
Yaƙe kawai ta yi ba ta ce komai ba,
ɗ
an ƙura mata ido ya yi na sakanni, cikin kulawa ya ce. "Kamar wani abun yana damun ki Jamila." Numfashi ta
sauke ta ce. "Babu komai Doctor." Ya ce. "Ban yarda ba, ga damuwa nan ƙarara a fuskarki."
Cikin yanayin damuwa ta ce. "Akwai abun da yake damu na, amma bazan iya fa
ɗ
ar shi ba."
"Saboda me? Please Jamila tell me, har kin saka hankalina ya fara tash
i."
"Ba fa wani abu ne, kawai dai ina tsoron yin maganar ne."
"Oh My God! Tsoron me? Ni ne fa? You are free to tell me everything da yake ranki, ko baki yarda da ni ba ne?"
Ɗ
an jim ta yi kamar mai nazari sannan ta ce. "Yardar da na yi da kai ne ya
sa zan fa
ɗ
a maka abun da yake raina, wani abu ne ya da
ɗ
e yana damu na, amma na rasa da wa zan yi sharing
ɗ
insa, Doctor! Abun da yake faruwa a cikin asibitin nan ya yi yawa, zaluncin ya yi yawa, Matar nan da Doctor Bulama ya hana ka, ka duba ta jiya mai naƙ
udar nan da ta matuƙar galabaita akan ba su biya ku
ɗ
in gado ba ta rasu, bayan ƴan'uwanta kuma sun yi fafutuka sun kawo ku
ɗ
in, wallahi jiya da ita na kwana a cikin raina, lokacin da ta zube a cikin reception
ɗ
in nan tana mu taimaka mata kawai nake tunawa, g
a
ɗ
a ya kawo kai zai fito amma ya hana mu, mu taimake ta." Ta ƙarashe maganar kamar za ta yi kuka.
Doctor Lukman ya sauke numfashi ya ce. "In dai Doctor Bulama ne abun da ya fi haka ma zaki ga ya yi, ke baƙuwa ce a asibitin nan shi yasa abun da yake dam
un ki, amma mu mun riga mun saba da irin wa
ɗ
annan abubuwan."
"Gaskiya idan aka cigaba a haka ba zan iya zaman asibitin nan ba Doctor, dan watarana sai zuciyata ta buga, a ce mutum babu abun da ya sani yake bawa muhimmanci a rayuwarsa sai ku
ɗ
i? Ku
ɗ
i abun
banza da zaka mutu ka bar su, a yanda aka san likitoci masu tausayi da jan patients
ɗ
insu a jiki gami da kwantar musu da hankali, amma shi ko ka
ɗ
an bai san hakan ba. Abun da yake bani mamaki kuma yanda har yanzu asibitin nasa yake ƙara ha
ɓ
aka, mutane suke
ta yabon sa suna ƙwararrun likitoci ne a ciki wa
ɗ
anda suka san aikinsu."
Murmurshi Doctor Lukman ya yi ya ce. "Ai komai da iyawa ake yi Jamila, ma'aikatan cikin asibitin nan kawai suka san halin da ake ciki, amma sauran mutane gani suke yi ana yin iyak
ar bakin ƙoƙari dan ganin an kula da mutum da yi masa abun da ya dace. Kuma kar ki manta, shi fa Doctor Bulama indai zaka cika masa ƴaƴan banki to zaka ga aiki yanda ya kamata, zai kula da kai tamkar
ɗ
an cikinsa."
"Kai amma abubuwan nasa sun yi yawa, y
a kiyayi ƙarshen sa, dan ba zai masa kyau ba, matuƙar bai tuba ya daina abun da yake yi ba."
"Ke dai kawai Allah yasa mu dace, amma ana abu a ƙasar nan, gashi shuwagabanninmu babu ruwansu, tunda ba su ko Ƴaƴansu ake yiwa ba, su in dai zaka ba su Haraji
mai tsoka to duk ma abun da zaka yi ka je ka yi."
"Akwai Allah."
Jamila ta fa
ɗ
a cikin rauni da damuwa.
Sha biyu da ƴan mintuna na rasa su Abra suka dawo gida, yau sun yi final exam gaba-d'ayansu.
Na'ima tana zaune a parlour ita da wat
a ƙawarta da ta kawo mata ziyara, suka yi sallama suka shigo, ta amsa musu tana bin Abra da wani wulaƙantaccen kallo, ƙasa ta yi da kanta gabanta na fad'uwa, ta san watan shan wahalarta ya kama tunda Abbi ba ya gari. Cikin girmamawa ta gaishe da baƙuwar ta
re da yiwa Nai'ma sannu da gida, sannan ta wuce
ɗ
akinta. Salman kuwa zama ya yi ya gaishe da baƙuwar tare da fa
ɗ
in. "Mami yau mun gama exam
ɗ
inmu ta third semester Ss 1, ranar Saturday
ɗ
in nan za mu yi speech in Allah ya kai mu. Na'ima ta ce. "Masha Allah,
Allah ya nuna mana ya bayar da sa'a." Ya amsa da Amin sannan ya tashi ya nufi
ɗ
akinsa.
Ƙ
awar Mami mai suna Maryam ta dube ta cike da munafurci ta ce. "Na'ima kar dai ki ce mun har yanzu kina riƙe da wannan Shegiyar yarinyar?"
"To ya zan yi, tunda m
ai gidan ya dage."
"Ta
ɓ
kin ga zaki iya ne, amma da ni ce da tuni ta bar mun gida wallahi, yanda take da kyan nan ai sai ta raba