Showing 30001 words to 33000 words out of 287295 words

Chapter 11 - KURA A RUMBU COMPLETE

magana da dai naji bazan iya jurewa ba se kawai nayi shahada cikin murya ta data ƙara laushi nace

"Anty Bilal ya tafi ne?"

Yanda kasan tana jira na k

uwa tayo kai na tana cewa

"Ki kiyaye ni Halima, ni zaki tambaya Bilal ya tafi ko yana nan ajiyar sa kika bani ko yaya akayi?. Badai bakya tausayin kanki ba da kananun shekarun ki zaki jawa kanki ciwo saboda namiji. Se ki zuba ruwa a ƙasa kisha zaki auri B

ilal autan maza. Badai namiji kika

ɗ

aukaka har kike

neman halaka kanki saboda shi ba Halima? Allah ya bada sa'a" se ta miƙe fuuu tayi waje tana ci gaba da maganganu.

Da kallo na rakata har ta fice ina jin babu da

ɗ

i a raina. Na rasa wace irin ƙiyayya An

ty Labiba take yiwa Bilal. Ban san me ya tsare mata da bata iya

ɓ

oye tsanar da tayi masa a zahiri ba.

A can waje kuwa cike da damuwa Bilal yake zauna, yana so ya koma cikin

ɗ

akin yaga halin da Halima take ciki amma rashin ganin fuska a gurin Anty Labib

a yasa yake zaune a gurin. Da daren jiya Mu'azzam ya kira shi ya sanar masa da Halima bata da lafiya an kwantar da ita a asibiti a yanda yace tana ta kiran sunan sa ne shine Abban su yace a kira shi yazo. Sanda yaje

ɗ

in ya tarar da ita anyi mata allurar ba

cci a hirar su ya tsinci wani abu a dalilin rashin lafiyar tata. Duk se yaji ya tsani kansa, yasan Halima tana son sa shima kuma yana son ta amma kuma ya rasa yanda ze yi dole ya fito ya gaya mata gaskiya. Be yi zaton zata saka abun haka a ranta har ya kwa

ntar da ita ba se dai da ya ci gaba da jan ta yana

ɓ

oye mata har se an kai ga

ɓ

ar da gaskiya zata fito da kanta a ganin sa gara ta sani su taru su nemawa kansu mafita.

Ganin kusan minti talatin shiru Anty Labiba bata leƙo ta kira shi ba ya fara tunanin

ko bacci Haliman ta koma dan yana da yaƙinin ido biyu ba zata gaza neman sa ba tun da tasan yana gurin, tashi yayi yana ƙarfafawa kansa guiwa akan ko me Anty Labiba zata fa

ɗ

a se ya koma

ɗ

akin, yana kai hannu ze bu

ɗ

e ƙofar ta fito, kallo me kama da harara t

a masa ha

ɗ

i da yin tsaki ta ra

ɓ

a shi ta wuce se yaji ransa ya

ɓ

aci. Ta girme shi kuma ƙanwar mahaifiyar Halima ce amma kuma hakan ba shi yake nufin zata ringa wulaƙanta shi kamar wani wanda yazo mata maula ba. Shi badan Halima ba me ma ze ha

ɗ

a shi da ita h

ar ta ringa wulaƙanta shi haka?

Fuska babu walwala ya shiga

ɗ

akin, na

ɗ

aga kai da sauri jin an bu

ɗ

e ƙofa muka ha

ɗ

a ido ban san sanda na miƙe ina sakin murmushi ba ya nufo ni shima yana murmushi yace

"Kin tayar mun da Hankali Halims, me yasa?"

"Sau k

e gani na nayi ƙasa ina wasa da gefen hijabi na ba tare da nace masa komai ba, ganin sa ya bani nutsuwar zuciya ya kuma tabbatar mun yana tare dani ma'ana ya janye wa

ɗ

an can kalaman marasa da

ɗ

i daya fa

ɗ

a mun jiya wai mu haƙura da juna.

"Ki zauna kar ƙafa

fun ki su gaji" ya fa

ɗ

a yana kallo na se na ƙarasa na zauna akan gado har sannan murmushi be bar kan fuskata ba, ya matso da kujera kusa da ni ya zauna yana leƙa fuskata yace

"Ashe haka kike so na ban sani ba Halims?"

Harar wasa na masa ba tare da nace

komai ba, ya sake gyara kijerar da yake a kai ya langwa

ɓ

ar da kai yana kallo na yace

"Ko da nace mu haƙura ƙarya nake yi ni da kaina nasan bazan iya jure rashin ki a tare da ni ba. Tun da kika tafi ni kaina dauriya ce kawai irin ta maza ta sa ba'a kawo n

i an kwantar a gadon Asibiti ba mutuwa ce ka

ɗ

ai zata iya raba ni dake Halims amma muddin ina raye dole zan nemo mafita, ki taya ni da addu'a Allah ya hore mun na fita kunyar ki kafin ranar auren mu albarkacin wannan son da kike mun bazan baki kunya ba".

Bude ƙofar da aka yi ya saka yaja baya daga gare ni muka kalli ƙofar a tare, Abba ne ya shigo tare da Uncle Mudassir Autan su Mamanmu. Cikin jin kunya Bilal ya miƙe daga kujerar da yake zaune yana musu sannu da zuwa,

fuskar Abba babu yabo babu fallasa ya

nufo in da nake se Uncle Mudassir ne ya amsa masa kafin shima ya matso yana mun murmushi na gaishe su ya shiga tambayar jiki na sannan ya

ɗ

auki folder dake kan bedside ya shiga dubawa dake shima likita ne.

"Dr yace zuwa yamma zasu sallame ki tun da bab

u wani abu ko akwai in da yake yi miki ciwo ne yanzun?" Abba ya tambaye ni, se na shafa ciki na da naji yayi ƙara alamar ina da buƙatar cin wani abu na girgiza masa kai a hankali nace

"Babu komai Abba na samu sauƙi".

"Allah ya ƙara afuwa, ki huta. Su Go

ggo Habiba suna hanya ni na hana Mu'azzam ma ya kawo ta tun da safe saboda an ce a barki ki huta yanzun ma ta tayar da rigima ne tun da kuma sallamar ki za'ayi shi yasa nace su zo

ɗ

in kawai" Abba ya sake fa

ɗ

a. Nayi rau rau nace

"Goggo Habiba kuma? To Mama

fa?" Be bani amsa ba ya juya kan Bilal da tun shigowar su yayi shiru kamar ruwa ya cinye shi yace

"Ina ganin zaka iya tafiya ko" se ya kalle ni kafin ya shafa kai ha

ɗ

i da rusunawa yace

"To Abba, Allah ya bata lafiya yasa kaffara ne" Abba da Uncle Mudass

ir suka amsa da amin se ya nufi ƙofa yana waige na.

"Idan ka samu sarari yau ko gobe kazo ina son ganin ka" Abba ya fa

ɗ

a Bilal na dab da fita, take na karanci razanar da Bilal yayi se kuma ya waske yana murmushi yace

"To Abba idan ma yanzu kake son ga

nin nawa se na jira ka a waje"

"Ka same ni a filin sukuwa ƙarfe hu

ɗ

u zuwa biyar na yamma" Abban ya bashi amsa daga nan ya fita bayan ya sake musu sallama zuciyar sa fal zullumin ganin me Abban Halima yake so yayi masa?

Se da akayi sallar magriba muka

bar asibiti saboda wata allura da aka yi mun ƙarfe shida. Na lumshe ido na ina ci gaba da sauraron fa

ɗ

an da Goggo Habi take yi, tun da taje asibitin bakin ta be huta ba har yanzun da muke hanyar komawa gida zagi kalar wanda ta manta ne kawai bata mun ba ha

r tana cewa in da ita ce Labiba bari na zatayi na mutu kawai tun da turbar da na za

ɓ

ar wa kaina kenan to saboda Allah ni na

ɗ

orawa kaina son Bilal ake nufi ko me? Allah da kansa ya ce shi yake sanya ƙauna a zukatan mutane, menene laifi na sabo da nayi so d

omin Allah? Zuciya ce kowa da irin tasa, wani yana

ɗ

aukar abubuwa da sauƙi in da wani yake zafafawa babu kuma wanda za'a ce baya kan daidai.

Naji da

ɗ

i kuma ban ji ba da naga mun wuce gidanmu ba gidan Anty Labiba ba. Allah ya gani haushin ta nake ji sab

oda ita ce silar komai da bata uzzurawa Bilal da tambaya ba ai da komi ba lalace haka ba rashin jin da

ɗ

in komawa gida kuma da naji nasan surutun Goggo Habi tsaf ze iya haifar mun da wani sabon ciwon se dai ba ta tata nake ba tun da nasan bata da ikon sakaw

a ko hanawa a cikin lamarin aure na, kakata ce ta

ɓ

angaren uwa ba uba ba balle naji tsoron zata iya tilasta Abba yayi abin da suke so.

Abin da ya saka jiki na yin sanyi yanda ko kallon banza ban ishi Mama ba balle na arziƙi, haka nan na shige

ɗ

aki na j

iki babu ƙwari ina jin babu da

ɗ

i. Mama da ko ciwon kai nake yi se ta damu bata samun nutsuwa har se taga na warke ita ce zan kwana a asibiti ba taje ta duba ni ba sannan in dawo gida tayi kamar bata san da wanzuwata ba? Ko da yake ba laifin kowa

bane se na

Anty Labiba ita take zugata, se kace ita wani ya mata dole a sanda ta kawo nata mijin da ni ban ma gama tantance yaren sa ba har yau, su ba yarabawa ba ba igala ba haka nan kuma ta aure shi suke zaune shekara goma ba wanda yace mata saboda me se ni zata s

aka a bakin duniya ta cusawa kowa tsanar wanda nake so.

Da daddare gurin ƙarfe sha

ɗ

aya yunwa ta matsa mun dole na katse wayar da muke yi da Bilal na fito neman abin da zan ci. Tun ƙarfe tara muke waya, yau

ɗ

in ya dawo asalin Bilal

ɗ

ina me so na da tat

talin farin ciki na. Zumu

ɗ

in da nake jini nin ban ga yana yi akan auran mu ba se gashi yau ya tashi gaba

ɗ

aya ya rikita ni da tsadaddun kalaman soyayya irin wa

ɗ

an da kunnuwa suke da muradin sauraro a ko da yaushe. Rabon da muyi hira ta nutsuwa kuma me da

ɗ

i

irin haka tun ba'a saka ranar auren mu ba. Kamar yanda ya ce mun wani alkhairi ne ya sakko mana ba zato na tsammani yana zaune kawai wani tsohon abokin Baban sa ya kira shi yake cewa ya samu labarin zeyi aure, a taƙaice dai ya saka yayi masa list na duk w

ani abu daya rage masa cikin harkar auran yace ze

ɗ

auki nauyi zancen da akeyi har ya turo masa ku

ɗ

a

ɗ

e ya ce a fara aikin kafin sauran su iso. Ya ce mun

"Halims Allah na son mu kasance tare, a sanda na sare nake ganin ba zan iya ba se ya turo mun da agaji

ta in da ban yi tsammani ba. Ke alkhairi ce a rayuwa ta ina roƙon Allah ya bani ikon kyautata miki kwatankwacin yanda kika kawo haske cikin rayuwa ta".

Saboda murna har rawa se da nayi duk da ba wai na gama jin ƙwarin jiki na bane ba, na ringa kwararaw

a ko ma wanene wanda ya kawo mana wannan

ɗ

aukin addu'a. Bamu kashe wayar ba se da naji zuciya ta ta fara tashi dalilin yunwa ga kuma surutun da muke ta yi ba dan Bilal ya so ba muka rabu akan da zarar na ci abincin na yi masa ko flashing ne.

Abba da Ma

ma na tarar zaune a falo, gaba na ya fa

ɗ

i ganin hawaye akan fuskar Mama Abba kuma yana durƙushe gaban ta da alama haƙuri yake bata, na matsa kusa dasu da sauri ido na na kawo ruwa na fara tambayar me ya faru?

"Babu komai Halima, wai tunanin zakiyi aure k

i bar mu ne duk ya fara sanyayar mana jiki shi ne take kuka" Abba ya fa

ɗ

a kamar me yin magana da yarinya yar shekara biyar ko ƙasa da haka. Fashewa nayi da kuka na zauna gaban Mama nace

"Ni ce ko? Sabo da ni kike kuka?"

"Me yasa zan yi kuka saboda ke H

alima? Bana fatan ubangiji ya nuna mun ranar da fushin wani daga cikin ku ze ta

ɓ

a zuciya ta har yasa in zubar muku da hawaye ina neman tsari da hakan. Hawayen tausayin nake yi bana baƙin ciki ba" Mama ta fa

ɗ

a se Abba yace

"Haba Amina ban san sands kika za

ma me nace akan magana guda

ɗ

aya ba, shi ba zaki yarda da ƙaddara ki bar komai a hannun Allah ba?"

Kafin tayi magana nayi saurin kama hannun ta ina kuka nace

"Dama na san saboda ni ne, dan Allah Mama kiyi haƙuri, ki yi mun addu'a ki kuma sakawa al'amar

i na da Bilal albarka nasan ubangiji baze kunyata ku ba. Addu'ar ku zata kasance hasken da ze kore mana kowanne duhu. Kuma ki dena damuwa Mama yanzun nan Bilal ya kira ni ya gaya mun wani abokin Baban sa ya bashi ku

ɗ

i yace ya ƙarasa gini, babu abin da ba z

e yi ba da yardar Allah Mama ki kwantar da hankalin ki babu wanda zeyi mana dariya kamar yanda suke sauraro".

Hannu biyu Mama ta

ɗ

aga tace

"Allah na bar amanar Halima a hannun ka. Kada ka bari wauta da makauniyar soyayya su jagoranci al'amuran ta a gid

an auren ta"

"Amin, yanzu ki kayi magana Amina. In sha Allahu se mun ce gara da aka yi" Abba ya sake fa

ɗ

a.

A sanyaye na tura shayin dana ha

ɗ

o zuciya ta duk babu da

ɗ

i. Ban zaci rashin son da Mama take yi wa aure na da Bilal ze saka har ta zubda hawaye ba

. Se na ringa jin kamar banyi daidai ba da tun farko naƙi bin ta tata amma kuma ban hango laifi na akan bin son raina da nayi ba. A cikin labarin ta na samu tawa ƙarfin guiwar. A kullum ta kan karanta mana irin rayuwar da sukayi da Abba, wuyar da suka ci t

are har zuwa yanzu da da

ɗ

i yazo shima suke shan sa tare.

Tun ina ƙarama na tashi da sha'awar irin rayuwar da iyaye na suke gudanar wa ta tsantsar soyayya da tattalin juna har zuwa kanmu yaran da suka haifa.

Mahaifiya ta Amina Sa'id haifaffiyar unguwar

Yakasai ce yayin da Abba yake haifaffen Galadanci. Tamkar banbancin dare da rana haka suka sha banban gurin asali, Mahaifin Mama attajiri ne kuma basarake wanda a zamanin sa sunansa yayi amsa kuwwa a ƙwaryar birnin kano da kewaye. Allah ya bashi tarin duk

iya wadda ya ƙare rayuwar sa yana hidimtawa iyalansa da al'ummar dake zagaye dashi. Mamana ita ce ya ta hu

ɗ

u cikin jerin yaran sa bakwai daya haifa da matar sa ta aure guda

ɗ

aya Hajiya Saude. Namiji ne babban su Alhaji Lawan se me bi masa Hajiya Rumana san

nan Mama Fauziyya se Amina mamana kenan, Baba Faisal ya rasu shekaru biyar baya, Baba Mudassir se Anty Labiba data kasance autar su.

Abbana ya fito daga babban gida me yawan ahali domin matan mahaifin su hu

ɗ

u, a jerin yaya shine na goma sha uku a gida

n gaba

ɗ

aya a

ɗ

akinsu kuma shine na hu

ɗ

u kuma namiji tilo. Gidan su gida ne irin na bani babu, Mahaifin su Malam Ibrahim talaka ne domin har ya mutu be bar musu komai ba ban da gidan gandu. Duk da bashi dashi ku

ɗ

i amma yayi ƙoƙari sosai akan tarbiyyar yara

nsa. Ya saka su makarantar addini duk kuma wanda kaga yayi karatun boko a gidan to shi ya saka kansa ba Malam Ibrahim ba. Abbana shine namiji na farko daya fara karatun boko a gidan domin sauran da sun tasa sukayi sauka a makaranta shikenan se su shiga kas

uwa, da dama ta fara zuwa se aure su fara tara Iyali wannan yasa jikokin gidan muke da bala'in yawa wasu idan ka kalli shekarun su dana iyayen su se kaga kamar basu suka haife su ire ire na mun shiga layin sa'annin yayan jikoki ne saboda iyayen mu da basu

yi aure da wuri ba.

A BUK Abba ya ha

ɗ

u da Mama, lokacin yana level 2 Business administration ita kuma tana level 1. Daga mutunchi kasancewar sa me ƙoƙarin gaske ya kan koya musu karatukan da suka shige musu duhu a hankali mutunchin nasu ya riki

ɗ

e zuwa

soyayya wanda ita Maman ce ta fara nuna sha'awar hakan. Daƙyar Abba ya amince, badan ba tayi masa ba ko kuma baya son ta se dan ganin tazarar dake tsakanin sa da ita. Ya kan ce mata

"Akwai banbanci me girma tsakani na dake Amina. Ni ba sa'an auren ki bane

, ƙima ta bata kai ta ko da direban da yake kawo ki makaranta ba ki rufa mun asiri ki barni na kammala karatuna lafiya domin shine madogara ta idan wani abu ya faru na rasa wannan damar ban san ina zan kama ba". Bata sare ba taci gaba da bibiyar sa da kuma

ubangiji ya ƙadarta akwai rabon aure a tsakanin su se gashi sun yi har an haife mu a kullum bakin

Abba baya gajiyawa da nanata halin karamcin da ahalin Mama suka gwada masa.

"Sun ƙauna ce ni a sanda bani da komai, sun aminta dani suka bani guda daga m

afi soyuwar ahalin su idan har ban saka musu ta hanyar faranta ran Amina har bakin raina ba da wanne ido zan tsaya gaban Allah na maida amar da mahaifin ta ya bani?" Abin da yake yawan fa

ɗ

a kenan. Mama ta manta asalinta da rayuwar jin da

ɗ

in da ta taso a ci

ki ta rungumu mijin ta da sabuwar rayuwar da ta za

ɓ

awa kanta. Sun kwana basu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login