Showing 147001 words to 150000 words out of 641791 words

Chapter 50 - HALYSAAH COMPLETE

03 Sep 2026

168

kuwa" Godiya tayi wani murmushi ta bude handbag dinta ta ciro wani babban laya bakikirin da shi ga er karamar kwado a jiki ta mika ma Momy tace "To aikin karshe kenan wannan Hajiya, Malam ya ce ki samu inda kika san baza a ta

ɓ

a tono sa ba ki binne a c

ikin gidan nan" Momy ta zauna gefenta tana murmushi ta amshi layan tace "To laya nawa na binne gidan nan ba a tono ba godiya, ai wannan karamin aiki ne a wajena don ba sabon abu bane" Godiya tace "Yauwa, bayan kin binne Malam yace ki basa yarinyar kawai, w

allahi yace min in har ta wuce sati biyu Abdul bai rabu da ita ba to bazata wuce sati biyar ba a gidansa" Fara'ar fuskar Momy ya bace tace "Har sati biyar Godiya? Ni da yace min sati daya kacal a waya" Godiya tace "Halan bai gaya maki irin abubuwan dake ƙa

n dan ki bane? Da yaya ma aka samo kansa har asirin nan yayi tasiri? Ai abubuwan ƙan Abdul sun fi karfin wani asirin wallahi kiji in gaya maki" Momy ta sauke ajiyar zuciya tace "An ta

ɓ

a gaya min haka da dadewa wallahi, don ni akwai malamin da yace min ma y

anda asiri ke cin ubansa shi sai an wahala asiri zai ci sa" Godiya tace "To wallahi Malam sai da ya tura masa aljanu don ma ki ji Hajiya, aikin nan sai da Malam ya hada da wasu malaman don aiki ne me wahalan gaske yace min wallahi" Momy tace "To ni fargaba

na kada fa in mika masa yarinya ace asirin nan bai ci ba abinda muke gudu ya afku mu shiga uku Godiya" Godiya tace "Sai kace yau Malam ya fara maki aiki? Ai da aikin bai yi ba kinsan bazai boye mana ba, sai dai ya kara mana lokaci yayi wani sabon aikin fa,

dama yace in na yarinyar ya ci shine zai sa na Abdul din ma yayi tasiri sosai" Momy tace "Haka ya ce kam" Godiya tace "Don haka zuwa gobe ki basa ita kawai su tafi an gama aiki sai jiran result, kuma ina me tabbatar maki zaki sha mamaki" Momy na murmushi

tace "Toh shikenan godiya, nagode sosai, zan tura masa cikon dubu dari biyar dinsa anjima" Da yammacin ranan bayan Momy taga Abdul ya fita gidan tayi maza ta aiki mai aikinta kasuwa saboda tayi amfani da daman ta haƙa rami a garden din gidan ta binne layan

da Godiya ta kawo mata, bayan mai aikin ta tafi Momy ta zaga zuwa garden din gidan ta samu spot me kyau ta fara haƙa rami da wuka, bayan ta haka yayi zurfi yanda take so sannan ta jefa layan ta mayar da ƙasan wajen ta dau wani dutse ta dora dai dai wajen

don kada a ga alamar an tono kasa, tap ta bude don wanke hannunta da wuƙan da tayi using, Khaleesat ta karasa bakin window din dakin Momy jin ƙaran bude ruwan pampo, in ta gaji da zaman dakin dama jikin window take zuwa ta tsaya tana kallon waje, ta tsaya

jikin window din tana ta kallon Momy dake ta wanke hannunta bayan ta wanke wuƙan, bayan ta gama ta kara komawa kusa da dutsen tana seta sa da kyau ta yanda ko da wasa baza a ga tonannen ƙasa ba, sai kuma ta mike ta fara tsinko doddoya dake Garden din, sann

an tayi using wuƙan hannunta ta yanki pumpkin leaves isasshe bayan ta gama ta bar garden din tana rike da ganyayyakin hannunta, babu abinda Khaleesat ta kawo a kai don tunaninta ganye Momy taje diba a garden din, Momy na kai ganyayyakin kitchen sai ga su M

eemah sun dawo daga shopping din da ta aikesu su yi ma Khaleesat, dariya Momy ta dinga yi a parlor ganin wasu shegun abayoyi masu saukin kudi da suka kwaso ma Khaleesat irin wanda ake dinkawa a kano, ga wasu shegun dogayen riguna su ma masu arha, hatta inn

er wears da suka siyo duk very low quality ones ne, babu wani abu na arziki da suka siyo ma Khaleesat, Momy na ci gaba da dariya tace "Duk maida su cikin ledojin kawai na yafe ganin wannan tarkace haka karima, amma baku da kirki yaran nan" Aunty Karima na

dariya ta maida kayan cikin leda ta kulle tace "Su ne dai dai er talakawa ai Momy, da so kika yi ki ga abayan dubu hamsin zuwa sama? Ai ita Meemah ma en gwanjo ta so mu je muyi selecting mata kawai" Dariya kawai Momy take, ita kuwa Meemah danna wayarta kaw

ai take don duk wani abu da ya shafi Khaleesat ko kadan baya bata dariya, she just can't wait taga irin rabuwan da Abdul zai yi da Khaleesat don shine babban abinda ke gabanta yanxu. Wajen karfe takwas da rabi Momy na zaune parlor da Abdul tana ta yi masa

hira, shi dai wayarsa kawai yake dannawa baya responding kamar ma bai san me take cewa ba, Momy ta kwalo ma mai aikinta kira, Mai aikin ta taho da gudu tace "Na'am Hajiya?" Momy tace "Zaki ga Kankana da na yanka a kitchen ki dauko ki kai ma Mamata a sama"

Mai aikin tace "To Hajiya" Juyawa tayi ta koma kitchen sai ga ta ta dawo rike da bowl din kankanan tana kallon Momy cikin ladabi tace "Amma Hajiya dakin a kulle yake" Momy tace "A'a a bude yake tun daxu, ki je ki kai mata" Bayan mai aikin ta tafi ta kai w

ater melon din ta dawo ta tafi kitchen ta ci gaba da aikin da take, Momy ta dau wayarta tace "Bari in inyi waya da Alhaji, daxu na ga kiransa ina kitchen wallahi" Shi dai Abdul bai ce mata komai ba har ta shiga dakin dake downstairs ya bi ta da kallo... Ba

yan minti biyu ya mike ya nufi stairs direct ya tafi bangaren Momy, yana bude kofar dakin Khaleesat dake zaune saman darduma bayan ta idar da sallah ta gama duk addu'o'in da zata yi ta juya ta kalli kofar, sosai gabanta ya fadi bayan sun hada ido da Abdul,

ya karasa cikin dakin babu yabo babu fallasa yace "Ta shi mu je shopping...." Khaleesat da gabanta ke faduwa ta nuna masa ledan da Momy ta kawo mata daxu duk da bata duba kayan ciki ba cikin sanyin murya tace "Ai Momy ta sa an min shopping din, ka gan su

can ma" Ya hade rai yace "Kee... Get up nace, i am not asking for ur opinion" Ta sauke idonta ta mike tsaye da kyar ta dauke darduman tana linkewa, sosai taji hankalinta ya tashi, a ranta ta dinga addu'an Allah ya kawo Momy dakin immediately, fixge darduma

n hannunta yayi ganin it's taking her a whole eternity to fold, ya ajiyesa saman kujera sannan ya kama hannunta suka nufi kofa fuskarsa a daure suka fita daga dakin, Khaleesat dai bin sa kawai take a tsorace, downstairs suka sauka har sannan yana rike da h

annunta, babu kowa a parlorn sai mai aiki dake goge goge a dining area, ya dau makullin motarsa da ya bari kan center table, Khaleesat ta marairaice masa cikin rawan murya tace "Ya Abdul Momy fa bata sani ba, kar ta shiga dakinta taga bana nan, kaga babu d

adi haka" Wani kallon da yayi mata yasa tayi shiru zuciyarta na bugawa, bata sake gigin ce masa komai ba har suka fita parlorn gidan zuwa parking space, Khaleesat taji hawaye ya cika idonta bayan ya sa ta shiga motarsa ya shiga driver seat, mai gadi ya bud

e masa gate ya fice gidan da motar. Momy ta fito parlor tana kallon Mai aikinta tace "Naji kamar fitar mota, waye ya fita?" mai aikin tace "Alhaji karami ne ya fita" Momy tace "Shi da wa?" Mai aikin tace "Shi da matarsa" Shiru Momy tayi don bata yi tunanin

zai ce zai tafi da Khaleesat yau ba, don so tayi taga yanda za su kwashe, shi yasa ma ta basa hint din dakinta a bude yake, ta zata can din kawai zai bi ta ko kuma ya kai ta dakinsa, Momy ta sauke ajiyar zuciya, ganin mai aikinta sai kallonta take ta hade

rai tace "Lafiya kike kallona haka munafuka?" Da sauri mai aikin ta juya ta bar wajen, Momy ta juya ta koma daki amma fa zuciyarta ya kasa nutsuwa sam sam, gani take kamar Abdul zai yi tarayya da Khaleesat, duk da malaminta bai ta

ɓ

a mata aiki bata ga resu

lt me kyau ba amma a wnn case din sai take

ɗ

ari

ɗ

ari kada abinda suke gudu yaje ya afku dama ga Godiya tace aikin me wahala ne, ai kuwa da ta shiga uku ta lalace, number Godiya tayi dialing ta zauna gefen gado tana jiran tayi picking. Hawaye kawai Khaleesa

t take tana dafa shayin da Abdul ya sa ta dafo masa a kitchen, ita ta ma riga tayi give up yau don bata da wani dubaran da ya rage mata in ba so take ta fusata Abdul ya doketa ba, she will just accept her kadr with good faith, gwara tayi accepting dinsa ka

wai a mijinta tunda haka Allah ya kaddara mata, goge hawayenta tayi tana tafiya a hankali ta tafi kai masa lipton din dakinsa, tana bude kofar ya ajiye wayar hannunsa yana kallonta, kanta a kasa ta karasa har inda yake ta duka ta ajiye masa black tea din,

ta mike zata bar wajen ya jawota ya zaunar da ita gefensa yana kallonta, ita dai bata bari sun hada ido ba zuciyarta na wani irin bugawa, ya dago kanta suka hada ido, sauke rigar baccin jikinta yayi slowly yana kallonta babu ko kiftawa, ta sunkuyar da kant

a bugun zuciyarta ya tsananta sosai, tana ji tana gani ya cire duk abinda ke jikinta yana kare ma each and every part of her body kallo, bata sake yarda sun hada ido ba, a hankali ya kwantar da ita, ta runtse idonta da sauri jikinta na rawa ganin inda yake

kokarin kai bakinsa, after some seconds Khaleesat ta bude idonta a hankali tana kallonsa jin bai yi abinda yayi niyya ba, taga wani wajen daban yake kallo babu ko kiftawa, after some seconds ta ga ya mike ya nufi kofa ya bude, fuska daure yake kallonta ba

bu yabo babu fallasa yace "I need my privacy....." Khaleesat ta mike zaune da kyar tana kallonsa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta jawo Hijab dinta da ya cire tun zuwansu gidan ta saka sannan ta dau kayan baccinta ta nufi kofa, bata bari ta hada ido da s

hi ba ta fita daga dakin taji ya kulle kofar da makulli, juyawa Khaleesat tayi tana kallon kofar.....

*Halysaah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah and u send ur evidence of payment 07087865788

👈🏻

, it's better ki ji tsoron Allah ki sauke nau

yi kiyi karatunki cikin kwanciyar hankali don littafin na kudi ne, in kika karanta with no payment i owe you 500*

We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, l

afaya, jewelries, kitchen items e.t.c.....

All at affordable prices

Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested....

Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM

HALY

SAAH 47

Da Asuba Khaleesat na zaune kan gado ta dafe kanta da yayi mata nauyi sosai, tun karfe uku da rabi bacci ya kaurace mata, bayan tayi sallahn nafila ta kai ma Allah kukanta shine take ta zaune saman gado tana tunanin rayuwarta, in 3 weeks time za

su yi resuming school wanda shekarar su na karshe kenan za su shiga a makarantar but unfortunately tasan baza a koma da ita ba, ko kadan bata saka ran zata koma John Hopkins ba dama, but it's really hurtful don duk shekarun da tayi a makaranta zai tashi a

banza kenan, ta goge hawayen da ya gangaro mata jin ana kiran sallan asuba ta sauka daga saman gadon, sai da ta dafa bango sbda juya mata da kanta ke yi, tun da ta tashi daxu take jin jikinta kamar ba ita ba, she can't even understand how she is feeling, s

ai da ta koma ta zauna na yan mintuna sannan ta tashi tana tafiya slowly ta wuce bandaki, wanke bakinta tayi sannan ta dauro alwala ta fito daga bandakin, bayan ta idar da raka'atanil fajr tayi sallan asuba, har karfe bakwai na safe Khaleesat na zaune kan

darduma duk da ta idar da azkar din ta, in tayi wannan tunanin tayi wancan a haka dai har ta mike daga karshe tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta bude ta fita daga dakin, bata karasa parlon ba ta tsaya tana kallon Abdul dake kwance saman 3 seater idonsa

a lumshe yana sauraron karatun qur'ani ta wayarsa dake gefensa, duk tunaninta bacci yake ganin yanda ya lumshe ido, har zata juya ta koma dakinta taga ya bude ido yana kallonta, ta sauke idonta ta karasa cikin parlon tana tafiya a hankali ta duka kusa da s

hi cikin sanyin murya tace "Ina kwana" Yace "Lafiya" Bata sake cewa komai ba kanta a kasa, after some seconds ta mike zata bar wajen, calmly yace "I need breakfast, ban ci abinci da daddare ba" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma tace "Toh...." Juyawa tayi ta

nufi kitchen don ganin me zata girka, doya da kwai tayi deciding tayi don shi tagani available a kitchen din, wajen karfe takwas ta gama komai ta kai har gabansa a parlon ta durkusa ta ajiye, ganin bread a kan dining table ta mike ta tafi ta dauko sannan

ta dawo ta ajiye masa tana kallonsa a hankali tace "Gashi na gama, in hada maka shayin?" Without looking at her yana danna wayarsa daga kwancen da yake yace "Ohk" Hada shayin tayi bayan ta gama ta koma gefe tana kallonsa a hankali tace "Na gama" Ajiye waya

rsa yayi ya sauko daga saman kujeran, shayin ya dauka yana sha, ba tare da ya kalleta ba yace "Ke ina naki shayin?" Shiru tayi bata ce komai ba, jin tayi shiru ya daga kai ya kalleta, sunkuyar da kanta tayi, sai kuma ta mike ta nufi kitchen, ba a dau lokac

i ba sai ga ta ta dawo da cup da tea spoon, ta duka kasa ta fara hada shayin nata, ya kalli madaran da ta zuba a shayinta ya dau wani spoon ya kara mata madaran, ita dai bata bari sun hada ido ba, a plate daya ya dibar masu doyan ya fara ci, ita dai juya s

hayinta kawai take a hankali, after some minutes ganin bata fara cin doyan ba ya daga kai ya kalleta yace "Ko a baki za a baki?" Ta

ɗ

an yi murmushin karfin hali ta dau fork ta fara cin doyan a hankali, da ta kallesa sai su hada ido, kana ganinta kasan she

is not comfortable a wajen don ya riga ya sa mata tsoronsa a zuciya, daga karshe ta ajiye fork din hannunta a kan tray, ya daga kai ya kalleta, a hankali tace "Na koshi" Bai ce mata komai ba, ta koma gefe tana shan shayinta slowly, after a while Abdul ya m

ike ya koma saman kujera, ta tashi ta dau sauran abincin ta kai kitchen, sai da ta wanke utensils da suka yi using sannan ta fito daga kitchen din, magana take son yi masa amma tana tsoro, ya kalleta tayi saurin sunkuyar da kai kamar munafuka tana wasa da

yatsunta, yace "Me ya faru?" Ta karasa ta duka daga gefensa a hankali tace "Dama pls ina son zan yi magana da Safiyyah, ka taimaka ka kira min ita ta wayarka" A takaice yace "Bazan kirata ba, kanwar baabarki ce Safiyyar?" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi,

ta sunkuyar da kanta tayi shiru bata ce komai ba, yace "Tafi ki bani waje" A hankali ta mike a sanyaye ta wuce dakinta, goge hawayen da ya taru idonta tayi ta zauna gefen gado, after a while ta share hawayen da ya ki tsaya mata ta mike ta cire hijab din ji

kinta ta linke ta ajiye sannan ta shiga bandaki, brush tayi sannan tayi wanka, ganin abubuwan wanke gashi a bathroom din ta wanke gashinta ta tsane da karamin towel sannan ta dau wani towel din ta daura ta fito, tana tsaye gaban madubi tana shafa man gash

i taji an bude kofar dakin, da sauri ta juya gabanta ya fadi sosai ganinsa, kana ganinsa kasan daga wanka ya fito shi ma, cikin dubara ta gyara daurin towel dinta tana jin zuciyarta na bugawa ta ci gaba da oiling gashinta, ya karaso har inda take tsaye ya

tsaya a bayanta yana kallonta ta madubi, ita dai ta kasa dago idonta tana jin saukan numfashinsa a bayanta, ta ajiye oil din hannunta a hankali don duk ta daburce, shi dai yana tsaye dab da ita yana kallonta ta madubi, ya kai hannu zai yi loosening din tow

el din kirjinta, juyowa take son yi da sauri kamar zata yi kuka cause bazata iya ganin kanta ta madubi a yanda yake ganinta ba, yaki barin ta juyo hakan yasa ta runtse idonta zuciyarta na bugawa, bai fasa kallonta ta madubin ba har ya cire towel din jikint

a ya jefar saman gado, he kept his eyes glued to her cause he just can't stop admiring her bare body any time he set his eyes on her, gaba daya taki yarda ta bude idonta, bata ankara ba kawai sai jin su tayi a saman gado, bata san sanda ta bude ido ba ta f

ashe da kuka tana turasa a tsorace ganin yau kai tsaye kawai far mata yake kokarin yi babu bata lokaci,

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login